TARAYYA 9-10
Page 9
Bayan rasuwar amnah sosai
suhailat tashiga damuwa shikuma gashi bai iya ya ake lallashi ba bare
Iyakacinsa idan zai fita
yanasaka
yin breakfast idan yadawo suyi dinner sbd bai cika lunch agidaba.
Hakadai ta dangana tacigaba
da rainon sabon cikinta.
Sultan yayi yayi yaqara aure
yamaqi dawowa qasar shiyasa yadauki mataki kaitsaye akansa.
Sultana tashiga damuwa matuqa
jin amnah ta rasu batareda sun ta6a ganinba saidai a hoto kawai gashi tanason
zuwa amma sultan yasa doka.
Jakadiya kuwa sosai tafara
shirya shiryen na kullum tana sashe sashe duddubawa cikin dubara sbd sotake saita
ringa fahimtar halayyarka sbd kar asamu magaji ta macenda batada nutsuwa ko
ma'ana.
Kullum cikin kwantarwada
suhailat hankali sultana take hardai taga ta warware itama hanakalinta ya
kwanta.
Lurada jakadiya sultana tayi
ta kalleta bayan ta kori dukkanin bayinta dake sashen sbd maganar datakesonyi
da jakadiyar.
Rumanah ce kawai a bedroom
din ammyn tana aikinta hankali kwance.
Cikin muryar bada umarni
tace,
Inason sanin hukuncin da
sultan ya yanke akan maheer sbd nasan me shirunsa yake nufi.
Sunkuyar dakai jakadiya tayi
wani zufa ya tsatsafo mata cikin sanyin jiki da sanyin murya tace,
Sultan yabada umarnin
atanadarwa yarima sa dakoki har biyar akillacesu zai dawo bazai komaba yanxu
sai ansamu qaruwa daga garesu.
Tashi zaune sultana tayi
cikin wani irin yanayi na tsananin damuwa da takaici taringa maimaita
innalillahi.
Kallon jakadiya tayi tana
qoqarin ganin damuwarta bata rinjayetaba murya amatuqar sanyaye tace,
Har kin tanadesu 'din?
Tukunadai ranki ya Dade
saidai nima ina cikin tsananin fargaba da tsoron yanda zata kaya sbd aurensa ma
ta yaya akasamu yayi bare yanxu mata har biyar.
Rintse idanu sultana tayi
tareda budesu jajir tace,
Idan kin zabesu kafin ki
gabatarwada sultan su ki gabatarmin dasu inason naga matanda wasu daga cikin
jikokina zasu fito ajikinsu.
Jakadiya na fita ta bada
umarnin abuga qararrawa atara mata dukkanin wata kuyanga dake masarautar.
Nan tafara dubasu cikin layi
harbasa qirguwa sbd yawansu amma takasa samun 'daya dazata ware duk wadda
takalla saitaga komai gyara da kulawar daza'ayi mata batakai matsayinda yarima
zai hada shimfida da itaba.
Da haka ta sallamesu tace
gobe kowanne yayo wanka su sake zuwa subi layi.
Tana gama gyaran bedroom din
tafito tazo gaban sultana ta durqusa cikin girmamawa tace,
Ammy nagama kinada buqatar
wani abu?
Kallonta sultana tayi da
idanuwanta dasukai jajir sbd baqin ciki ta girgiza mata kai.
Ganin halinda ammyn take ciki
yabata tsoro ta miqe hartakai qofa ta waiwayo cikin damuwa murya asanyaye tace,
Saida safe ammy.
Asanyaye ta isa dakinsu ta
tararda daga mamani har nuratu basu dawoba ta tube taso watsa ruwa amma jin
batada gajiya kuma batai wani aikin wahalaba tayi kwanta.
Tana qoqarin juyawa nuratu
tashigo amatuqar gajiye ta zauna bakin 'yar katifarta tana cewa,
Rumanah wlh tsufa da wuri zai
kamani sbd wahala.
Murmushi rumanah tasaki
ahankali kafin ta tashi zaune tace,
Me kike gudu da tsufa da
wuri?
Harararta nuratu tayi tana
zame kayanta tace,
Ke kuma mekike yiwa sauri da
tsufa?
Nifa rumanah banason tsufa da
wuri sbd bazan ta6a cire rai daga hangowa kaina wata irin kyakkyawar rayuwa,
Ke nifa har mafarki nakeyi
nazama wadda tafi kusanci ga Wanda wai zai mulki masarautarnan anan gaba,
Kuma kinsan menene?
Mace nake gani amafarkina
koda yaushe saidai adon zinarai dake jikinta tana hanani ganin fuskarta....
Mamani dake shigowa tayi
saurin qarasowa ta riqota tana washe dukkanin haqoranta tace,
'Yarda zaki haifawa yarima
ce......
Fusgewa nuratu tayi da qarfi
tana cewa,
Barni da zancenki mamani
koyaushe bakinki baya tsayawa mmatsayinsa..
Sake washe baki mamani tayi
tace,
Nuratuna dama nasan tuntuni
jikina nabani kece zaki fitardani cikin wannan qasqantacciyar rayuwar,
Jikina nabani kece za'a zaba
amatsayin sa 'dakar yarima.....
Dariyace taxowa rumanah tayi
saurin rufe baki sbd gudun masifa da balain mamani dazata iya kwana tana surfa
mata.
Cikin takaicin halin
mahaifiyarta nuratu takalleta tace,
Lallai mamani bakya sona
tunda harkike fatar nazama baiwarda za'a riqa kwana dani ina haihuwa ana karbe
'yayan.
Cikin saurin mamani tace,
Kibar maganar baiwa daga
ranarda kika hada shimfida dashi kintashi daga baiwa sbd duk Wadda ta haifo
magaji sultan ya 'yantata daga ranar kuma ita za'a miqawa matsayi dakuma
kujerar zaman uwar sarki sbd tariga ta haifo sarki,
Duk Wanda taso nadawa yayiwa
danta riqon qwarya shi zata nada har 'danta ya girma abasa kujerarsa,
Idan kika haifi namiji nuratu
babu Wanda zaki bawa riqon kwarya kece zakiyi mulkin da kanki,
Kece zaki hau kujerar sarauta
da kanki,
Kece zaki mulki dubban
'daruruwan sarakuna da daulolinsu,
Kece zaki zama mace ta farko
dazatayi mulkin wannan masarauta da aka tsani haihuwar mata.....
Kasa riqe dariya rumanah tayi
tasaketa tana kallon mamani data watso mata mugun kallo tayi saurin hadiye
dariyar.
Nuratu ma dariyar tasaki tana
kallon mamani kafin takalli rumanah suka saki wata dariyar.
Mamani tayi mugun hasala tayo
kan rumanah nuratu tayi saurin riqota tana cewa,
Haba mamani nah kece fa uwar
sarauniya nuratu kuma kakar magajin sarautar dariyafa kawai mukeyi ta farin
cikin wannan mafarkin naki mai dadin gaske kokuwa 'dayar mamar magajin sarauta.
Dariya suka qunshe suna
kallon juna suna kallonta.
Ganin sun maidata mahaukaciya
yasa qyaci ta fice ahasale.
#Mamuhgee
Page 10
Baca Juga
Haske writers association💡
+
Bayan fitarta rumanah taja
abun lullubewarta tana murmushi tace,
Nuratu kinfa karyawa mamani
gwiwa daga kawai tana mana fatar samun jin dadi da 'yanci idan kika zama
sarauniya.... 1
Kallonta nuratu tayi cikin
tsananin sanyin jiki tace,
Rumanah ke kinamin fatar
nazama baiwarda za'a riqa kwana da ita tana haihuwa Ana karbe yayan idan nazama
haka me naqaru dashi arayuwata bayandai ta tabbata naza baiwa tahar mutuwa...
Qarasowa da sauri rumanah
tayi ta rungumeta ganin hawaye na zubo mata tace,
Nuratu bana miki fatar wannan
rayuwar ko amafarki bare afili,
Keda mamani kune 'yan uwana
kullum fatana da adduana musamu kubuta atare mukoma ga asalinmu domin kuwa
saimun koma asalinmu zangano nawa asalin.
Cikin sanyin murya nuratu
tace,
Rumanah bawa baida ra'ayin
kansa ko abinda yakeso sai Wanda uwayen gidansa suka yanke akansa,
Shin kina tunanin qaddara
zata iya zuwa kaina aza6eni cikin masu zuwa shimfidar yarima?
Girgiza mata kai rumanah tayi
cikin son qarfafata tace,
Insha Allah bazamu ta6a
wannan rayuwarba nuratu.
Rumanah ammy bazata ta6a bari
kiyi wannan rayuwarba saidai ni banada tabbaci saidai Allah ya dubi rashin
gatana.
Jiki sanyaye zuciya fal da
tunani da zullumi suka kwanta har mamani tadawo cikin dare ta kwanta babu Wanda
yayi bacci acikinsu sbd tunani.
Washe gari fuska 'daure
mamani ta tashi babu Wanda ta amsa gaisuwarsa acikinsu qarshema kan rumanah
taso sauke haushinta Dan har marinta tayi daga gaisuwa.
Cikin sanyin jiki ta share
hawayenta tareda girgizawa nuratu data bude baki zataiwa mamani magana kai
tareda sakin murmushin dole mai ciwo kafin ta kammala shirinta ta fice tana
cewa,
Natafi'"""cikin
sanyin murya.
Kodata isa sashen part ammy
cikin sanyin jiki tafara aikinta har qarfe goma tabuga lokacin ammy ta tashi
Kanta qasa tagaida kafin
tahau gyaran dakin cikin rashin walwala da rashin kuzari sbd duk lokacinda
mamani tayi mata Abu abin na taba zuciyarta ganin batada wasu 'yan uwa kamarsu
tunda sukadaine nata.
Ammy sosai ta lurada rashin
walwalarta ta danne tata damuwar cikin kulawa takira sunanta.
Amsawa tayi tareda barin
gyaran gadon datakeyi tazo gabanta ta durqusa kanta na qasa. 1
Qare mata kallo tayi taga
yanda jikinta ke 'Dan rawa tace,
Rumanah meya faru dake?
Mayarda hawayenta tayi cikin
qarfafa muryarta tace,
Bakomai ammy.
Sam batason takurawa rumanah
shiyasa ta kyaleta kawai.
Tundaga lokacin sabuwar
tsangwana da muguwar tsana tashiga tsakaninta da mamani sbd gani takeyi itace
take zugewa nuratu kunne akan tadaina wanka da tsafta sbd kar azabeta.
Duk yanda take daurewa kasawa
takeyi saita kwana tana kuka sbd wani irin zagi da gori data sakota gaba dashi
akan iyayenta dasuka rasu.
Tun tana boyewa tuni damuwa
tabayyana ajikinta sbd ramar datayi.
Sultana duk datana cikin
damuwar dawowar maheer dakuma hukuncin sultan Saida damuwar ganin halinda
rumanah take ciki tadameta musamman ganin tana ramewa ta daina walwala kwata
kwata ta mayarda kanta cikin bayi 'yan uwanta duk wani aikin wahala tanayi
Wanda yaqara hargitsata.
Duk yanda sultana tayi da ita
tafada meke damunta ta nuna mata ba komai sbd idan tafada tasan azabardasu
mamani zasusha zai iya sanadin rayuwarsu kuma bazai tsaya akantaba harda
nuratu.
Jakadiya itace ta bincikowa
sultana tsaf abinda ke faruwa da rumanah sosai ranta ya 6aci hartayiwa sultan
Aiken abinda ke faruwa da rayuwar 'yar amintaccen bawansa daya rasu saikuma ta
dakatar sbd tasan hukuncinsa bazaiyi dadiba Dan rayuwarsuce ke lilo a sama kuma
barinsu duniya tamkar barin asalin rumanah ne sbd mamani kadaice tasani.
*
Qarfe biyar na yamma jirginsu
ya sauka a qasar
Kasancewar ansan bayason
rawar jiki da yawa yasa motoci uku kawai sukazo daukarsa da iyalinsa sai
khaleefa dasuka zo tare bayan yazo gurinsu daga zuwa weekend yabiyosu suka dawo
tare.
Tunda yafito ake zubewa ana
gaishesa so daya kawai yadaga kai alamar amsawa hannunsa daya na aljihun
wandonsa sai shades dinsa daya gyara.
Suhailat na gefensa ta saci
kallonsa zuciyarta na nauyi sbd ganin tsantsar kyawu da kwarjininsa taji
kishinsa na taso mata tayi saurin dauke kai tana gyara riqon handbag dinta.
Itada shine a mota 'daya
'dayar motar khaleefa dasu amah sai 'dayar ta guards.
Koda suka isa masarautar tuni
duk wani guard da manyan masarautar suka fito tarbonsa.
Cikin girmamawa ake zubewa
ana gaidasa harya isa gaban mahaifinsa a hankali yasaki murmushin da iyakacinsa
fuskarsata ya gaidasa sultana cikeda girmamawa da kewarsa.
Lokacinda isawarsu maheer ta
isowa sultana sakin murmushi tayi cikin tsananin farin ciki kafin tayiwa wanda
ya isoda saqon babbar kyautar yana ficewa suhailat dasu amma suka shigo part
'din jakadiya na gaba.
Cikeda girmamawa suhailat
taqaraso gaban sultana ta durqusa duk da cikinta daya fara girma ta gaidata.
Cikeda kulawa sultana ta amsa
tana kallonsu amah dasuka zauna jikin mahaifiyarsu sbd rashin sabo dasu.
Tana kallon yaran tace,
Jakadiya aje asake dubowa
part dinsu idan gyaran ya kammala sbd yaran sun gaji suna buqatar hutawa.
Washe baki Jakadiya tayi
cikin girmamawa tace,
Allah yataimaki sarauniyar
sarki kuma kakar sark ai tun asubar fari baiwa rumanah ta kammala duk wani
gyara da'akasata a part 'din daga part 'din na yarima har part din gimbiya
suhailat kuma kuyangi biyar nacan najiransu domin hidimarta data yara kuma anyi
musu gargadin ko kallon part din yarima karsuyi bare tunanin shiga koda dasunan
wanine ya aikesu.
Murmushi sultana tasaki
tareda kallon suhailat tace,
Suhailat kuje kuhuta da yaran
sun gaji sosai.
Miqewa tayi daidai fitowar
rumanah daga bedroom din ammyn fuskokinsu suka sauka akan na juna daidai kuma
shigowar yarima a palon na qurya Wanda qamshinsa yasasu juyawa qofar atare.
Saurin durqusawa rumanah tayi
tareda sunkuyar dakanta ta gaidasu atare batareda ta bambamtaba.
Suhailat ce kawai ta amsa
cikin wani mugun sanyin jiki daya saukar mata lokaci 'daya.
Ammynsa ya nufa da wani irin
murmushi da duk duniya itakadai yakewashi
Cikeda farin ciki da
murmushin daya kasa 6oye farin cikinta ta miqe tsaye yana zuwa ya rungumeta.
Cikin rawar jiki rumanah ta
fice sbd wani kallo da Jakadiya ta watso mata.
Itama jakadiyar ficewa tayi
hakama suhailat sbd tasan qaidane idan zai gana da mahaifiyarsa kowa ficewa
yakeyi sbd itakadaice takejin doguwar maganarsa bayan ita ko suhailat datake
matarsa baya doguwar magana da ita,su bayi ma ko masu hidimarsa tun tashinsa
bayajin yata6a yiwa bawa magana.
Bayan fitarsu Jakadiya
takalli rumanah data nufi qofar fita babban palon farko tana qoqarin barin part
din gabadaya takira sunanta.
Dawowa tayi tana sunkuyar
dakai sbd ko iya dagowa takalli suhailat bata iyayi sbd faduwar gaban datake
ji.
Ki kama yaran ki rakasu part
dinsu ta huta akula da yaran kar abari su dameta sbd yanayinta.
Jinjina kai tayi cikeda
ladabi ta miqe ta 'dauki fammah tareda riqe hannun amah kuma ta 'dauki handbag
din suhailat din tabi bayanta.
#Mamuhgee
Post a Comment for "TARAYYA 9-10"