HALIN GIRMA 36-40
2/17/22, 09:45 - Buhainat: Halin Girma
36
*******�
Cikin wani yanayi taji kamar bacci yana fuzgarta, ta sake gyarawa sosai Ummimi ta matsa mata sosai ta
kwanta a bayan, nan take kuwa bacci ya dauke ta. A tunanin Ummimi tsabar gajiya da wahala ce ta saka ta baccin, dan tun safe suka fito kuma tana lura bata saka komai a cikin ta ba sai ruwa, ita dai ta bata kudi taje cafeteria ta siya abinci taci, amma ita kuwa bata ci komai ba, dole ne ko ba karatu kake ba, ka jigata balle. Tausayin ta taji, musamman da ta gama fuskantar halin kirkin da, bama ita kadai ba duk ma'aikatan gidan na murna da samun ta a matsayin uwargijiyar su, babu hantara balle tsangwama, gaba dayan su son ta suke da gaske.  Tafiya suke tayi babu alamun zasu tsaya, har duhu
ya fara mamaye sararin samaniya, kallon ta Ummimi tayi taga har lokacin bacci
take da gaske, shiru kake ji a motar babu wanda yake magana a cikin su, a
tunanin da za'a samu ko yar karamar hira ce tsakanin driver da na gaban amma
babu wani wanda yayi magana a ciki, jakar dake kusa da Iman din ce ta fadi
kasa, Ummimi ta sunkuya da nufin dauka, abinda ta hango a hannun shi ya saka
hantar cikin ta kadawa, a firgice ta dago tana dunkule jakar a hannun ta,
juyowa yayi ya dube ta, ya sake dago mata hannun nasa da kyau dan ta gani
sosai, bindigar ce kuwa, tsoro ne ya kamata,
"Idan kika sake kika bud'e bakin ki a wajen nan, sai na
fasa kanki da alburushi."
Da sauri ta rufe bakin ta da hannun ta, juyawa yayi kan driver
yace
" Idan ka kai karshen titin zaka gangara haggu."
Da ka ya amsa, daga gani a tsoroce yake, rashin sani ya hanasu
ganewa tun shigowar su motar. Kallon Iman take ganin da gaske bacci take, bacci
me nauyi da ya hanata jin duk abinda ya faru, mamaki ne ya kama Ummimi, dama ta
saba irin bacci haka ko kuma dai akwai matsala, da sauri ta dan taba ta, sai
taga ta motsa kad'an tamma kuma bata tashi ba, ajiyar zuciya ta sauke, hawayen
da take ta makale shi ya gangaro zuwa fuskarta, me yasa mutane suka lalace
haka? Labarin da suke ji a gidan radio yau shine ya faru dasu? Idan har masu
sarauta da masu hannu da shuni basu da tsaro toh waye kai kuwa talaka? Anya
rayuwar zata tafi a haka?
  Cikin tsananin fargaba take har suka karaso wani
gida, karami a cikin gungurmin jeji, babu gida gaba babu baya, ba zaka taba
tunanin halitta irin ta mutum zata rayu a wajen ba, tana jin yadda suka dinga
shiga kan tudu da kwari alamun sam hanyar bata mota bace, ko tace mota bata
taba bi ba. Murfin motar ya bud'e yana nunawa driver bindiga, suka fito a tare
ya zagayo wajen sa ya rik'e kugunsa. Fito yayi da bakin sa, sai ga wasu kartin
maza su biyu sun fito, tare da wata mace a bayan su, tafawa sukayi da daya daga
ciki sannan yace
"Kayi babban aiki, aikin da zai firgita ilahirin k'asar har
ma da ketare, tana ina?"
Bayan motar ya nuna masa, ya tafi zuwa wajen ya bud'e yana leka
ciki
"Baccin ne be sake ta ba har yanzu?"
"Eh!"
"Tasha ruwan kenan!" Yayi murmushi yana rufe kofar
"Tasha sanda ta shigo motar."
"Kayi kokari sosai... Kudos!"
"Thank you sir."
"This is a shame to the Nigerian Armies, The royalties,
government, gaba daya ma, duk sunyi failing, ta yaya kake tunanin mutane zasu
sake yarda dasu? Bayan sun damka hakkin kulawa rayuwar su garesu, sai ya zama
sun k'asa tsare kan su?"
Sai ya kwashe da dariya
" Yaron nan a bayan mu yazo, yaron nan ta dalilin sa na
rasa komai, ciki harda aikin da na kwallafa rai, saboda shine shafaffai da mai?
Saboda shi din dan gata ne, shiyasa aka fifita shi akan kowannen mu, me yafi
mu? Mulki?"
"Oga!"
" Haka ne mana!" Ya fad'a da karfi
"Haka ne. Kullum cikin favoring dinsa ake, kullum cikin
yabon sa ake, na kai mataki Babba amma yaron nan, ta dalilin sa komai ya baci,
ya kake tunanin zan iya hakura?"
"Kunsan shekarun da na dauka ina gina rayuwata har na kawo
wannan lokacin?"
"A ah." Suka girgiza kai dukka
" Shekara goma sha daya, amma cikin sakan da be wuce goma
ba, ya kwace komai, khaki na, rank dina, mutunci na a idon duniya, na muzanta,
na zama abin gudu da k'yama."
Duk sun yi shiru kowa na sauraren sa, shirun shima yayi dan
bashi da abin fad'a kuma
" Ku shigar dasu ciki, idan princess ta tashi a fad'a
min."
Sai ya juya ciki ransa fari tas, ya tabbatar saura kiris bomb ya
tashi, bomb din da zai tarwatsa duk wani farin cikin Muhammad Ahmad Santuraki
da duk wani makusancin sa, shekara biyar kenan yana bibiyar sa, ya kuma samu
nasarar samun duk abinda ya samu a yanzu, wanda yake tabbatar da su kadai sun
isa su tarwatsa duk wani farin cikin sa. Matsala daya da ya samu, bashi kadai ne
yake son ganin bayan sa ba, nasa kawai yafi zafi ne, sai ya hada guiwa dasu,
yayi amfani dasu wajen samun abinda ya samu akan sa, ya kuma tabbatar da babu
wata alaka da zata sake hada su a nan gaba, ya datse duk wata hanya da zasu
neme shi.
  Ta jima tana bacci sosai, Ummimi dake durkushe a
gabanta tana kuka sosai taga ta motsa, ta cigaba da motsawa tana yamutsa fuska
kafin ta bud'e idon ta da kad'an kad'an da sukayi mata matukar nauyi, saman
dakin ta fara kalla, sai kuma ta shiga jujjuya idanunta tana son gano a in da
take, da sauri ta yunkura zata mike, Ummimi ta taimaka mata tana rik'e ta
"Karki tashi da sauri jiri zai iya daukar ki, ina tunanin
sun zuba miki magani ne.". Ta fad'a cikin muryar kuka
"Ina ne nan? Me muke anan Ummi?"
"Ni ma ban sani ba, wanda kukayi magana dashi, shi ya kawo
mu nan, sun sato mu!"
"Musaddik?"
"Eh."
"Innalillah wa inna ilaihi rajiun." Ta furta a
hankali, kanta da yake jujjuyawa ta saka hannu ta dafe, amai ne taji yana taso
mata, ta yunkura da nufin tashi amma kafin ta kai kofar har ta soma aman, wanda
babu komai a cikin sa sai zallar ruwa, tun tana yi har ta koma kakari
kasancewar babu abinda yake cikin ta tun safe, rik'e ta Ummimi tayi tana kuka,
tana jera mata sannu, sai da taga ya lafa sannan ta taimaka mata ta maida ita
gefen tabarmar da ta tashi,
"Bari na samo miki ruwa, sannu."
Ta tashi ta fito, su biyu ne a zaune suna karta, suna ganin ta
suka tashi
" Ruwa take so dan Allah. "
Da Ido sukayi wa juna signal, kafin daya daga ciki ya shiga wani
daki, ya dawo da ruwa ya mik'a mata, ta karba ta juya ciki, ta tarar da ita
tana ta juyejuye akan tabarmar, ta rik'e cikin ta da yake murda mata kamar zata
amayar da kayan cikin ta. Dagota tayi, ta bata ruwan ta kuskure bakin ta,
sannan ta sha, ta koma ta kwanta tana sake rik'e cikin ta.
  ***Kwanan Zeenat biy babu Bashir babu alamar sa,
Abba kuma ya zuba musu Ido be sake cewa komai ba, ko Mama be sake mata maganar
ba, shirun nasa yayi masifar bata tsoro, dan bata san me yake shiryawa ba,
ranar suna zaune Zeenat din na cin wainar fulawa, ba wani dadin ta take ji ba
amma itace kadai take mata dadin ci, sai nama da tuwo idan ta same su kamar
wata tsohuwar mayya, jigum jigum suke kowa da abinda yake damun sa. Kofar falon
ce ta bud'e duk suka kalli kofar a tare, Abba ne ya shigo, ya wuce dakin sa,
k'asa k'asa Zeenat din tayi masa sannu da zuwa be ma ji ba, ya shige jimawa
kadan ya fito, ya dubi Mama da tayi tsam tana kallon sa yace
"Tunda har ban isa na saka ko na hana Zeenatu abu a gidan
nan ba, kin nuna min ban isa ba tun fil'azal, na bar miki ita, idan har tana so
mu shirya da ita lallai ta koma dakin ta, ke kuma, hakuri na ya gaza, kije gida
kya dawo duk sanda kika shirya gyara auren yarki, idan har Zeenatu bata koma
dakin mijinta ba, toh zaman mu ba zai cigaba ba. "
Daga haka ya saka kai ya fice, ba don darajar yaran dake
tsakanin su ba, ba kuma don darajar zaman da tayi dashi na dadi a baya ba, da
zai sauwake mata ne kawai, amma hakan ba zai yiwu ba, har yanzu yana sonta yana
kuma son ta gyara halayenta.
  Tashin hankali ba'a saka maka rana, da girman ta
da komai gotai gotai zai ce taje gida, zagaye ta dinga yi a falon kaamar tayi
hauka, duk tsawon shekarun da sukayi da Ibrahim be taba nuna mata ko yatsa ba,
sai gashi a yanzu da girma ya soma hawa kansu, tayi abinda gaba daya mutuncin
ta ya zube a idon sa, har yana cewa zaman su ba zai yiwu ba.
" Mama dan Allah kiyi hakuri, zan koma wallahi ba zanzo ku
samu matsala da Abba akai na ba, zan jure koma menene dama ni na jawo ma kaina.
"
" Ba laifin ki bane, babu abinda zai faru , sake gwada
kiran Bashir din idan be daga ba sai kawai na saka Habib ya kaiki chan gidan
su, daga nan sa neme shi ai dole yazo ya dauke ki."
Da sauri ta dauko wayar, ta kira amma sai taji alamar anyi
blocking number, ajiyewa tayi jiki a sanyaye tana fadawa Maman, kira mata Habib
tayi, tace yazo maza gida yanzu duk abinda yake yi, be dau wani lokaci ba sai
gashi, ta fad'a masa abinda take so yayi,yace mata babu mota Abba ya fita,
sakashi tayi yaje ya kira musu napep yazo suka tafi, suka fita ta ja ajiyar
zuciya, ba zata iya jure tafiyar ko ina ba, ta riga tayi girman da zaman gidan
su zai mata wahala sosai, idan kuma ta tafi bata san ta yadda zata dinga ji
daga wajen Zeenat din ba.
***Yana zaune bayan sun gama wani taro da sukayi, ba zaka iya
tantance yanayin da yake ciki na bakin ciki bane ko na farin ciki, kiran layin
Musaddik yake amma still amsar daya ce, switch off, sunyi dashi kafin su taso
zai kirashi, gashi babu wani isashen lokaci da zasu sake batawa, su biyu ne
suka shigo, suka sara masa sannan suka koma gefe suka tsaya
"It's time sir."
Mikewa yayi be ce komai ba, ya shige cikin dakin, ya dauki
jacket dinsa da dayar wayarshi, sauran kayan nasa sun riga sun fitar dasu tun
dazu,gaba yayi suka bishi a baya, yana cigaba da kiran Musaddik din, ganin da
gaske ba zai same shi ba, shiyasa ya sauya akalar kiran zuwa kiran ta. Jiya
basuyi magana ba gaba daya, yasan tana kaiwa yamma a school haka kuma yasan ta
dawo a gajiya, ko da ya kirata no answer sai kawai ya kyale ta, a zuwan suyi
magana a yau kafin ya taho. Ringing wayar tayi tayi ba'a daga ba, bayan ta
katse ya sake kira amma still no answer, sai ya kashe wayar tasa baki daya ya
tura ta cikin aljihun wandon sa, sanda suka karaso wajen motocin da zasu dauke
su, tuni duk sun shiga shi kadai ake jira, dama kuma shine Captain din tafiyar.
Yana shigowa duk suka mike tsaya, irin doguwar babbar motar nan ce, sai da ya
zauna sannan duk suka zauna, driver ya jasu suka bar harabar wajen.
  Tun daren jiya labari ya kai fadar Maimartaba na
rashin dawowar Iman din daga makaranta wanda ma'aikatan gidan ne suka kai
labarin, kamar wasa da kowa ya dauka, a tunanin su ko wani wajen ta biya, amma
ganin har dare ya soma yi ya saka hankali ya fara tashi, zama ma neman gagarar
Fulani tayi bayan an tabbatar da bata je gidan su ba, ba kuma wani da zata je
wajen sa, number driver da tata duk suna shiga amma kuma babu answer. Waya
Maimartaba yayi a dare ya sanar da yan sanda abinda yake faruwa, a take ya
tashi jami'an tsaron ko ta kwana, suka bazama neman, in da aka samu wayar Iman
din da ta driver a cikin makarantar in da aka ajiye a waje daya cikin wata
farar leda.
  Tsawon daren babu wanda ya runtsa a tsakanin su,
in da suka gama tabbatar da sace su akayi, kuka sosai Fulani take tana hango
kalar tashin hankalin da muhammad zai shiga idan ya dawo. Zuwa safiya labari ya
fara fita, bayan Maimartaba sunyi waya da gwamna, da wasu manyan jami'an tsaro,
cikin kankanin lokaci labari ya baza lungu da sako na k'asar har ma da kasashen
dake da makfwataka da k'asar.
 Ana zargin an sace matar dan sarkin Adamawa, jikan
sarkin Kano babban jami'in sojoji Captain Muhammad Ahmad Santuraki haka gidajen
jaridu suka dinga wallafawa a shafukansu, nan da nan mutane suka dauka kowa na
kokarin tofa albarkacin bakin sa.
_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*
*_NANA HAFSAT(MISS XOXO) s_*
_SO DA ZUCIYA_
*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI'AR ZUCIYA_
*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_
*_HAFSAT RANO_*
_HALIN GIRMA_
*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_
*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇
D'aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k
*_Zaku tura kudin a_*
6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*
*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇
08184017082
*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇
09134848107
2/17/22, 09:45 - Buhainat: Halin Girma
37
*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇ðŸ¾_*
https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share
*_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇ðŸ¾_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb
*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇ðŸ¾_*
https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS
*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇ðŸ¾_*
https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw
*******�
Cikin matukar tashin hankali Abba ya shigo gidan, bayan abinda
ya gani a shafin BBC HAUSA, ya saka shi matukat kaduwa, idan har suna nufin
surukin sa kenan, toh kenan Iman aka sace? Innalillah wa inna ilaihi
rajiun,tashin hankalin da ba'a saka maka rana. Sauri sauri yake yana kokarin
isa bangaren Abba babba, kiran Mummy ya shigo wayar sa,
"Shikenan." Ya furta
"Sun samu labari kenan, ta tabbata da gaske ne."
Ya sake fad'a sai kuma ya daga wayar yana kokarin daidaita
tashin hankalin da yake ciki.
"Hello Abban Iman, abinda nake gani a news gaskiya
ne?"
"Labarin da nake samu yanzu kenan, yanzu muke shirin tafiya
dan samun sahihancin labarin, ki kwantar da hankalin ki, in sha Allah babu wani
abu da zai faru."
"Innalillah wa inna ilaihi rajiun." Ta furta tana
sakin kuka
"Zan tawo yanxu.."
"Sai kin zo." Ya katse kiran da sauri yana shiga ciki,
a tsaye ya tarar da Abban yana kaiwa da komowa, yana shiga Abba Musa da Abba
Kabiru suka shigo, babu wata magana da suka tsaya yi suka fice da sauri, suka
dauki hanyar gidan sarki, dan anan ne kawai zasu samu gaskiyar abinda suke so
suji, da Abba Musa yace su kira Muhammad din amma kuma sai suka fasa suka ga
gwara su je din kawai ba lallai shima ya iya daukar waya ba.
 Haka sukayi, cikin tsananin tashin hankali suka isa gidan,
bayan sun gabatar da kansu aka shigar dasu har in da maimartaba yake, babu wasu
mutane sai makusantan sa, suna jimamin abinda ya same su haka bakatatan, sannan
lokaci zuwa lokaci suna communicating da chan police station din, duk da babu
wani labari akai, dan duk wanda yayi aikin yayi masifar kwarewa wajen gudanar
da plan din nasa dan be bar duk wata hanya da za'a neme shi ba, amma duk da
haka ba zasu karaya ba, zasu yi iyakar kokarin su dan ganin an samu so cikin
kankanin lokaci.
  Labarin da su Abba suka samu yayi masifar sake
daga musu hankali dan har kwalla sai da Abba yayi ba tare da kowa ya lura,
yadda ake bada labarin rashin imanin masu kidnapping din nan kawai yake tunawa,
ga iman sam bata da hayaniya, zata cutu ainun a wajen su sai dai fatan Allah ya
bayyana ta cikin aminci da koshin lafiya.
 Suna zaune jugum kowa yana tunanin yadda Moh zai idan ya
dawo, ya ci karo da wannan mugun labarin duk uban tsaron da yake ganin ya zuba
a gidan sa, lallai addu'a ce kawai mafita a wannan zamanin, dan a duk in da
mutum yake ba wai ya tsira daga sharrin su bane.
  Haka kawai yaji kamar bashi da lafiya, duk daukin
da yake na zuwa gida ya ganta bayan tsawon lokacin sai yaji kamar duk guzarin
sa na barin sa. Tun a airport din yaga kamar ma'aikatan na kallon sa, kallon da
ya kasa gane na menene, sai kawai ya kyale hakan a wani dalili nasu da suka
sani. Daga nesa ya hango motocin sa, suna jiran isowar sa, dora jacket dinsa
yayi a saman kafadar sa ya shiga takawa zuwa wajen su dan basu ganshi ba. Sai da
ya kusa daf dasu sannan suka ankara, duk suka taho da sauri kowa na kokarin
riga dan uwansa isa, kayan hannun sa suka karba, aka bud'e masa motar ya shiga
ya zauna.
"Muje mana." Yace ganin yaki tada motar
"I'm sorry sir." Yace sannan ya tada motar suka bi
bayan su sauran. Sake neman layin Musaddik yake a lokaci daya yana neman nata
amma duk magana daya ce, switch off, kansa ne ya daure sosai ta yadda za'a ce
basu da charge a wayar su kuma tun jiya, be san me yasa ba, sai kawai yaji
kamar babu lafiya.
"Me ya faru?"
"Na'am?"
"Kaji ni ai, what's going on!"
"I'm very sorry sir, bamu san yadda akayi hakan ta faru ba,
amma we are trying our best kuma gaba daya k'asar ma."
"Ban gane ba, me kake nufi?"
"Kayi hakuri sir, in sha Allah za'a gansu."
" Nace maka me ya faru? Me kake nufi?" Ya fad'a a
tsawace yana tasowa kamar zai dake shi
"Kayi hakuri sir, ana neman Madam da driver ta da House
help din, tun jiya basu daw...**
" What!!!" Ya fad'a da karfi
"We are very sorry sir!"
" Wannan zancen banza ne, zancen wofi, menene amfanin ku?
Nace menene amfanin ku?"
Ya harzuko sai kawai ya taka birki suka tsaya
" Ta yaya akayi tun jiya basu dawo ba, kuma babu wanda zai
kirani ya fad'a min? Tun jiya fa!"
" Ohhh... Innalillah wa inna ilaihi rajiun, what's going
on, me yake faruwa?"
A cikin tsananin tashin hankali yayi maganar, zuwa lokacin
idanun sa sun yi masifar kadawa, wani abu me karfi yazo ya tsaya masa a
makoshi, ya dinga jin kamar ya kamasu yayi ta bugu har sai sun fada masa yadda
akayi suka yi wannan sakacin.
  Basu wuce gida kai tsaye ba, station suka wuce
yana ta kiraye kirayen waya cikin karfin hali, ashe tuni labarin ya kai wa
shugaban su har ma da abokan tafiyar sa amma kowa yayi masa kus, ransa yayi
masifar baci, ga wani irin tashin hankali da yake ciki, yana tsoron wani abu ya
faru da ita, ba zai taba yafewa kansa ba, ba kuma zai yafewa duk wanda yake da
hannu a wannan al'amarin ba.
   Duk bayanan da ya kamata ya samu ya samu
a station, abu daya ne basu da tabbaci shine in da suke, dan duk babu waya a
tare dasu,sannan an cire tracker din dake hade da motar ta daina aiki tun daga
cikin school din anan ne last location din motar.
  Jiri ne yaji yana kokarin kayar dashi k'asa, da
sauri aka bashi kujera ya zauna yana dafe kansa, wayar sa da take ta faman kara
alamun kira ya zaro yana duba number din, Ammi ce tun dazu take son su yi
magana be samu dama ba, yace zai kirata amma kuma yasan ta kasa hakuri ne, kowa
ya shiga tashin hankali da dimuwa kasancewar kuma har an kwana amma babu wani
labari.
  Daga wayar yayi muryar sa a chan ciki, ya gaida
Ammin ta amsa cike da tausayawa tilon dan nata, tasan yana da karfin zuciya da
kokarin maida komai ba komai ba a tsawon rayuwar sa bata ga wani abu da ya
gigitashi ya firgita shi ba, amma tasan dole ne wannan tashin hankalin ba zai
iya rik'e shi ba, ba zai iya shanye shi ba ace matar ka na hannun bata gari, ba
kuma kasan abinda zai je ya dawo ba. Lallashi da ban baki ta dinga yi masa,
tana so ko yaya ne ya kwantar da hankalin sa duk da tasan ba lallai ba, yaji ta
ne kawai amma bashi da sukunin nan, yana cikin wasiwasi da tunanin wanda zai
aikata masa wannan danyen aikin, idan kidnapping dinta akayi saboda ransom
yasan tabbas zasu neme su a tsakanin kwana uku, amma kuma idan ba dan hakan
bane fa? Tsoro ne ya kara kamashi, ya mike da k'yar cikin wasiwasin abinda zai
je ya dawo, baya fatan wani abu daban ya bullo wanda be taba tunani ko hasashe
ba, a tunanin sa duk wani me matsala dashi ba zai wuce gidan su ba, Kamal da mahaifiyar
su, wambai da sauran masu goyon bayan Kamal din, bayan su, baya tunanin akwai
wani da wata matsala ta hada su da har zai iya yi masa haka.
  Tunanin sa ne ya katse, yana tuna abinda yake
cikin flash din nan da ya bawa Musaddik, yana bukatar sake dubawa ko zai samu
wata amsa a cikin video din, amma kuma ya kalla yafi sau nawa, sai dai kamar
akwai wani abu da yake missing, be san menene ba, amma kuma zai koma baya ya
sake dubawa sosai.
Tunanin sa ne ya tsaya
akan Kamal, dalilin da ya kaishi bangaren sa har ya ajiye masa wannan macijin
robar, babu wani abu da ya dauka bayan wannan ajiyar da yayi,tashi yayi da
sauri
"Tracker ce!"
Ya furta ba tare da yasan
a fili yayi maganar ba.
"Me kake tunani?" Shugaban yan sandan yace shima yana tashi
tsaye
"Kwanakin baya an ajiye min abu me kama da micijin robar
irin na wasan yara a adamawa,ina kyautata zaton tracker ce a jiki, ya akayi
nayi missing step din?"
"Wa kake tunani?"
" Bana tunanin kowa, amma koma waye ne, yana da alaka da
wannan case din."
" Ina macijin robar."
" Yana gida!"
" Nan ko adamawa?"
" Yana nan..."
"Ok muna bukatar shi ko zai taimaka mana wajen binciken
mu."
" Shikenan."
Hannu ya mik'a masa
" Sai naji daga gareku."
" In sha Allah zamuyi kokarin mu."
" Nagode." Ya juya ya fice yana ayyana yadda zai fara
bibiyar su tamkar yadda suka dade suna bibiyar sa suma.
" Kamal...! I'm coming for you."
A waje ya tarar dasu Abba da wasu yan tsirarin makusantan fada,
sai Musaddik da yake zaune daga gefe, wani kallo Moh yayi masa suna gaisawa
dasu Abba suna jajantawa juna, sai ya taso ya iso wajen su, ya tsaya daga gefe
suka gama gaisawa, tafiya Moh yace su Abba suyi saboda daren da ya fara yi
sosai, sallama sukayi masa akan zasu dawo gobe jikin kowa a mace suka tafi
gida.
" Ina ka shiga?" Ya jeho masa tambayar bayan ya raka
su Abba da ido sanda suke barin station din
"Ina gida, bansan me yake faruwa ba saboda an dauke min
waya a masallaci bayan mun idar da sallah jiya, sai Mom ce take fad'a min wai
meenal ta gani a media shine...."
"Is ok." Yace yana yin gaba
" Menene kake shirin yi next?" Ya bishi yana tambayar
shi
" Me zanyi? Bayan case din yana hannun da ya dace, sai mu
zuba ido mu gani."
Yayi maganar kamar be
damu da abinda ya farun ba, gid'a kai Musaddik yayi ya cigaba da bin bayan sa
ganin yadda yake sauri kamar zai tashi sama. Har wajen mota ya rakashi, ya
tsaya daga baya maimakon ya shiga kamar yadda suka saba, alamar ya akayi Moh
yayi masa ganin ya toge daga baya be shigo ba
" A mota nazo, zamuyi waya Allah ya bayyana ta Allah ya
rufa asiri."
" Ok."
Kawai yace ya zuke glass
din motar sama, suka bar wajen.
"His acting strange, amma tun yaushe?"
Ya tambayi kansa yana mamakin yanayin Musaddik din, share zancen
yayi kawai ya lumshe idon sa, kirjin sa na masa wani irin suya.
A harabar masarautar
suka tsaida motocin, aka bud'e masa ya fito ya nufi ginin bangaren Takawa,
yanayin tafiyar sa kadai zaka kalla ka gane tsantsar damuwar da tayi masa
dabaibayi, har be san kalar tunanin da ya kamata yayi ba, a wanne hali take? Me
taci me suke mata? Duk shin yake masa yawo akai, a daren yau ba sai gobe ba,
zai fara aikin da yake ta jinkirtawa tsawon lokaci yana jiran right time kamar
yadda yasha cewa, sai dai yanzu yana ji aransa shine right time din.
Tun da ya shigo Takawa
yake kallon sa cike da tausayawa, akwai sauran dauriya da jarumta a tattare
dashi duk kuwa da babu kaso mafi rinjaye na karsashin sa, amma karya kake daga
kallon fuskar sa ka iya tantance abinda yake wakana a zuciyar sa. Hakan ya dade
yana bashi nasara akan duk mutanen da basa son shi, dan be basu kofar da zasu
gano lagon sa ba, kuskuren sa daya, da yake kyautata zaton shi ya basu damar
cutar dashi, shine yadda ya kasa boye son da yake mata, har ya zama musu wani
tsani na ganin sun kaishi k'asa.
Ya jima da sanin Kilishi
bata son ko ganin wulgawar shi, haka Kamal yana cikin jerin mutanen da zasu iya
yin komai don ganin bayan sa, sai kuma wambai da wasu mukarrabn fadar, sai dai
asalin kiyayar ba tashi bace, ta mahaifiyar shi ce da suke ganin an auro ta
daga gari irin na kano, suna ganin kamar hakan zai saka kanawa su zama sune
zasu mulke su. Sai dai idan ka tattara duk wadannan mutanen toh zaka samu basu
da wata alaka da iman din, balle idan sun cutar da ita su amfana da wani abu,
hakan ya saka kansa ya sake chunkushewa, ya rasa kalar tunanin da zai.
Zubewa yayi agaban
Takawar, sai a lokacin yaji kamar an zare duk wani karfin zuciyar sa, yaji
bashi da sauran katabus, yaji komai masa ya saki, sai ya dinga jin sa tamkar
wani karamin yaron da aka dake shi aka kuma hanashi kuka.
"Karka yi kokarin shanye bacin ran da kake ciki muhammadu,
ka fitar da komai zaka ji sauki."
Jan jikin sa yayi zuwa gaban Takawan, ya kwantar da kansa a
saman cinyar sa.
Ya jima sosai a haka,
kafin ya fara jin nutsuwa na saukar masa, sai a lokacin ya dago, ya zauna
daidai.
"Sannu, babu abinda zai faru in sha Allah, zasu dawo lafiya
lou."
"In Sha Allah."
***Babu wanda batan Iman be girgiza ba, hatta Mama da take
ikirarin bata son ta sai da taji babu dadi, gidan ya cika duk kowa ya zo suna
zaman jajantawa juna, zeenat dama ko da Habib ya kaita gidan su Bashir din
achan suka same shi, yace su dawo zai zo da daddare sai su tafi, haka suka sake
kwaso kafa suka dawo gashi shiru be zo ba har washegari sai kuma wannan bakin
labarin.
Mummy da Mamma sun zo a
ranar suma, suka sauka a gidan Iman din, kana kallon su kasan suna cikin tashin
hankali, kowa baya cikin nutsuwar sa musamman Abba, da mahaifiyar ta wanda suka
fi kowa kusanci da ita idan ka cire mijinta. Shi ba zaka taba gane ainahin
yanayin da yake ciki ba. Tunda ya shigo gidan ya shige daki ya kulle kansa, ya
dauko system din sa ya jona ta, yayi playing video din nan yana son ganin wani
abu. Ya dade sosai a dakin, har ma suka manta da ya shigo gidan, ba laifi gidan
da mutane wanda suka zo daga chan gidan sarki, sai su Ya Maryam da yan uwa dai
na kusa. Duk suna jiran tsammani.
***Sosai take galabaita saboda aman da take ta faman yi, babu
wani abu da yake zama a cikin ta komai taci sai ta dawo dashi, zuwa lokacin ta
gama galabaita dan ko tashi bata iyayi komai sai dai Ummimi tayi mata. Sau biyu
yana fad'a musu cewa gimbiya ta bata da lafiya amma suka yi biris da ita, suka
kyaleta a cikin wahalar suna sane da labarin yadda ake neman su babu dare babu
rana, duk wani moves din da jami'an tsaron suke suna sane dashi.
Sigari ya zuka ya
fezar, sannan ya karbi sabbin layukan da ya saka aka kawo masa wajen guda
hamsin, daya ya dauka, ya mik'a hannu ya dauki yar karamar waya a gefen sa ya
saka, ya hau kai yayi murmushi ya shiga text message ya saka number Moh, ya
rubuta
_"Ba kudi muke bukata ba, rayuwar ka muke bukata a matsayin
fansa ga rayuka biyu masu muhimmanci a wajen ka, matar ka da cikin da take
dauke dashi." _
Yana tura wa ya balla sim din, ya kyalkyale da mahaukaciyar
dariya.
_" Let the game begins Captain MAS!" _
_ZAFAFA2022🔥_*
*_NANA HAFSAT(MISS XOXO_*
_SO DA ZUCIYA_
*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI'AR ZUCIYA_
*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_
*_HAFSAT RANO_*
_HALIN GIRMA_
*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_
*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇
D'aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k
*_Zaku tura kudin a_*
6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*
*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇
08184017082
*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇
09134848107
8
2/19/22, 19:58 - Buhainat: Halin Girma
38
*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇ðŸ¾_*
https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share
*_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇ðŸ¾_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb
*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇ðŸ¾_*
https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS
*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇ðŸ¾_*
https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw
****
Zaune yake a office din commissioner of police lokacin da
message din ya shigo wayar, karantawa yayi yana kai karshe ya mike tsaye da
sauri.
"Ya akayi?" CP ya tambaya shi yana kallon yana yin sa
"Akwai matsala..." Sai ya mik'a masa wayar ya soma
zagaye a cikin office din cikin tsananin tashin hankali, idan har akwai ciki a
jikin Iman toh lallai tana cikin halin tashin hankali, yasan yadda ciki
musamman a watannin farko yadda yake wahalar wa yawa yawan mata suna shan
wahala kafin ciki yayi kwari wasu kamar zasu rasa ransu saboda tsabar wahala.
Ya take ciki yanzu? Me take ci?
"Akwai wani da kake da matsala dashi banda matsala ta cikin
gida?"
CP ya tambaye shi bayan ya maimaita karanta sakon fiye da sau
goma, har ya gano abu daya a cikin sakon, akwai kiyayye me zafin gaske tsakanin
duk wanda ya turo sakon, duk wanda yake son ranka ba karamin kiyayye yake maka.
 Girgiza kai yayi ba tare da yayi magana ba,
"Idan ka gamsu da maganganun da mukayi, lallai muna da
bukatar Kamal a binciken mu, domin idan har ka tattara bayanan baya da na yanzu
zaka gane akwai wani abu da yake a boye a bayan dukkan cases din, case din ka
da Laila, evidence din da ya wanke ka, sannan matar ka, zai iya yiwuwa wani ne
da yake son ta tun ba yanzu ba, ko kuma wanda yake da matsala da kai ne amma
shi da kansa yake son daukar fansa shiyasa har yayi kokarin wanke ka a baya,
duk wannan tunani na ne, ban ce ya zama gaskiya ba, amma ina ji a raina, cases
din suna da alaka da juna."
Zama ya kuma yayi a kujerar da ya tashi yana tattare bayanan
dukka a kwakwalwar kansa, jiya baki daya ranar a cikin bincike yayi ta, babu
mutum daya da binciken sa ya nuna masa sai Kamal. Evidence din farko shine
sanda ya shiga bangaren sa, sai na biyu da suke zaune suna magana da wani mutum
ya sunkuyar da kansa, wata mace a gefen sa itama babu fuskar ta, fuskar Kamal
din ce kadai ta nuna wanda ya tabbata shi be sani ba, yana kyautata zaton gadar
zare suka danawa Kamal din sukayi amfani da son mulkin sa suka samu abinda suke
so sannan suka yi dumping din sa.
"Duk abinda ya kamata ayi, ayi Sir."
"Zamu fara da Kamal, ina fatan hakan ba zai zama matsala ga
Maimartaba ba."
"In Sha Allah." Yace yana mikewa, jiri ne ya debe shi,
yayi kamar zai fadi da sauri CP ya tashi yana riko shi
"Subhanallah, Capt akwai matsala ba, sai ka daure saboda
tana matukar bukatar taimakon ka a wannan gabar."
Gid'a masa kai yayi yana rik'e kansa da yake mugun sarawa, be
runtsa ba tunda ya diro garin Kano, ba kuma yajin idan ka cire ruwa ya sakawa
cikin sa wani abu, sai da ya dawo daidai sannan ya mike yayi masa sallama, ya
rakashi da ido yana yaba wa kwazon sa.
***Gidan su Iman din ya wuce kai tsaye, dan sunyi waya da Abba
da safe yake ce masa bashi da lafiya, kamar ma bp din sa ne yayi sama, yasan
batan Iman din ne ya saka shi shiga matsalar.
  A kofar gida ya tarar da Habib da saurayin nan na
ranar nan, dauke kai yayi kamar be gansu ba, sai da Habib din ya taso yazo
wajen sa yana kokarin kiran waya.
"Sannu da zuwa."
"Ah... Babban Yaya."
Ya mik'a masa hannu suka gaisa, sannan yayi masa jajen abinda ya
faru, suna maganar Mahfuz ya karaso wajen, ya mik'a masa hannu kansa tsaye,
kamar ba zai bashi hannun ba, sai kuma ya mik'a masa a dakile suka gaisa.
"Zanga Abba."
"Owk Bismillah."
Yayi gaba, shi kuma suka biyo bayan shi tare da Mahfuz har part
din su, Abba na kwance a falo kan doguwar kujera, Mama ta shiga ciki dauko
Hijab suka shigo, ya durkusa har k'asa ya gaida Abban, wanda yake kallon sa
ciki da tausayawa, ya ga dauriyar sa sosai dan kana kallon sa zaka gane yadda
ya tabu, ya rame sosai amma be karaya ba, be kuma zauna ba tun da ya dawo.
"Akwai labari ne muhammadu?"
"In sha Allah Abba, ana iyakar kokari."
"Toh basu kira ba har yanzu ko?"
"Basu kira ba Abba."
"Shikenan Allah ya dawo mana dasu cikin koshin
lafiya."
"Amin Abba"
"Sannu da kokari, kai ma Allah ya biyaka, Allah ya tona
asirin azzalumai, tun jiya ban runtsa ba, na rasa in da zan saka raina naji
dadi, shikenan mutun bashi da daraja a k'asar nan tamu? Ace satar mutum tafi
satar kaza sauki? Wannan wacce irin musiba ce... Allahumma ajirni fi
musibati..."
"Allah ya bayyana su."
" Amin ya Allah. "
Suka hada baki gaba daya, shigowar Mama da Zeenat a bayan ta ne
ya katse maganar da Moh yaso yayi, ya dan kalle su sai ya dauke kai ya maida
wajen Abba da alamun sa ya nuna yana jin jiki. Gaisawa sukayi da Mama sama sama
tayi masa jaje, sannan Zeenat da gaishe shi itama ya amsa yana mikewa.
"Bari na koma Abba, duk yadda ake ciki zan kira dan Allah
ka kwantar da hankalin ka."
"Shikenan, Allah yasa muji alkhairi."
" Sai anjima." Ya dan kalli gefen da Mama take ya
fad'a sannan ya fice Habib da Mahfuz suka bi bayan sa, sun kusan kai gate din
gidan Mahfuz yace
" Zan iya taimakawa."
Tsayawa chak Moh yayi da tafiyar da yake ya juyo.
"Idan har zaka yarda zan iya taimakawa."
"How? Ta yaya?"
"Security ne from an intelligent agency a UK."
"Sounds good."
Moh yace yana dan rage hadewaar fuskar sa. Sai ya bud'e hannun
sa alamun babu matsala yace
"Idan har zaka iya taimakawa, shikenan sai muje ko?"
"Let me freshen up, zan zo daga baya. Ina zan same
ka?"
" Habib ka rakoshi gida na, don't take long please."
" In Sha Allah."
Juyawa yayi ya fice su kuma suka koma ciki don Mahfouz ya
shirya, anan suka tarar da Gaji a part din ta saka Abba a gaba tana ta rusa
kuka, bata samu labarin ba sai da Moh yazo yanzu sannan tasan abinda yake
faruwa, taji zancen a radio har ta tausaya amma bata kawo Iman bace ,bata ma
fuskanci zancen ba kwata kwata ma gaba daya. Baki Abba yake bata akan tayi
hakuri amma taki, sai kuka take ita lallai sai an kaita gidan Iman din, a dole
haka Abba ya saka tabi su Habib din ko ta barshi ya ji da kansa shima kawai
dauriya ce irin ta namiji.
  Yana shiga gidan ya tarar da motocin masarauta,
ciki ya shiga kansa tsaye, da mamaki yake kallon Fulani a zaune a falon nasu,
tare da mummy da Mamma sai wasu matan, suna zaune jingum jingum cikin alhini da
jimami, daga gefe hadiman Fulanin ne suma a falon, kallo daya yayi ma duk matan
falon, ya karasa gaban Fulanin ya durkusa ya gaishe ta, ta amsa muryar ta na
rawa alamun bata dade da gama kuka ba, juyawa yayi ya gaida su mummy
wanda sai a lokacin ya samu ganin su, ta fad'a tayi fayau amma kuma a nutse
take sosai, sai yace ma Mamma ta fita fita hayyacin ta, wuce su yayi zuwa ciki,
suka rakashi da kallon tausayawa.
  Dafe kansa yayi bayan ya zauna a gefen gadon,
komai nata yana nan a dakin hatta da handouts din da ta fito dasu ranar da zata
tafin gasu nan a saman gado, be san me yasa abubuwan suka juye masa a yadda be
yi zato ko tsammani ba. Wayar sa ce tayi kara, ya dauka yana kallon sunan, Bubu
ne
"Menene alakar Kamal da batan matar ka?"
"Barka da rana Bubu..."
"Barka dai, ya mukaji da alhinin? Allah ya bayyana su cikin
koshin lafiya."
"Amin ya Allah."
"Ina jin ka, menene alakar Kamal da batan matar ka?"
Saman goshin sa ya shafa kad'an, kafin yace
"Bincike ne ya kawo hakan Bubu."
"Shikenan, Allah ya sa muji alkhairi."
"Amin ya Allah." Yace sannan sukayi sallama.
  A tsammanin sa Musaddik zai neme shi da zarar
gari ya waye, ya kuma rakashi duk wani waje da zai je, amma kuma ga mamakin sa
sai gashi har rana ta daga babu ko waya daga gareshi, bayan yafi kowa sanin
muhimmancin da Iman take dashi a wajen sa, shine mutum na farko kuma na karshe
da ya yarda dashi kaf duniyar nan idan ka cire mutane hudu mafiya kusanci
dashi, Ammin sa, Takawa, Aji da Bubun sa, bayan su be yarda da kowa ba sai Musaddik
wanda ya yarda da tsantsar kaunar da shi ma yake masa, fiye da wadda shi yake
masa, say da yawa Musaddik ya sha shiga rigima saboda shi, ya kuma sha shiga
tashin hankali saboda shi, amma kuma ya kasa gane dalili daya, da zai saka
Musaddik din kasa jajanta masa kamar yadda ya saba a baya, duk wani abu masa
tare sukeyi.
  Tashi yayi yana dan zazzagaya dakin, yana so ya
dauke tunanin daga zuciyar sa,yana so yayi wa Musaddik din uzuri a karo na
farko kasancewar dan Adam ajizi ne, watakila wani uzurin ne ya danne wannan
din. Wayar sa ce tayi kara, ya matsa yana dubawa, sakon text message ne from an
unknown number, da sauri ya dauki wayar yana dubawa.
_"Ka shirya?"_
Da sauri ya maida masa reply
"Waye kai, me kake so?"
Sai da aka dau lokaci sannan akayi reply da wata number daban
"Ashe har kana da lokacin tsayawa tambayar waye bayan
rayuwar matar ka da ke cikin hatsari."
"Ina zamu hadu? Ka dawo da ita nayi maka alkawarin zan kawo
maka kai na da kai na."
Nan ma sai da aka sake daukar lokaci kafin yayi masa reply da
wata number daban kuma
_"Idan na shirya zan neme ka, karka bata lokaci wajen
tracking din number, ba zaka taba samu ba." _
Kiran number yayi da sauri, amma sai yaji ta a kashe, ya bi
sauran layukan da sukayi magana suma duk a kashe, text message ya turawa CP na
numbers din dukka.
  Kira ne ya shigo wayar sa daga gate din gidan,
kamar be zai daga ba sai kuma ya tuno da zuwan su Habib, dagawa yayi suka
tambaye shi ko yasan su, yace a farsu su shigo brothers din Iman ne, da haka ya
kashe ya sauya rigar sa zuwa mara nauyi saboda zafin da yake ji.
***Dagata Ummimi tayi ta taimaka mata bayan ta gama amai, ta
gyara wajen ta dawo ta tsugunna a gabanta tana mata sannu, da kai ta amsa mata,
ta rufe idon ta hawaye ya gangaro mata. Shigowa sukayi su hudu, shine a gaba
suna bin bayan sa, ya zo gabanta ya durkusa ya saka hannu ya dago kanta.
"Fine Lady." Ya shafi gefen fuskar ta, ta saka ragowar
karfin da take dashi ta ture shi, ya tuntsure da dariya yana kallon ta
"Ga Dr nan zai duba min ke, dan ina tunanin nine zan maye
gurbin Capt bayan na aikashi barzahu, kina da kyau."
"Dr matso, a duba min da kyau idan har ciki ne, a cire shi
ko ta yaya ne, ba zan iya jure ganin sa ba, kaga auren mu ba zai dau lokaci ba
idan aka cire shi."
Matsawo likitan yayi, ya bud'e idon ta, sannan ya taba goshin
ta, ya dauko wata roba a cikin kayan sa ya mikawa Ummimi.
" Gashi fitsari zatayi."
Kin karba tayi, na bayan ya daka mata tsawa, ta karba da sauri
tana daga Iman din, dukkan su hawaye suke amma babu me bud'e baki yayi musu
saboda tsoro. Tare sukaje tayi fitsarin suka fito ta dawo ta kawo masa, ya
karba a wajen ya duba, ya kuma tabbatar da ciki ne, yan tambayoyi yayi mata
akan period dinta ta amsa tana kuka.
"Ciki ne oga, na sati shida."
"Ya za'a yi dashi?"
"Ba zai wahalar fita ba, tunda karami ne. Yanzu dai zan
dawo sai nazo da maganin da zata sha."
"Yayi kyau, rakashi yaro." Rik'e masa jaka wanda aka
kira da yaro yayi suka fita, sannan shi ma suka fita.
"Hello... Samha baby." Ya fad'a da yaji ta daga wayar
"Eh tana hannu har yanzu."
"Eh ya tabbatar da ciki ne, amma za'a cire shi tunda baki
da bukatar shi."
"A ah... Babu fa abinda zan yi wa masoyinki, kawai wata yar
harkalla ce zamu karasa ta. "
" Yawwa toh" tace tana jin dadi.
" Sai mun sake magana ko? "
" Amma ai bana samun ka kwata-kwata a waya, me yasa?"
" Babu komai, idan akwai bukatar muyi magana ni zan kiraki
da kai na."
" Shikenan."
Dariya yayi sosai bayan sun gama maganar, be san bata da tunani
ba kwata-kwata sai yanzu, amfani yayi da ita ya samu abinda yake so, ba kuma
zai kyale wanda ta kwallafa rai akai ba, ba zata taba samun cikar burin ta ba
in dai yana numfashi.
***A waje ya tarar da su Habib din bayan ya gama parker motar, ganin
tare suke da Gaji ya sakashi saurin karasawa ya taimaka mata ta fito, sannan
suka gaisa ya saka aka rakata ciki su kuma yace su biyo shi garden dake baya.
Kujeru ne a wajen, ya zauna sannan suka zauna suma, yana karantar yanayin
Mahfuz din, sai a lokacin yayi masa kallon tsaf, ya kuma fahimci hakan yanayin
sa ne, ku kuma yanayin environment din da ya taso kamar yadda Habib yayi masa
bayani dazu.
"Ta yaya zaka iya taimakawa?" Yace bayan ya gama
nakaltar yanayin sa, gyara zama yayi sosai, yayi murmushi sannan yace zai masa
yan tambayoyi,da ka ya amsa masa ya bashi go ahead.
"Babu wani message ko kira da ka samu daga wajen kidnappers
din?"
"Akwai."
"Zan iya gani?"
"Why not?" Ya mik'a masa wayar, ya karba ya duba
messages din dukka, ya jima yana sake dubawa kafin ya mik'a masa wayar sa
"Kayi tunani sosai, wanene kake da matsala dashi, irin
wadda kasan lallai da zai samu dama akan ka zai iya aikata maka komai?"
"Babu shi, bansan waye ba gaskiya."
" Babu ko old friend? Ko abokin aiki?"
Shiru yayi cikin tunani
" Think... "
_" Zan dawo komai daren dadewa, sai na dauki fansa akan ka,
ko da zan karar da komai da na mallaka ma duniya sai na maida rayuwar ka abun
kwatance! "_
"JABIR! " Yace yana mikewa tsaye da sauri, tashi Mahfuz
yayi shima yana kallon sa
" Waye shi. "
" Aboki na ne, abokin aiki na ne. "
" Recently na samu labarin ya zama babban terrorist kuma
yana da connection da manyan k'asar, bayan shi bana tunanin akwai wanda zai
bukaci rayuwa ta, babu. "
"Ya akayi na manta? Ya akayi? "
" Kasan in da za'a same shi? "
Girgiza kai yayi,
" Ban sani ba. "
Komawa sukayi suka zauna, Mahfuz ya ciro biro da paper ya rubuta
wani abu, daidai lokacin da Moh ya daga wayar Musaddik yace ya same shi a
garden, yana ajiye wayar sai gashi ya zagayo dama chan yana cikin gidan, da
kallo Mahfuz ya bishi kafin ya karaso wajen yace
"Waye shi?"
"Best friend dina ne."
"Ok." Yace a gajarce ganin ya karaso, ya mik'a musu
hannu suka gaisa amma da ya bawa Mahfuz hanun sai ya rik'e hannun nasa har sai da suka kalle shi dukka,
sai ya saki yana murmushi ya jingina da kujerar da yake kai, wani kallo
Musaddik yayi masa ya zauna yana maida hankalin sa kan Moh.
"I'm very sorry Capt..."
"Babu komai, nasan wani uzuri ne dakai." Ya katse shi
kafin ya karasa.
"Babu wani progress ko?" Yace
"Babu."
"Allah ya bayyana su."
"Amin."
"Ya aiki?" Mahfuz ya tambayi Musaddik unexpectedly
"Aiki Alhamdulillah."
"Wanne aiki kake?"
"Harkar kwangila, kaifa?"
"Detective!"
Wani kallo Musaddik yayi masa, yayi shiru,.sai kuma ya kalli Moh
"Naga kamar kana da baki, dama inaso muyi maganar flash din
nan ne tunda naga ka dawo."
"Flash?" Mahfuz yayi karaf ya tambaya
"Let's talk about that later." Moh yace sai ya mik'a
wa Musaddik hannu
"Suna ina?"
Sosa kansa yayi
"Dalilin da yasa kaga kamar ina janye kaina a case din nan
kenan, wallahi bansan ya akayi ba, na rasa su gaba daya."
"What!"
"Kayi hakuri,ranar da aka sace wayata aka hada dasu gaba
daya, bansan ya zan maka bayani ba, nasan kuma muhimmancin flash din a wajen
ka, shiyasa na kasa nutsuwa."
Murmushi kawai Mahfuz yayi, ya dire pen din hannun sa akan dan
deborin da yake gaban sa, ya dora hannun sa akai ya jingina yana masa kallon
tsaf.
" Idan nace wani abu zaka yarda dani?"
Girgiza masa kai Moh yayi dan maganar batan flash din ba karamin
bashi mam I'llaki tayi ba.
"Ina bukatar yara hudu cikin yaranka na gate."
" Me zasuyi maka?" Musaddik yace ransa a bace.
" Wait and see." Yayi murmushi, shi Moh ba gane kan
maganar ba kwata kwata, yayi dai abinda Mahfuz yace ya kirawo su suka zo, suka
tsaya daga gefe, tashi Mahfuz yayi ya zagayo ta bayan Musaddik,
"Take off your mask!"
"Kamar ya?"
"Me kake nufi Mahfuz?" Moh da shima ya mike ya fad'a
cike da mamaki
" This man is deceiving you, ka kalli hannun sa, ka kalli
fuskar sa, akwai banbancin skin color, he's definitely using a mask, idan har
ya musa, zan tabbatar maka."
"Noo...you are mistaken, wannan Musaddik ne, trusted friend
dina ba zai taba deceiving dina ba,you cannot accused somebody without a
proof."
" Shine zan maka proving yanzu ai, wait and see, guys... Ku
rik'e shi."
" Dakata!"
Moh yace ransa na baci, ba zai dauki wulakanta Musaddik yana
kallo ba.
"Waye wannan Capt, waye zai zo ya shiga tsakani na da
kai?"
"Calm down aboki na, misunderstanding aka samu amma zan
masa magana..." Sai ya juya wajen Mahfuz din
"Let's call it a day, zamuyi magana gobe, Habib ku jirani a
wajen mota."
"Muje Mahfuz." Wani
kallo yabi Musaddik din dashi, sannan ya juya suka bar wajen da Habib.
Juyawa kan Musaddik yayi da ransa yayi masifar baci, ya shiga
bashi hakuri akan abinda Mahfuz din yayi, yace ya jirashi yana zuwa bari ya
sallame su. Yana barin wajen ya ciro waya, ya kira shi yana matsawa chan gaba.
"Akwai matsala." Yana dagawa yace
"Ya fara suspecting dinka ne?"
"Be fara ba, wani banzan yaro ne bansan daga ina yazo ba,
yaso dole sai ya nuna masa gaskiyar mask da na saka..."
"Ya yadda?"
"Be yarda ba, kasan ya yarda dani sosai, so ba zai taba
kawowa ba. "
" You have to be very careful, shi kuma yaron zan san yadda
zan yi dashi. "
" Ok sir. " Ya kashe wayar yana juyowa, sukayi ido
biyu da Moh da yake tsaye a bayan sa kamar mayunwacin zakin da ya shekara be ce
ba.
***Assalamu alaikum sisters, masu korafi naga wasu daga cikin
korafin ku, ina mai baku hakuri akan matsalolin da aka samu, dan gane da rashin
posting halin girma shekaran jiya da jiya, hakan ya faru ne sakamakon ciwon
hakorin da ya matsa min hade da zazzabi, wanda har ta kai ban iya samun duba
sakonni ba balle har na iya zaman rubutu
Duk cikin zafafa biyar
babu wadda a cikin mu take jin dadi a duk sanda batayi posting ba, Allah ne
shaida ana iyakar kokari wajen ganin Anyi abinda ya dace. Sai dai idan abu ya
sha kan mutum a ba yadda ya iya. Allah ya huci zuciyar duk wanda ransa ya baci
ta dalilin jira ko wani abu, ba da gangan bane wani lokacin kuma ajizanci ne na
dan Adam.
Allah ya rufa asiri ya sa mu gama lafiya
2/21/22, 08:16 - Buhainat: Halin Girma
38
*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇ðŸ¾_*
https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share
*_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇ðŸ¾_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb
*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇ðŸ¾_*
https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS
*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇ðŸ¾_*
https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw
****
Zaune yake a office din commissioner of police lokacin da
message din ya shigo wayar, karantawa yayi yana kai karshe ya mike tsaye da
sauri.
"Ya akayi?" CP ya tambaya shi yana kallon yana yin sa
"Akwai matsala..." Sai ya mik'a masa wayar ya soma
zagaye a cikin office din cikin tsananin tashin hankali, idan har akwai ciki a
jikin Iman toh lallai tana cikin halin tashin hankali, yasan yadda ciki
musamman a watannin farko yadda yake wahalar wa yawa yawan mata suna shan
wahala kafin ciki yayi kwari wasu kamar zasu rasa ransu saboda tsabar wahala.
Ya take ciki yanzu? Me take ci?
"Akwai wani da kake da matsala dashi banda matsala ta cikin
gida?"
CP ya tambaye shi bayan ya maimaita karanta sakon fiye da sau
goma, har ya gano abu daya a cikin sakon, akwai kiyayye me zafin gaske tsakanin
duk wanda ya turo sakon, duk wanda yake son ranka ba karamin kiyayye yake maka.
 Girgiza kai yayi ba tare da yayi magana ba,
"Idan ka gamsu da maganganun da mukayi, lallai muna da
bukatar Kamal a binciken mu, domin idan har ka tattara bayanan baya da na yanzu
zaka gane akwai wani abu da yake a boye a bayan dukkan cases din, case din ka
da Laila, evidence din da ya wanke ka, sannan matar ka, zai iya yiwuwa wani ne
da yake son ta tun ba yanzu ba, ko kuma wanda yake da matsala da kai ne amma
shi da kansa yake son daukar fansa shiyasa har yayi kokarin wanke ka a baya,
duk wannan tunani na ne, ban ce ya zama gaskiya ba, amma ina ji a raina, cases
din suna da alaka da juna."
Zama ya kuma yayi a kujerar da ya tashi yana tattare bayanan
dukka a kwakwalwar kansa, jiya baki daya ranar a cikin bincike yayi ta, babu
mutum daya da binciken sa ya nuna masa sai Kamal. Evidence din farko shine
sanda ya shiga bangaren sa, sai na biyu da suke zaune suna magana da wani mutum
ya sunkuyar da kansa, wata mace a gefen sa itama babu fuskar ta, fuskar Kamal
din ce kadai ta nuna wanda ya tabbata shi be sani ba, yana kyautata zaton gadar
zare suka danawa Kamal din sukayi amfani da son mulkin sa suka samu abinda suke
so sannan suka yi dumping din sa.
"Duk abinda ya kamata ayi, ayi Sir."
"Zamu fara da Kamal, ina fatan hakan ba zai zama matsala ga
Maimartaba ba."
"In Sha Allah." Yace yana mikewa, jiri ne ya debe shi,
yayi kamar zai fadi da sauri CP ya tashi yana riko shi
"Subhanallah, Capt akwai matsala ba, sai ka daure saboda
tana matukar bukatar taimakon ka a wannan gabar."
Gid'a masa kai yayi yana rik'e kansa da yake mugun sarawa, be
runtsa ba tunda ya diro garin Kano, ba kuma yajin idan ka cire ruwa ya sakawa
cikin sa wani abu, sai da ya dawo daidai sannan ya mike yayi masa sallama, ya
rakashi da ido yana yaba wa kwazon sa.
***Gidan su Iman din ya wuce kai tsaye, dan sunyi waya da Abba
da safe yake ce masa bashi da lafiya, kamar ma bp din sa ne yayi sama, yasan
batan Iman din ne ya saka shi shiga matsalar.
  A kofar gida ya tarar da Habib da saurayin nan na
ranar nan, dauke kai yayi kamar be gansu ba, sai da Habib din ya taso yazo
wajen sa yana kokarin kiran waya.
"Sannu da zuwa."
"Ah... Babban Yaya."
Ya mik'a masa hannu suka gaisa, sannan yayi masa jajen abinda ya
faru, suna maganar Mahfuz ya karaso wajen, ya mik'a masa hannu kansa tsaye,
kamar ba zai bashi hannun ba, sai kuma ya mik'a masa a dakile suka gaisa.
"Zanga Abba."
"Owk Bismillah."
Yayi gaba, shi kuma suka biyo bayan shi tare da Mahfuz har part
din su, Abba na kwance a falo kan doguwar kujera, Mama ta shiga ciki dauko
Hijab suka shigo, ya durkusa har k'asa ya gaida Abban, wanda yake kallon sa
ciki da tausayawa, ya ga dauriyar sa sosai dan kana kallon sa zaka gane yadda
ya tabu, ya rame sosai amma be karaya ba, be kuma zauna ba tun da ya dawo.
"Akwai labari ne muhammadu?"
"In sha Allah Abba, ana iyakar kokari."
"Toh basu kira ba har yanzu ko?"
"Basu kira ba Abba."
"Shikenan Allah ya dawo mana dasu cikin koshin
lafiya."
"Amin Abba"
"Sannu da kokari, kai ma Allah ya biyaka, Allah ya tona
asirin azzalumai, tun jiya ban runtsa ba, na rasa in da zan saka raina naji
dadi, shikenan mutun bashi da daraja a k'asar nan tamu? Ace satar mutum tafi
satar kaza sauki? Wannan wacce irin musiba ce... Allahumma ajirni fi musibati..."
"Allah ya bayyana su."
" Amin ya Allah. "
Suka hada baki gaba daya, shigowar Mama da Zeenat a bayan ta ne
ya katse maganar da Moh yaso yayi, ya dan kalle su sai ya dauke kai ya maida
wajen Abba da alamun sa ya nuna yana jin jiki. Gaisawa sukayi da Mama sama sama
tayi masa jaje, sannan Zeenat da gaishe shi itama ya amsa yana mikewa.
"Bari na koma Abba, duk yadda ake ciki zan kira dan Allah
ka kwantar da hankalin ka."
"Shikenan, Allah yasa muji alkhairi."
" Sai anjima." Ya dan kalli gefen da Mama take ya
fad'a sannan ya fice Habib da Mahfuz suka bi bayan sa, sun kusan kai gate din
gidan Mahfuz yace
" Zan iya taimakawa."
Tsayawa chak Moh yayi da tafiyar da yake ya juyo.
"Idan har zaka yarda zan iya taimakawa."
"How? Ta yaya?"
"Security ne from an intelligent agency a UK."
"Sounds good."
Moh yace yana dan rage hadewaar fuskar sa. Sai ya bud'e hannun
sa alamun babu matsala yace
"Idan har zaka iya taimakawa, shikenan sai muje ko?"
"Let me freshen up, zan zo daga baya. Ina zan same
ka?"
" Habib ka rakoshi gida na, don't take long please."
" In Sha Allah."
Juyawa yayi ya fice su kuma suka koma ciki don Mahfouz ya
shirya, anan suka tarar da Gaji a part din ta saka Abba a gaba tana ta rusa
kuka, bata samu labarin ba sai da Moh yazo yanzu sannan tasan abinda yake
faruwa, taji zancen a radio har ta tausaya amma bata kawo Iman bace ,bata ma
fuskanci zancen ba kwata kwata ma gaba daya. Baki Abba yake bata akan tayi
hakuri amma taki, sai kuka take ita lallai sai an kaita gidan Iman din, a dole
haka Abba ya saka tabi su Habib din ko ta barshi ya ji da kansa shima kawai
dauriya ce irin ta namiji.
  Yana shiga gidan ya tarar da motocin masarauta,
ciki ya shiga kansa tsaye, da mamaki yake kallon Fulani a zaune a falon nasu,
tare da mummy da Mamma sai wasu matan, suna zaune jingum jingum cikin alhini da
jimami, daga gefe hadiman Fulanin ne suma a falon, kallo daya yayi ma duk matan
falon, ya karasa gaban Fulanin ya durkusa ya gaishe ta, ta amsa muryar ta na
rawa alamun bata dade da gama kuka ba, juyawa yayi ya gaida su mummy
wanda sai a lokacin ya samu ganin su, ta fad'a tayi fayau amma kuma a nutse
take sosai, sai yace ma Mamma ta fita fita hayyacin ta, wuce su yayi zuwa ciki,
suka rakashi da kallon tausayawa.
  Dafe kansa yayi bayan ya zauna a gefen gadon,
komai nata yana nan a dakin hatta da handouts din da ta fito dasu ranar da zata
tafin gasu nan a saman gado, be san me yasa abubuwan suka juye masa a yadda be
yi zato ko tsammani ba. Wayar sa ce tayi kara, ya dauka yana kallon sunan, Bubu
ne
"Menene alakar Kamal da batan matar ka?"
"Barka da rana Bubu..."
"Barka dai, ya mukaji da alhinin? Allah ya bayyana su cikin
koshin lafiya."
"Amin ya Allah."
"Ina jin ka, menene alakar Kamal da batan matar ka?"
Saman goshin sa ya shafa kad'an, kafin yace
"Bincike ne ya kawo hakan Bubu."
"Shikenan, Allah ya sa muji alkhairi."
"Amin ya Allah." Yace sannan sukayi sallama.
  A tsammanin sa Musaddik zai neme shi da zarar
gari ya waye, ya kuma rakashi duk wani waje da zai je, amma kuma ga mamakin sa
sai gashi har rana ta daga babu ko waya daga gareshi, bayan yafi kowa sanin
muhimmancin da Iman take dashi a wajen sa, shine mutum na farko kuma na karshe
da ya yarda dashi kaf duniyar nan idan ka cire mutane hudu mafiya kusanci
dashi, Ammin sa, Takawa, Aji da Bubun sa, bayan su be yarda da kowa ba sai
Musaddik wanda ya yarda da tsantsar kaunar da shi ma yake masa, fiye da wadda
shi yake masa, say da yawa Musaddik ya sha shiga rigima saboda shi, ya kuma sha
shiga tashin hankali saboda shi, amma kuma ya kasa gane dalili daya, da zai
saka Musaddik din kasa jajanta masa kamar yadda ya saba a baya, duk wani abu
masa tare sukeyi.
  Tashi yayi yana dan zazzagaya dakin, yana so ya
dauke tunanin daga zuciyar sa,yana so yayi wa Musaddik din uzuri a karo na
farko kasancewar dan Adam ajizi ne, watakila wani uzurin ne ya danne wannan
din. Wayar sa ce tayi kara, ya matsa yana dubawa, sakon text message ne from an
unknown number, da sauri ya dauki wayar yana dubawa.
_"Ka shirya?"_
Da sauri ya maida masa reply
"Waye kai, me kake so?"
Sai da aka dau lokaci sannan akayi reply da wata number daban
"Ashe har kana da lokacin tsayawa tambayar waye bayan
rayuwar matar ka da ke cikin hatsari."
"Ina zamu hadu? Ka dawo da ita nayi maka alkawarin zan kawo
maka kai na da kai na."
Nan ma sai da aka sake daukar lokaci kafin yayi masa reply da
wata number daban kuma
_"Idan na shirya zan neme ka, karka bata lokaci wajen
tracking din number, ba zaka taba samu ba." _
Kiran number yayi da sauri, amma sai yaji ta a kashe, ya bi
sauran layukan da sukayi magana suma duk a kashe, text message ya turawa CP na
numbers din dukka.
  Kira ne ya shigo wayar sa daga gate din gidan,
kamar be zai daga ba sai kuma ya tuno da zuwan su Habib, dagawa yayi suka
tambaye shi ko yasan su, yace a farsu su shigo brothers din Iman ne, da haka ya
kashe ya sauya rigar sa zuwa mara nauyi saboda zafin da yake ji.
***Dagata Ummimi tayi ta taimaka mata bayan ta gama amai, ta
gyara wajen ta dawo ta tsugunna a gabanta tana mata sannu, da kai ta amsa mata,
ta rufe idon ta hawaye ya gangaro mata. Shigowa sukayi su hudu, shine a gaba
suna bin bayan sa, ya zo gabanta ya durkusa ya saka hannu ya dago kanta.
"Fine Lady." Ya shafi gefen fuskar ta, ta saka ragowar
karfin da take dashi ta ture shi, ya tuntsure da dariya yana kallon ta
"Ga Dr nan zai duba min ke, dan ina tunanin nine zan maye
gurbin Capt bayan na aikashi barzahu, kina da kyau."
"Dr matso, a duba min da kyau idan har ciki ne, a cire shi
ko ta yaya ne, ba zan iya jure ganin sa ba, kaga auren mu ba zai dau lokaci ba
idan aka cire shi."
Matsawo likitan yayi, ya bud'e idon ta, sannan ya taba goshin
ta, ya dauko wata roba a cikin kayan sa ya mikawa Ummimi.
" Gashi fitsari zatayi."
Kin karba tayi, na bayan ya daka mata tsawa, ta karba da sauri
tana daga Iman din, dukkan su hawaye suke amma babu me bud'e baki yayi musu
saboda tsoro. Tare sukaje tayi fitsarin suka fito ta dawo ta kawo masa, ya
karba a wajen ya duba, ya kuma tabbatar da ciki ne, yan tambayoyi yayi mata
akan period dinta ta amsa tana kuka.
"Ciki ne oga, na sati shida."
"Ya za'a yi dashi?"
"Ba zai wahalar fita ba, tunda karami ne. Yanzu dai zan
dawo sai nazo da maganin da zata sha."
"Yayi kyau, rakashi yaro." Rik'e masa jaka wanda aka
kira da yaro yayi suka fita, sannan shi ma suka fita.
"Hello... Samha baby." Ya fad'a da yaji ta daga wayar
"Eh tana hannu har yanzu."
"Eh ya tabbatar da ciki ne, amma za'a cire shi tunda baki
da bukatar shi."
"A ah... Babu fa abinda zan yi wa masoyinki, kawai wata yar
harkalla ce zamu karasa ta. "
" Yawwa toh" tace tana jin dadi.
" Sai mun sake magana ko? "
" Amma ai bana samun ka kwata-kwata a waya, me yasa?"
" Babu komai, idan akwai bukatar muyi magana ni zan kiraki
da kai na."
" Shikenan."
Dariya yayi sosai bayan sun gama maganar, be san bata da tunani
ba kwata-kwata sai yanzu, amfani yayi da ita ya samu abinda yake so, ba kuma
zai kyale wanda ta kwallafa rai akai ba, ba zata taba samun cikar burin ta ba
in dai yana numfashi.
***A waje ya tarar da su Habib din bayan ya gama parker motar,
ganin tare suke da Gaji ya sakashi saurin karasawa ya taimaka mata ta fito,
sannan suka gaisa ya saka aka rakata ciki su kuma yace su biyo shi garden dake baya.
Kujeru ne a wajen, ya zauna sannan suka zauna suma, yana karantar yanayin
Mahfuz din, sai a lokacin yayi masa kallon tsaf, ya kuma fahimci hakan yanayin
sa ne, ku kuma yanayin environment din da ya taso kamar yadda Habib yayi masa
bayani dazu.
"Ta yaya zaka iya taimakawa?" Yace bayan ya gama
nakaltar yanayin sa, gyara zama yayi sosai, yayi murmushi sannan yace zai masa
yan tambayoyi,da ka ya amsa masa ya bashi go ahead.
"Babu wani message ko kira da ka samu daga wajen kidnappers
din?"
"Akwai."
"Zan iya gani?"
"Why not?" Ya mik'a masa wayar, ya karba ya duba
messages din dukka, ya jima yana sake dubawa kafin ya mik'a masa wayar sa
"Kayi tunani sosai, wanene kake da matsala dashi, irin
wadda kasan lallai da zai samu dama akan ka zai iya aikata maka komai?"
"Babu shi, bansan waye ba gaskiya."
" Babu ko old friend? Ko abokin aiki?"
Shiru yayi cikin tunani
" Think... "
_" Zan dawo komai daren dadewa, sai na dauki fansa akan ka,
ko da zan karar da komai da na mallaka ma duniya sai na maida rayuwar ka abun
kwatance! "_
"JABIR! " Yace yana mikewa tsaye da sauri, tashi
Mahfuz yayi shima yana kallon sa
" Waye shi. "
" Aboki na ne, abokin aiki na ne. "
" Recently na samu labarin ya zama babban terrorist kuma
yana da connection da manyan k'asar, bayan shi bana tunanin akwai wanda zai
bukaci rayuwa ta, babu. "
"Ya akayi na manta? Ya akayi? "
" Kasan in da za'a same shi? "
Girgiza kai yayi,
" Ban sani ba. "
Komawa sukayi suka zauna, Mahfuz ya ciro biro da paper ya rubuta
wani abu, daidai lokacin da Moh ya daga wayar Musaddik yace ya same shi a
garden, yana ajiye wayar sai gashi ya zagayo dama chan yana cikin gidan, da
kallo Mahfuz ya bishi kafin ya karaso wajen yace
"Waye shi?"
"Best friend dina ne."
"Ok." Yace a gajarce ganin ya karaso, ya mik'a musu
hannu suka gaisa amma da ya bawa Mahfuz hanun sai ya rik'e hannun nasa har sai da suka kalle shi dukka,
sai ya saki yana murmushi ya jingina da kujerar da yake kai, wani kallo
Musaddik yayi masa ya zauna yana maida hankalin sa kan Moh.
"I'm very sorry Capt..."
"Babu komai, nasan wani uzuri ne dakai." Ya katse shi
kafin ya karasa.
"Babu wani progress ko?" Yace
"Babu."
"Allah ya bayyana su."
"Amin."
"Ya aiki?" Mahfuz ya tambayi Musaddik unexpectedly
"Aiki Alhamdulillah."
"Wanne aiki kake?"
"Harkar kwangila, kaifa?"
"Detective!"
Wani kallo Musaddik yayi masa, yayi shiru,.sai kuma ya kalli Moh
"Naga kamar kana da baki, dama inaso muyi maganar flash din
nan ne tunda naga ka dawo."
"Flash?" Mahfuz yayi karaf ya tambaya
"Let's talk about that later." Moh yace sai ya mik'a
wa Musaddik hannu
"Suna ina?"
Sosa kansa yayi
"Dalilin da yasa kaga kamar ina janye kaina a case din nan
kenan, wallahi bansan ya akayi ba, na rasa su gaba daya."
"What!"
"Kayi hakuri,ranar da aka sace wayata aka hada dasu gaba
daya, bansan ya zan maka bayani ba, nasan kuma muhimmancin flash din a wajen
ka, shiyasa na kasa nutsuwa."
Murmushi kawai Mahfuz yayi, ya dire pen din hannun sa akan dan
deborin da yake gaban sa, ya dora hannun sa akai ya jingina yana masa kallon
tsaf.
" Idan nace wani abu zaka yarda dani?"
Girgiza masa kai Moh yayi dan maganar batan flash din ba karamin
bashi mam I'llaki tayi ba.
"Ina bukatar yara hudu cikin yaranka na gate."
" Me zasuyi maka?" Musaddik yace ransa a bace.
" Wait and see." Yayi murmushi, shi Moh ba gane kan
maganar ba kwata kwata, yayi dai abinda Mahfuz yace ya kirawo su suka zo, suka
tsaya daga gefe, tashi Mahfuz yayi ya zagayo ta bayan Musaddik,
"Take off your mask!"
"Kamar ya?"
"Me kake nufi Mahfuz?" Moh da shima ya mike ya fad'a
cike da mamaki
" This man is deceiving you, ka kalli hannun sa, ka kalli
fuskar sa, akwai banbancin skin color, he's definitely using a mask, idan har
ya musa, zan tabbatar maka."
"Noo...you are mistaken, wannan Musaddik ne, trusted friend
dina ba zai taba deceiving dina ba,you cannot accused somebody without a
proof."
" Shine zan maka proving yanzu ai, wait and see, guys... Ku
rik'e shi."
" Dakata!"
Moh yace ransa na baci, ba zai dauki wulakanta Musaddik yana
kallo ba.
"Waye wannan Capt, waye zai zo ya shiga tsakani na da
kai?"
"Calm down aboki na, misunderstanding aka samu amma zan
masa magana..." Sai ya juya wajen Mahfuz din
"Let's call it a day, zamuyi magana gobe, Habib ku jirani a
wajen mota."
"Muje Mahfuz."
Wani kallo yabi Musaddik din dashi, sannan ya juya suka bar wajen da
Habib.
Juyawa kan Musaddik yayi da ransa yayi masifar baci, ya shiga
bashi hakuri akan abinda Mahfuz din yayi, yace ya jirashi yana zuwa bari ya
sallame su. Yana barin wajen ya ciro waya, ya kira shi yana matsawa chan gaba.
"Akwai matsala." Yana dagawa yace
"Ya fara suspecting dinka ne?"
"Be fara ba, wani banzan yaro ne bansan daga ina yazo ba,
yaso dole sai ya nuna masa gaskiyar mask da na saka..."
"Ya yadda?"
"Be yarda ba, kasan ya yarda dani sosai, so ba zai taba
kawowa ba. "
" You have to be very careful, shi kuma yaron zan san yadda
zan yi dashi. "
" Ok sir. " Ya kashe wayar yana juyowa, sukayi ido
biyu da Moh da yake tsaye a bayan sa kamar mayunwacin zakin da ya shekara be ce
ba.
***Assalamu alaikum sisters, masu korafi naga wasu daga cikin
korafin ku, ina mai baku hakuri akan matsalolin da aka samu, dan gane da rashin
posting halin girma shekaran jiya da jiya, hakan ya faru ne sakamakon ciwon
hakorin da ya matsa min hade da zazzabi, wanda har ta kai ban iya samun duba
sakonni ba balle har na iya zaman rubutu
Duk cikin zafafa biyar
babu wadda a cikin mu take jin dadi a duk sanda batayi posting ba, Allah ne
shaida ana iyakar kokari wajen ganin Anyi abinda ya dace. Sai dai idan abu ya
sha kan mutum a ba yadda ya iya. Allah ya huci zuciyar duk wanda ransa ya baci
ta dalilin jira ko wani abu, ba da gangan bane wani lokacin kuma ajizanci ne na
dan Adam.
Allah ya rufa asiri ya sa mu gama lafiya
2/21/22, 08:16 - Buhainat: Halin Girma
39
*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇ðŸ¾_*
https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share
*_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇ðŸ¾_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb
*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇ðŸ¾_*
https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS
*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇ðŸ¾_*
https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw
****
"Capt... Yaron nan ya bata min rai, ya za'a yi ya zarge ni
haka?"
Sassauta fuskar sa yayi, ya dafa shi
"Karka damu yarinta ce."
"Naga alama, waye shi? Aina yake?"
"Bansan shi ba, abokin Habib ne I guess!"
"Amma ka barshi ya zage haka, naji ma kamar hausar shi bata
fita."
"Eh, born and raised a UK ne, dole zaka ji banbanci,
anyways ya wuce na masa fad'a kuma."
"Shikenan, yanzu menene next? Da ya kamata muyi?"
Daga kafada Moh yayi cikin halin ko in kula yace
"Babu komai for now, muna cigaba da addu'a."
"Bari na wuce, I'm sorry akan maganar missing files din
nan."
"Karka damu."
Da kallo ya bishi har ya fice daga wajen, ya daga waya ya kira
waya, sukayi magana sannan ya kashe. A kalla Mahfuz ya zama wani haske a
binciken sa, kowa da yanayi da tsarin aiikin sa, ya san aikin sa sosai ya kuma
masifar burgeshi, he's smart and intelligent daga ganin shi,kuma da yake akwai
banbancin yadda k'asar mu take da tasu sun fi mu skills da kayan aiki.
 Shugaban su ya kira, ya fad'a masa abinda ake ciki, ya
kuma tabbatar masa da zasu yi duk yadda zasuyi, a yanzu za'a binciki layin
mudassir din a nan za'a gane da wadanda yake waya, yana ajiye wayar ya kira
Ammi sukayi magana sannan ya kira Aji da yake ta avoiding kiran sa tun ranar,
yana dagawa kuwa ya haushi da fad'a akan kin daga wayar sa da yayi, hakuri ya
bashi kawai sukayi magana ya kashe.
 Bayan kamar awa daya aka kirashi, ya shirya a gurguje ya
fita cikin tawagar yaran matasan sojoji, kowanne a cikin su a kalla zaka gane
babu sauki a tattare dashi, bakin glass ne a fuskar Moh, baka ko ganin kwayar
idon sa. A wani waje suka hadu, ya tarar da taron jami'an tsaro birjik kowannen
su cikin shiri, babu kalar da babu na jami'an tsaro tun daga kan police, DSS,
civil defense, uwa uba sojoji. Gaisuwa ya dinga amsawa daga kananan ma'aikata
har ya karasa wajen manyan da suke kasan wata rumfa suna magana. Details din
bayanan da aka samu ta wayar Musaddik din suke dubawa, in da ya nuna babu wata
waya da yake yi illa da mutum uku, Moh din sai wata number da take kiran sa
kullum a private number sai kuma Samha Bello Turaki, da Kamal Abubakar
Santuraki
  Kansa ne yayi masifar daurewa, menene alakar
Samha a cikin case din? Karba yayi ya sake dubawa sosai ya tabbatar da abinda
yake a rubuce. Yasan Laila ce take son shi ba Samha da take kawarta ba,menene
akalar Samha da Iman dinsa da har za'a hada kai da ita a sace ta?be san dalili
ba, abu daya ya yarda dashi, dukkan su anyi amfani dasu ne, domin a samu
galaba akan sa, su kuma idon su ya rufe, suna son ganin bayan din suka
fadawa gadar zaran JABIR!
"Mun gabatar da duk binciken da zamuyi akan shi, mun kuma
tabbatar da ba Musaddik bane, yayi amfani da fuska ne, sannan yayi amfani da
wata na'ura da take kwafar murya, wadda take da masifar tsada Kuma alamu sun
nuna ya jima tare da kai, ba zaka taba ganewa ba idan har ba sani kayi ba,
Musaddik yana da kusanci da kai shiyasa har sukayi amfani dashi wajen samun
kanka, da weakness dinka, sai kuma dan uwanka Kamal da suka taimaka musu
don cimma tasu bukatar da hadin guiwar Samha da bamu san wata alaka dake
tsakanin ku ba."
"Layin da yake private mun saka an bud'e mana shi,
kuma mun tabbatar da ana kira da layin ne daga wani bangare ma dajin falgore!
"
"Yana ina yanzu? "
" Yana ciki, idan an gama shiryawa shine zai shige gaba,
kaine team captain din da zai jagoranci tafiyar daga bangaren mu. "
" Ok sir! "
Yace yana sara masa, wucewa yayi zuwa in da aka ajiye fake
Musaddik din, yana so ya tantance banbance banbancen dake tsakanin sa da
Musaddik dinsa da ya kasa ganewa, yana durkushe a k'asa bayan dukan da ya sha,
ya tabbata dai da JABIR ya tantance shi sosai kafin ya kawo shi, dan hatta
tsawo da yanayin sa irin ma Musaddik din ne, fuskar sa ya dago, ya kare masa
kallo zuciyar sa na tafarfasa, kamar zai daure amma sai ya k'asa, ya dunkule
hannu ya naushe shi a baki, nan da nan kuwa sai jini, ya saka kafa ya hambare
shi. fitowa yayi ya tsaya a filin yayi bayanin yadda zasu yi idan sun isa, duk
suka amsa suka shiga motocin su a gurguje suka dauki hanyar dajin falgore.
  Gudu suke kamar zasu tashi sama, haka suke a duk
sanda suka fita operation amma kuma na yau yasha banban da sauran operation da
suka taba zuwa, yau abun nasu ne, su aka taba kai tsaye shiyasa kowa yake ji kaamar
abin ya shafe shi sosai, cikin kankanin lokaci suka isa saboda masifar gudun da
suke, barbazuwa sukayi a dajin kamar yadda yake according to plan. A daidai
lokacin Dr da zai kawo maganin ya iso, tana kwance kamar kullum ta gama
galabaita sosai ya shigo rataye da jakar sa, tana ganin sa ta mike da sauri,
bata ma san tana da ragowar karfin nan ba sai data ganshi, ya ajiye jakar ya
ciro magungunan a ajiye su, sannan ya koma gefe ya tsaya yana jiran shigowar
ogan, jim kadan sai gashi ya shigo, ya duba magungunan yayi masa bayanin yadda
za'a sha.
"Tashi!" Ya daka mata tsawa yana tamke fuska
"Dan Allah kayi hakuri, dan Allah."
"Wallahi sai kin sha."
"Dan Allah kayi hakuri." Ummimi tace tana kuka
"Shut up munafuka, idan na sake jin bakin ki sai na sheke
ki har sai kin daina numfashi. "
Gefe ta koma jikin ta yana ta rawa, bindiga ya ciro ya nuna Iman
dashi
"Karbi kisha kafin na harbe ki. "
Hannu ta miko ya zuba mata, ya kafe ta da jajayen idon sa, yana
nuna ta da bindigar, ta sha sannan ya juya yana murmushin mugunta ya fice
likitan yabi bayan sa. Dakin da ya ajiye Musaddik da driver ya shiga, ya tarar
da Musaddik din a kwance amma kuma sallah yake daga haka, kwafa yayi ya fito
bayan ya rufe kofar, yazo wajen yaran nasa da suka cika harabar wajen dauke da
manyan bindigu cikin shirin ko ta kwana.
"Zan shiga na kwanta, ku kula sosai bana so a samu
matsala."
"An gama Oga."
 Suka hada baki wajen fad'a, ciki ya shiga su kuma suka
cigaba da tsaiwa a wajen.
 Zagaye gaba daya dajin sukayi, kowa ya kama stand dinsa,
Moh da sauran zaratan sojojin suka kutsa kai ciki, sai da suka dan shiga sosai
sannan suka hango bukkokin dake wajen, wanda suka tabbatar da nan suke. Sake
rarrabuwa sukayi waje waje, suka sake zagaye bukkukin.
 Sai da suka gama shiryawa tsaf, sannan Moh ya basu
signal na su yi attacking dinsu, nan fad'a musu ta sama ta ka, nan suka rikice
suka shiga kokarin maida martani, sai dai yawan Jami'an tsaron ya ninninka
yawan su,. Cikin baccin da ya soma dauke shi yaji alamun yamutsewar wajen,
kafin ya kai ga mikewa aka bugo kofar dakin aka shigo, Moh ne a gaba yaran sa
na take masa baya, dukkansu a shirye suke su bada rayuwar sa dan ceto Madam din
Oga. Kasancewar be shiryawa zuwan su ba, sai ya zama kamar sun ci galaaba akansa
ne, babu bindiga ba babu komai a hannun Moh, ya matse shi a jikin bango ya
shiga bugun sa, bugu ba na wasa ba, sai da yayi masa laga-laga ya sake shi
cikin jini ya fadi kasa, ya bi ya take kansa da kafarsa cikin tsananin bacin
rai ya soma magana.
"Kafin kaga karshe na, ni zan ga karshen ka da duk wanda ya
goya maka baya..."
" Oga an samu Madam, she's bleeding so badly." Da
sauri ya juya yabi bayan dan sanda da ya shigo, ya bar yaran nasa da JABIR.
 Jini ne sosai yake zuba, da sauri ya karasa gabanta,
idon ta da yake kokarin rufewa da kalle shi. Rawa jikin sa yake ya tallafota
jikin sa
" Bude idon ki, dan Allah ki bud'e idon ke, me sukayi miki?
Me sukayi miki?"
Karasa rufewa idon sukayi ruf, ya dagata ya fita da ita jikin sa
na rawa, idan har wani abu ya same ta, sai ya karar da dangin JABIR kaf.
_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*
*_NANA HAFSAT(MISS XOXO) s_*
_SO DA ZUCIYA_
*_SAFIYYA HUGUMA_*
_DABI'AR ZUCIYA_
*_MAMUH GEE_*
_DEEN MARSHALL_
*_HAFSAT RANO_*
_HALIN GIRMA_
*_BILLYN ABDULL_*
_TAKUN SAKA_
*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇
D'aya 300
Biyu 400
Uku 500
Hudu 700
Biyar 1k
*_Zaku tura kudin a_*
6019473875
*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*
*keystone bank*
*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇
08184017082
*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇
09134848107
2/24/22, 08:05 - Buhainat: Halin Girma
40
*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇ðŸ¾_*
https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share
*_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇ðŸ¾_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb
*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇ðŸ¾_*
https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS
*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇ðŸ¾_*
https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw
****Wasu daga cikin sojin ne suka bi bayan sa, in da sauran
jami'an tsaron suka cigaba da dudduba bukokin har suka samu nasarar ganin
Musaddik da driver a wani daki, sai makamai masu yawan gaske suma daki gida,
dukkan su suna bukatar taimakon gaggawa musamman Musaddik da yake cikin
mawuyacin hali.
  Karar harbi suka ji, daga baya wanda basu san
dalilin harbin ba, a zaton su sun kama duk yaran JABIR din, da shi kansa JABIR
din bayan dukan da Moh yayi masa. Zagayawa baya sukayi, suka ga mutum a kwance
cikin jini, bashi da alamun yana tare da sauran yan iskan amma kuma basu san me
ya kawo shi wajen ba.
"Mu taimaka masa."
"Waye ya harbe shi?"
"Akwai sauran yan iskan a baya, let's check, ku dauke shi
ku tafi dashi zamu biyo bayanki. "
" Ok. "
Suka ce suka taimaka masa, da k'yar yake numfashi saboda tsabar
wahala, a motar da aka saka Musaddik suka saka shi, suka bi bayan motar da Moh
suke ciki dan basu taimakon gaggawa. Rik'e yake da hannun ta yana kuka wiwi
kukan da ya kasa dauriyar rik'e shi, gani yake kamar motar bata sauri
duk kuwa da irin gudun da suke tsulawa, idan har wani abu ya same ta, ba zai
bar kowa ba wannan alkawarin sa ne.
 Sanda suke karaso asibitin tuni iyayen gulma yan jarida
sun iso domin samun na watsawa, kofar baya suka koma suka bi, suka shiga
asibitin dan a yanayin da take ciki ba zai yarda wasu yan iska su dauke ta a
hoto su yada wa duniya ba, duk ma wata gidan jarida ko talabijin da tayi
gangancin haka sai ya yi shari'a dasu.
  Da sauri nurses din suka karbeta, daidai lokacin
da Babban likita ya karaso cikin tawagar sauran manyan likitoci mata da maza,
aka shiga da ita ciki domin bata taimakon gaggawa.
  Zagaye ya soma yi a wajen cikin yanayi na fitar
hayyaci, wayar sa da take ta faman nemam agaji ya gaza fitowa da ita balle ya
iya amsa kiran da ake ta faman doka masa da ba zai wuce daga makusantan sa ba,
bashi da sukunin ciro wayar balle ma ya amsa ta, balle ya iya wata magana ba
tare da yasan halin da Iman din sa take ciki ba.
   Cikin kankanin lokaci asibitin ya cika da
manyan mutane daga masarauta da kuma gidan gwamnati, Takawa ne ya karaso a
karshe ya samu shiga wajen da Moh din yake shi kadai sai wasu sojoji daga gefe,
sauran mutane suna ta dayan bangaren in da aka kai Musaddik da saurayin da aka
harba wanda yake cikin yanayi mara dadi.
  Yana ganin Takawa yayi saurin isa gareshi, sai
kuma ya ja ya tsaya a gabansa ba, hannun sa ya kama, ya ji yadda hannun yake
rawa sosai kamar wanda yake jin masifaffen sanyi.
"Kayi addu'a muhammad, babu abinda zai faru kaji?"
Da ka ya iya amsa masa, sai a sannan ya ga su Abba, ya matsa ya
gaishe su, dukkanin su suna cikin tashin hankali, Abba kamar bashi ba saboda
tashin hankali, sun riga Takawa zuwa wajen amma ba'a barsu sun shigo ba saboda
tsoron da yake wajen sai da Takawa yazo sannan suka samu shigowa. Sunyi waya da
Maman Iman din tun dazu ya kuma san zuwa yanzu sun karaso amma ba lallai su
shigo kai tsaye ba, sai ya dubi Muhammad yace
"Mahaifiyar ta suna waje, nasan ba za'a barsu su shigo
ba."
"Bari naje." Ya fad'a yana yin gaba, daya daga cikin
sojan ya bishi suka tafi tare, daga chan baya ya hango su a tsaye suna magana
da wani Soja da yaki fafur barin su, su shiga wajen, ganin Moha da kansa ya
nufo wajen ya saka sojan sake kallon matan.
"Alhamdulillah." Mamma tace tana share hawayen ta
Bud'e musu sojan nan yayi tun ma kafin ya karaso, dan yayi masa
alamar ya barsu, suka shigo suka sameshi, ya gaishe su, sannan suka tambaye shi
Iman din, Alhamdulillah kawai yace suka bishi zuwa ciki duk jikin su ya kara
sanyi sosai da lamarin.
  Be barsu sun karasa wajen da su Takawa suke ba
kasancewar duk maza ne, sai yasa aka kawo musu kujera suka zauna shi kuma ya
karasa ciki.
  An dauki tsawon lokaci kafin likita guda daya ta
fito, har zata wuce sai ta ga Takawa, da sauri ta je ta durkusa ta gaishe shi,
sannan tace suna kokarin su in sha Allah babu matsala, sannan ta je ta dauko
abu ta dawo ta koma ciki.
   Sun iya iyakar kokarin da zasuyi wajen
ganin sun tsaida cikin amma kuma hakan be yiwu ba,saboda karfin maganin da aka
bata ba zai bar cikin ba, Allah yaso babu wani illa da yayi mata bayan fitar da
cikin. Wankin ciki suka hada sukayi mata sannan aka saka mata drip saboda ta
rasa ruwa sosai a jikinta tsawon kwanaki tana amai sannan babu abincin da take
ci. Numfashin da take fitar wa ne kadai zai baka tabbacin tana da rai bayan
haka babu wani abu na jikinta da yake motsi, tayi fayau kamar ba ita ba, sai
uban fari da tayi kamar babu wadataccen jini a jikinta.
  Tura ta akayi zuwa dakin da aka kwantar da ita,
sannan Drs din suka fito wajen da su Takawa suke, suka kwashi gaisuwa sannan
sukayi bayanin yadda al'amarin ya kasancewa pills din da aka bata ne yayi karbi
sosai, jiri ne ya kwashi Muhammad yayi kamar zai fadi wani bafade yayi saurin
taro shi, ya rik'e shi jikin sa. Hakuri kowa na wajen ya dinga bashi, kafin a
bada damar a shiga a ganta, Takawa ne ya fara shiga sannan su Abba suka shiga
tare dasu Mummy, sannan suka fito aka bar Muhammad din ya shiga. Tunda ya shigo
ya hangi yadda take fitar da numfashi a wahalce, jikin sa ya kara sanyi sosai,
shine duk ya jawo mata wannan matsalar tana zaman zaman ta. A da ya dauka
matsalar sa kawai gidansu ne, shiyasa gaba daya ya taso da tsanar mulki tun
bayan da yaga abinda ya faru da Baban su Laila lokacin bashi da wani girma
sosai amma hakan be bar kwakwalwar sa ba, ya taso da tsanar mulkin da ganin
cewa duk wata masifa tana cikin gidan sarauta.
  Sunyi aiki tare da JABIR zai iya kiransa da
abokin sa mafi kusanci dashi a wanchan lokacin, bashi da hannu a matsalar da
JABIR din ya samu daga sama har aka sallame shi aka kuma karawa Moh din matsayi
irjn wanda ya Jabir din ne ya chanchanta, bayan nan duk wata alaka tasu ta
yanke, har ya manta dashi sai lokaci zuwa lokaci yake tunashi,be taba saka wani
abu a ransa game dashi ba, rayuwar sa yake kansa tsaye ba tare da sanin akwai
babban makiyinsa da yake burin ganin bayan sa ba.
  Maganar Takawa ce ta fado masa wadda yayi masa
ita dazu kafin ya bar asibitin
_"Ka sani bawa baya taba wuce ko ketare kaddarar sa, dan
haka ka dauka wannan din kaddarar ka ce kayi addu'a Allah ya baka ikon cinyeta.
Sanin kanka ne mutum be isa ya hana ko dakatar da kaddarar ka ba, kafi kowa
sanin yaran da suke tare da kai suna tsaron ka gida da mota ba wai na matsayin
da kake dashi bane a aikin ka, alfarma tace ya saka aka baka su har haka, wanda
duk munyi hakan ne saboda mu baka kariya a gida da waje, sai dai yanzu na kara
tabbatar wa babu dan adam din da ya isa ya tsare ka face Allah, kuma duk abinda
Allah ya kaddara zai faru toh fa sai ya faru ko da a gaban idon mutum
ne."_
  Gaban gadon ya ja ya tsaya cikin tsananin
tausayin ta, be taba kawo tunanin wani abu zai faru da su haka ba a dan
kankanin lokaci nan, ya zata shikenan ta rabu da duk wata matsala tun da suka
riga sukayi auren su, ashe ba haka bane. Hannun wanda babu drip a jiki ya
rik'e, ya zauna a gaban gadon yana karewa fuskar ta kallo, daga gani kasan ba
jin dadin baccin take ba, bacci ne me cike da wahala iri iri.
  Ya jima sosai a dakin, babu motsin komai, kamar
babu kowa aciki, knocking akayi, ya cire kansa da k'yar ya kalli kofar ba tare
da yayi magana ba, sai da aka sake kwankwasawa sannan yace
" Bismillah. " Turo kofar akayi, Zeenat da Habib ne a
gaba sai Mam, sai sauran jama'ar gidan da sai yanzu suka samu damar shigowa
wajen, tashi yayi daga zaunen, ya mikawa Habib hannu suka gaisa, fuskar sa ta
dan daga alamun yayi kuka, ya mai jiki yayi masa sannan suka gaisa da sauran
matan, suka fita tare da Habib din waje,
"Ina Mahfuz?"
Yayi karfin halin tambayar sa dan yayi tunanin tare zasu zo. Dan
duban sa Habib din yayi kamar me tunani, sai kuma yace
"Ai tare aka fito dasu daga wajen da Iman din take."
Kallon rashin fahimta Moha yayi masa yace
"Ban gane ba?"
Kwalla ce ta zubowa Habib din yayi saurin sharewa yana daurewa
yace
"Dazu da safe ya fito daga gida akan zaizo ya same ka, nace
zan raka shi amma ya bari anjima yace zai gane ma ai, shikenan ya tafi, bansan
ya akayi ba, sai gashi shima an same shi a chan in da Iman din take."
Kafin ma ya karasa tuni Moh ya firgice, yasan an ce akwai mutum
uku bayan iman da Ummimi, daya an harbe shi ma aamma sam be kawo tunanin komai
ba, be ma kara tunawa ba saboda damuwar da ta danne shi, yana so dai yaje ya
tabbatar da Musaddik na cikin wadanda aka samo din amma sai yake ganin kamar
idan ya matsa daga wajen ta komai zai iya faruwa.
"Yana ina?"
"Yana chan emergency unit har yanzu bamu ji komai daga
garesu ba, su Abba dai suna chan?"
"Innalillah wa inna ilaihi rajiun, muje."
Sauri sauri ya dinga yi kamar zai tashi sama, idan wani abu ya
samu yaron fa? Ya zai da ransa wai? Ba'a barin kowa ya shiga wajen nasa saboda
yadda case din nasa ya zama very complicated case, bayan sun yi nasarar cire
bullets din amma sam jinin ya ki tsayawa, ana kara wani, wani yana fita, su
kansu abin ya basu tsoro ganin yadda yake zubar da jini, shiyasa suka hana kowa
shiga, su Abba da suka dawo wajen tun da suka samu labari jikin kowa ya gama
sarewa da al'amarin Mahfuz din.
  Moh na isa wajen dr na fitowa daga ciki, jikin sa
babu kuzari ya nufo wajen da su Abban suke, ya kalle su daya bayan daya kafin
yace
" Sai dai muyi hakuri... "
Wani irin zubewa Moh yayi a wajen, kirjin sa na masa wani irin
suya, ashe Ajali ne ya kawo shi k'asar? Ashe dama shine sanadin mutuwar sa, me
yasa yayi masa wannna tsawar, me yasa ya ci masa mutunci bayan be san wani abu
dangane dashi ba,
"Nooo Dr... No be mutu ba, Dan Allah karka ce min ya mutu
dagaske, ban kyauta masa ba, be kamata ya mutu ba, he's innocent be kamata yayi
facing irin wannan mutuwar ba, me yayi? Menene nasa a ciki?"
"Get hold of yourself Capt, kullu nafsin za'ikatul ma'ut,
hakikaa kowacce rai sai ta dandani zafin mutuwa, shi da ya tafi be yi sauri ba,
mu kuma bamuyi jinkiri ba, addu'a kawai yake bukata."
Dr yace ya juya ya barsu a wajen, babu wanda ya iya motsi a
wajen saboda tsabar kaduwa, yaro me zumunci me shiga rai, me son yan uwan sa,
ya Yaya zataji? Labarin mutuwa irin wannan mara dadi, kullum korafin ta akan
Nigeria shine rashin tsaro, ko waya sukayi ta kan ce musu Nigeria ta zama
abinda ta zama, rai ba abakin komai yake ba. Kullum maganar ta kenan, tsoron ta
kenan, ashe bata tsira ba, Ashe zaman ta a chan bashi ne zai sauya kaddara ba?
Innalillah wa inna ilaihi rajiun kowa yake maimaitawa babu hargitsi ko hargowa,
saboda dauriya irin ta maza, sai dai kana kallon su zaka san mutuwar ta dake
su, musamman Habib da Moh, kafin kace kwabo labarin ya zagaye ko ina, kowa sai
da ya tausaya wa Mahfuz irin kaddarar da ta fad'a masa.
  Zuwan Aji da Bubu ne ya dawo da Moh cikin
hayyacin sa, babu hawaye ko digo a fuskar sa amma ya daku, ya kadu da zaka iya
rantsewa ya dade a kwance yana jinya me tsanani.
  Baya magana bayan amsa gaisuwa sai dai kawai ya
amsa maka da ka, har zuwa lokaci itama bata farka ba, yaje yaga Musaddik wanda
yake da sauki sai ciwuka a jikin sa yawanci na duka ne. Sai kuma yunwa da ta
ramar dashi sosai, driver da Ummimi babu abinda ya same su dama su ba sune
targets din ba.
  Wajen azahar ya dawo dakin da take, har lokacin
bata tashi ba, mummy ce kawai a dakin tana zaune gaban gadon da Iman din take,
idon ta yayi ja sosai, addu'a take tofa mata ya shigo ta tashi a kunyace tana
kokarin barin dakin
"Dan Allah mummy ki yi zaman ki, dama nazo na duba ko ta
farka ne, zanje station din na dawo."
Komawa tayi ta zauna shi kuma ya fita, ya shiga mota ya nufi
station din. Direct office din CP ya wuce ya samu DSP yana press conference
akan case din, kokarin fita yayi amma babu dama sun riga sun ganshi, sukayi
masa cha kuwa kowa na son masa tambayoyi, be basu dama ba dan yanzu ba wannan
ne a gaban sa ba, da kansa zai shirya ya basu lokaci amma ba yanxu da be ma san
me yake masa dadi ba sam. Hakuri aka basu, aka kuma sallame su sannan ya samu
ganin CP din sukayi magana, ya kuma shiga wajen da aka ajiye Jabir din. Yayi
matukar laushi sosai saboda ba karamin duka sojajin nan sukayi masa ba, dama
yasan ba zasu kyale shi ba, hakan ba dan dai basaso a samu matsala ne amma tsaf
zasu iya kashe shi a wajen.
  Baya jin a yanzu akwai wata halitta da ya tsana
sama da Jabir din, shiyasa ya tsaya daga kofar be shiga ba, dan idan ya shiga
zai iya shake shi har sai ya daina numfashi. Wani dan sanda ne a gaban sa rik'e
da wani katon katako, yana masa tambayoyi, sai kuma wasu yan sandan suma daban
daga gefe cikin fushi suke interrogating dinsa yana rokon suyi hakuri. Juyawa
yayi ya bar wajen ya koma suka karasa magana da CP sannan ya bar station din ya
dawo asinine, in da ya wuce kai tsaye wajen Musaddik, ya samu dakin da yan
sanda suna daukar bayanai daga wajen sa, wucewa yayi ya koma bangaren Mahfuz da
har yanzu ba'a saki gawar sa ba, sai an gama bincike tsaf sannan za'a basu suyi
masa sutura. A chan ya zauna tare da su Habib dasu Abba har bayan Magriba
sannan aka basu gawar tasa, suka dauke ta suka nufi gida da ita don yi masa
sutura a mika shi gidan sa na gaskiya.
  Zuwan su ya saka gidan rikicewa, dama kowa ya iso
ana zaman jira cike da alhini, ba karamin taba kowa mutuwar tayi ba, nauyi da
kunya ya Moh shiga ciki, sai yake ganin kamar shi ya jawo, da be saka shi a
cikin maganar ba, da duk hakan bata faru ba, a daren aka hada shi, aka kuma
rakashi gidan sa na gaskiya. Allah sarki.
Mutuwa darasi ce babba, Rayuwa bata da tabbas, Allah ya bamu
ikon amfani da lokacin mu kafin ya kure mana,Allah kasa mu cika da imani. Amin
ðŸ˜
 Â
Â
***Wani irin juyawa cikin Samha yayi lokacin ta samu labarin an
kama Jabir, tsoron ta daya kar sunan ta ya shigo ciki, itace ta bawa Jay din
shawarar kidnapping Iman din, kuma ita kadai ce tasan plan dinsa duk da itama
bata san amfani yayi da ita ba. Wayar ta ce tayi kara da take gefen ta,dan
tsorata tayi, sai kuma ta kai hannu ta dauka tana kallon number, Kamal ne yake
kiranta, dagawa tayi ta saka wayar a handsfree
"Ashe dama abinda zaku aikata kenan ke da dan iskan chan
shine kuka shigo dani ciki kuka samu duk wani bayani akan shi, daga karshe kuka
watsar dani."
"Ai kai ba karamin kidahumi bane, idan banda gara irin ka,
waye yake da amana a wannan zamanin, kowa kansa ya sani bari kaji, dan haka
karka dameni ka kyale ni naji da abinda yake damuna."
"Ai wallahi kadan kika gani, asirin ki ya gama tonuwa dan
na gama zayyane komai a gaban yan sanda, abubuwan da kuka sakani nayi duk na
fad'a sai ki jira hukunci, wallahi ko shi MOH ya kyale ki wallahi ni ba zan
kyaleli ba kinji na rantse!"
Kit ta kashe wayar ta jefar da ita,
"Wannan wacce irin masifa ce?"
Da sauri ta ja jakarta ta fito, bata tarar da maman ta a falo ba
dan haka tayi saurin ficewa ta dauki mota ta bar gidan, tana tafe tana gwada
kiran Laila amma bata dagawa, ta rasa abinda yake mata dadi, sai kawai ta wuce
gidan ta sameta suyi magana ko zata taimaka mata, amma tana zuwa gate sai aka
hanata shiga, tayi mamaki sosai hadda fitowa tayi musu bayanin kanta, amma
kemaimai suka hanata bayan sun tabbatar mata da sun gane ta, umarni ne aka basu
kar su sake barin ta, ta shiga masarautar.
Post a Comment for "HALIN GIRMA 36-40"