Skip to content Skip to sidebar Skip to footer

HALIN GIRMA 31-35


 31

 Â    ×××Ya fada a can 'kasan zuciya yana yamutsa fuskar sa. Yanayin yadda ya yamutsa fuskar tasa ne hakan yasa Zaraah sake matse tata fuskar. Ta wulkita idanu ta dankara masa harara. Hade da kokarin bude murfin motar cikin fushi da takaicin sa.

 

Ledar ya dora mata akan cinya. Tare da sake rufe murfin motar .

 

"Budemun. "Ta fada a hankali.

 

Hade da kaudar da fuskar ta zuwa kan murfin motar. Don sam batason kallon fuskar Maheer. Domin tamkar sudeis yayi kaki ya tofar. Saboda tsananin kamar da suke.

 

"Tsiwar ki ta bude miki" Ya fada cikin muryar umarni . Ya kuma bata rai don karta dauka da wasa yake.

 

‘Kunkuni ta fara yi ahankali . Maheer ya saki siririn tsaki,

 

“Dauka ledan ki fita. Kuma this should be the very last time da zaki tsallake dokata kinji na gaya miki.�

 

Ya karasa ransa a matukar bace . Cikin zuciyar sa na masa zugi.

 

“Toh ina ruwanka da rayuwata.�

 

“Ni kike gayawa haka?� Yana kokarin jefa mata wani kallo mai dauke da kalamai.

 

“Ni dai ka budemun na fita…�

Ta karasa fada tamkar zatayi kuka.

 

. Hade da sake kiciniyar bude murfin motar. Hannun sa d’aya ya dora akan nata da zummar hanata kokarin fitar da take.

 

Wani Irin electric shock ne ya ziyarce ilahirin jikin su da kwakwalen su. Da sauri ya janye itama ta dauke nata hannun.

 

“Dauki kayan ki fita . Kuma su zaki dinga amfani dasu wajen fita unguwa da sauran su. Kar ki kuskura ki kawo wani abun a zuciar ki. Amanar da dan uwana ya bani nake zartarwa.� Ya karasa hade da jan kasan leben sa ahankali .

 

Lock din ya cire, Ta fice da sauri har tana tuntube. Ya sauke zuciya kawai hade da girgiza kai. Ya ja motar zuwa bangaren sa.

 

Ya sha mamaki kwarai matuka wajen ganin masu aikin gidah nata rushe rushen bangaren nasa ana sake kawata shi.

 

Zai yi magana kenan sai ga fitowar Addayo daga ciki. Fuskar ta kumshe da murmushi. Gayar da ita Maheer yayi ya na mata kallon karin bayani game da gyaren bangaren nasa.

 

“Addayo�

 

“Na’am na ikko dan albarka. Kaga bangaren ka ya fara sauyawa ko?�

 

Ya daga kai alamar eh hade da susar keyar sa.

 

“Toh me zaa jira, Aure an rigada an daura, Sai tariya kadai ta rage. Ina ita kishiyar tawa ne.�

 

“Ta shiga sashen su.�

 

“Yauwa inason ganin ku an jima da yardar Allah.�

 

“Tohm Addayo! Saukar yaushe?�

 

“Tun dazu fa nazo. Dan na tsaya gidan Harisu ne.�

 

“Okay Masha Allahu.�

 

“Allah ya maka albarka, Allah ya jikan mahaifan ku da dan uwanka.�

Ta karasa fada tana mai goge hawayen dake tsiyaya a idanunta

 

 

“Aaamen Addayo� Ya bata amsa yana runtse idanun sa.

 

“Muje bangare na nan aka mayar maka da kayan ka kafin a kammala nan din.�

 

“Toh Addayo.�

 

Tana gaba da yar sandar da take dogarawa, Shi kuma Maheer yana biye da ita a baya yana tunanin yadda zasu kwashe da Zaraah idan suka tare. Dubada ganin su duka biyun ba kaunar junan su suke ba. Gwara gwara ma shi yakan ‘daga mata kafa awasu abubuwan saboda amanar ta da Sudeis ya bashi.

 

••â€?.     ••â€?.     

 

   Tana shigewa parlorn nasu bakinta dauke da sallama ta ajiye ledar hannunta akan kujera. Hadi da kwaye hijabin dake jikin ta, Ta ajiye a kusa da ita.

 

Dadaa dake daki tafito tana jijjiga baby sudeis daya tashi a bacci.

 

“Dadaa barka da yammaci.�

 

“Barkan mu..�

 

“Love of my life� Zo nan.� Ta karbu baby sudeis a hannun ta tana kallon sa. Har cikin bargon jikinta take kaunar baby Sudeis. Idan ta dauke shi ji take nutsuwa da kwanciyar hankali ta dabaibayeta.

 

Dadaa na hankalce da ita, Ta zauna akan kujera hade da janyo ledar da Zaraah ta ajiye.

 

“Wannan kayan fa?�

 

“Yaya Maheer ne ya sayo�

 

“Na waye?� Dadaa ta tanbayeta tana dudduba hijaban da su safa hadi da sabuwar wayar.

 

“Wai nawa ne� ta karasa cikin kasa da murya.

 

“Yauwa zo ki zauna anan Zaraah. Ki bani hankalin ki da nutsuwar ki. Abunda zan gaya miki abune mai muhimmanci a rayuwar ki. Kinga saura kwanaki kalilan ku fara jarabawar kare makaranta ko? Dan haka inaso kafin lokacin ki samu nutsuwa ki kuma sa aranki hukuncin da aka zartar akan ki shine mafificin alkhairi agare ki.�

 

“Tohm Dadaa. � Ta fada, Hadi da zama a gefen kujera . Tuni hawaye suka shiga reto a idanun ta.

 

“Allah yasa ba laifi nayi ba Dadaa da aka yankemun hukunci�

 

“Aa wallahi ko d’aya! Hasalima nina bada hadin kai wajen yanke hukuncin. Illa dai kiyi hak’uri na rashin neman yarjewar ki da bamu yi ba.  Kina sauraro ko?â€?

 

“Toh Dadaa. Ina ji�

 

“Ba wani abu bane fyace daurin auren ku da akayi da Maheer. Maheer dai yayan Sudeis marigayi…�

 

Dadaa na karasa fada, Maheer ya doka sallama ya shiga parlorn. Don sanarwa Zaraahn nema su da Addayo take�

 

Zaraah ta daga idanunta da suke zama tamkar garwashi saboda tsananin yadda suka rine sukayi ja. Ta sauke akan Maheer. Hawaye d’aya na bin d’aya suka shiga kwarara a fuskar ta.

 

 

Unedited

Sorry for the late post

Thank you ❤️❤️

 

 

 

*_WAIWAYE......ADON TAFIYA inji masu salon iya magana_*

 

*ZAFAFANKU BIYAR 🔥🔥🔥🔥sune suka sake dawo muku da wasu nau'in QAWATATTU kuma TSARARRUN LABARAN,masu dauke da SABBIN JIGO na MABANBANTAN LABARAI masu tsuma ZUCIYA*

 

*_SANIN HALI.....yafi sanin kama,indai kasan TAFIYAR ZAFAFA babu dana sani ko nadama cikin zuba kudi wajen siyan litattafansu,koda jin sunan ma kasan cewa tafiyar ta dabance_*

 

*GWADA IDAN BAKI TABA BA!!!,HAUSAWA SUKACE SAI AN GWADA AKAN SAN NA ƘWARAI,burinmu kowa ya shigo cikin tafiyar a dama dashi*

 

*JERIN SABABBIN LITATTAFAN NASU NA WANNAN KARON SUNE*

 

*_DEEN MARSHALL👉🏾 Mamuhghee_*

 

*_HALIN GIRMA👉🏾hafsat rano_*

 

*_TAKUN SAƘA👉🏾billyn abdul_*

 

*_SO DA ZUCIYA👉🏾miss xoxo_*

 

*_ƊABI'AR ZUCIYA👉🏾huguma_*

 

*DUKKAN WADAN NAN LITATTAFAN ÆŠAI ÆŠAI HAR BIYAR...ZAKU SAMESU AKAN KUDI NAIRA 1K KACAL*

 

2👉🏾400

3👉🏾500

4👉🏾700

5👉🏾1000

 

*Zaku saka kudinku ta wannan asusun bankin*

6019473875

MUSAA ABDULLAHI SAFIYA

keystone bank

 

Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number

 

08184017082

 

*IDAN KATIN WAYA NE KO VTU,SAIKU TURA ZUWA GA WANNAN NUMBER TARE DA SHAIDAR BIYANKU*

 

09134848107

 

*_HAR KULLUM MUNA MARABA DA ALFAHARI DA MASOYANMU_*🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽

#team zafafa biyar

 

 

XOXOWRITES🤩

2/9/22, 20:30 - Buhainat: Halin Girma

      31

 

*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_*

https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share

 

*_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_*

https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb

 

*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_*

https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS

 

*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_*

https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw

 

******* �

 

Lokacin da suka isa Abuja dare yayi dan basu suka bar Yola ba sai wajen karfe takwas na dare, sun dan samu delay ne shiyasa, direct Hotel suka nufa ta dinga masa magiya akan ya kaita gida amma fafur yaki, yayi mata kunnen uwar shegu har suka huta bata bar mitar ba, yi yayi kamar be ji ta ba, shima akwai gidan Bubu da suke sauka duk sanda suka zo ko shi yazo kawai akwai dalilin sa na zuwa nan din. Waya taga yana ta faman yi, da mutane daban daban duk akan maganar zuwan nasu, sai da ya gama tas wajen takwas da rabi sannan ya tashi ya nufi kofa ya bud'e, ya karbi sakon ya rufe ya dawo yana ajiye ledar a saman makeken gadon hotel din.

 

"Tashi ki shirya akwai dinner da Chief of Army Staff, da sauran manyan soldiers na k'asa, a madadin wanchan event din kawai aka hada wannan dinner din kowa da family nasa."

 

" Owk." Tace tana mikawa, ya nuna maya ledar da hannu yana shigewa toilet. Daukar ledar tayi me dauke da tambarin wani babban Mall, ta bud'e doguwar riga Abaya ta gani me kyau, ciro ta tayi tana ware ta, sosai tayi mata kyau ta ajiye a gefe ta ciro sauran tarkacen kayan hadda wata kar karamar jaka da tafi kama da purse sai takalmi hills amma ba chan ba. Shiryawa ta hau yi tana yi tana kallon toilet din har ta gama be fito, ta matsa wajen yar trolley dinsu da ciro perfumes ta faffesa sannan ta zauna tana dauko wayarta da take haske alamun kira ne ya shigo, Mamma ce, tasan cewa zatayi taji su shiru,ita kanta batayi tunanin nan din zasu zarto ba dan tasan an gama shiryar su kada ma Mamma taji labari tasan ba zata huta ba har sai sun iso. Dagawa tayi daidai lokacin da ya fito daga shi sai gajeren wando, faffadan kafadarsa ta kalla da take a mummurde, ta sauke kanta tana jin wani yanayi da bata san na menene ba, a gabanta ya tsaya yana rik'e k'ugu, yana, hannun sa daya rik'e da karamin towel, ganin ta dauke kai kamar bata ganshi ba, ya saka shi yarfa mata ruwan da yake hannun sa a fuska, yi tayi kamar zata tashi amma da daure ta cigaba da wayar, ta bawa Mamman hakuri yana ji ta gama ta ajiye wayar tana tashi da sauri.

 

"Kinyi kyau Matar Muhammad."

 

"Nagode." Tace a kunyace bubbude hannayen sa yayi, ya ja baya yana tattare fuskar sa.

 

"Shirya ni..."

 

"Na'am?"

 

"Eh ki shirya ni, ki shafa min mai ki saka min kaya..."

 

"Kamar dan baby?"

 

"Toh da mene? Ai babyn naki ne ni."

 

Dariya ta saka tana sake gyara zaman ta

 

"I'm serious fa, kinga we are running late, kar suyi ta jiranmu."

 

Ganin da gaske yake, ya sakata tashi ta dauko man, ta shiga shafa masa yana lullumshe ido, da gangan ya dinga sata komawa baya yana cewa be yi ba, nan fa. Da dai daga alamun so yake ayi tayi sai ta tattara man ta mayar, ta dauko masa suits din da ta gani tare da abayar ta, ta mika masa ya noke yana sake bararrajewa. Girgiza kai tayi, ta shiga saka masa, yana sake narke mata kamar wani karamin yaro a gaban mahaifiyar sa, sai data gama tas ya rage saura necktie sannan ya karba ya karasa sawa a gaban mirror, ya kalli kansa yana hango ta ta cikin mirror din,da hannu yayi mata alamar tazo, ta tako ta tsaya daga kuibin sa, ya matso da ita jikinsa yana kara kansa a jikin fuskar ta.

 

"Perfect!" Yace yana dariya, wayar sa dake kusa da wajen ya dauka, yayi musu hoto me kyau a gaban mirror din, sannan ya daga kiran da George yake masa.

 

"We are on our way."

 

Kawai yace ya katse kiran, ya rik'e hannun sa cikin nata suka fito, duk da suka hauro reception din suke shan kallo, tana jin shi yana jan tsaki k'asa-k'asa har suka shiga wajen da yake a cikin hotel din ne dalilln da ya saka ma suka sauka anan din kenan saboda already an riga anyi booking dakin tun kafin ranar ma. Duk in da suka wuce sojoji ne a tsaitsaye sun yi shirin ko ta kwana, cikin girmamawa suke gaida su, har suka kai babbar kofar shiga wajen.

  

    Wata iriyar kunya ce ta dabaibaye ta lokacin da suka shiga wajen, mutane ne masu yawa kai kace wani gagarumin biki ake, kowacce kofar shiga wajen dankare take da jami'an tsaro, ji tayi ido yayi mata yawa, gashi duk sun tashi da shigowar su. Mafiya yawancin su ba hausawa bane, sai yan daidaiku da tayi hangowa daga in da take. Wajen zaman su waitress dake tsaye a wajen ta nuna musu, basu wuce chan ba kai tsaye sai da suka je wajen manyan kusoshin, suka kwashi gaisuwa in da taga yayi wata irin gaisuwa tasu ta daban, sannan suka samu wajen zama suka zauna sai a lokacin ya sakar mata hannu.

 

"Sannu Amarya!"

 

Wata bahaushiya a kusa da ita tayi mata magana, amsawa tayi tana maida mata murnushin da tayi mata, sai kuma suka gaisa da sauran matan wasu hausawa wasu ba hausawa ba, kafin kuma a fara gabatar da abinda ya hada su.

  Captain Is'mail ne a gaba gaba akan komai shi da George, su ne ma organizers din event din shiyasa ko zama sun kasa yi, har sai da lokacin cin abinci yayi sannan suka zauna shima na wucin gado,ana gama ci aka cigaba da gudanar da event din. Sun sha kyaututtuka sosai har sai da Iman ta gaji da karba, idon ta yayi nauyi kwanciya take so kawai yayi, yana lura da ita, yasan ba karamin aikin su bane su kai fiye da biyu a wajen babu kuma wanda zai damu, ita kuwa akwai rashin sabo, tashi yayi yana zura hannunsa cikin aljihun wandon sa, ya nufi wajen da Is'mail yake ya jashi gefe, yayi masa magana kana ya dawo wajen zaman sa ya zauna. Sai da aka kara kamar mintuna ashirin sannan isma'il din ya bada sanarwar amarya bata jin dadi zata je ta huta, da haka suka samu suka sulale daga wajen suka nufi masaukin su. Dukkan su a gajiye suke dan haka babu abinda suka kara bayan sauya kayan jikin su sai bacci, cikin kankanin lokaci bacci yayi awon gaba dasu.

 

    Da wuri ta tashi, ta shirya ta zauna tana duba lokaci, baccin sa yake tsakanin sa da Allah tun bayan dawowar sa sallar asubah gashi ta matsu ta ganta a gidan, gashi babu alamun zai tashi har past 10, an kawo musu breakfast daga reception din taci kad'an ta ajiye masa sauran ta cigaba da zaman jiran sa. Wasa wasa lokaci ya dinga ja, babu abinda yake sai chanja kwanciya da juyi daga nan ya koma nan cikin jin dadin baccin. Ganin da gaske ba zai tashi ba, ya sakata zuwa daidai saitin kansa, ta dan rankwafa da niyyar tashin sa, hannu takai kan sajen fuskar sa, ta taba kadan, juyi taga yayi ya sake maida kansa dayan barin, sake durkusowa tayi ta bayan nasa ta kai hannun ta jikin sa, kam taji ya riko hannun ya makale shi tsakanin hannun sa da jikin sa, ja tayi taji ya makale shi kam, gashi sauran kad'an ta fado kansa gaba daya, dayan hannun ta saka ta taba shi,

 

"Please ka tashi zamu makara."

 

"Uhum..." Yace cikin muryar dake cike da nauyin bacci, ya sake kankame hannun nata a jikinsa wanda ta jawo mata fadawa kansa ta gefe daidai saitin bayan sa.

   Sun jima a haka tana jin shi yana fitar da numfashin bacci, kafin yayi motsi ya bud'e idon sa da suke cike da bacci sosai, ya juyo bangarenta yana sakin hannun nata.

 

"Ka tashi dan Allah."

 

"Um um..."

 

"Ka manta zamu fita?"

 

Da kai ya amsa mata da eh, kokarin tashi tayi zaune ya daddanne ta, ta hanyar dora kafarsa a jikin ta

 

"Kinsan fa jiya bamuyi wani bacci ba, please muyi bacci idan muka tashi sai mu fita."

 

"Past eleven fa, please please please."

 

"Ohhhh! Ni dai gaskiya, gaskiya bacci nake so nayi, anjima sai muje idan mun tashi, bari kiga."

 

Ya sake kadannade ta da kafafun nashi da sukayi mata nauyi ta kasa janye su,gani tayi yana maida idon sa zai rufe tayi saurin rik'e fuskar sa

 

"Dan Allah!"

 

"Shikenan." Yace yana sauke kafarsa, ta samu ta mike tana murmushi

 

"Amma da sharadi, ke zaki min wanka ki shirya ni, ki kuma bani abinci a baki."

 

"Ahhhh." Ta bud'e baki cike da mamaki

 

"Fine, bari na koma bacci na sanda na gama mun fita."

 

Da sauri ta rik'e blanket din da zai sake rufa

 

"Zanyi."

 

"Good girl."

 

  Yace yana mata murmushin mugunta. Janye blanket din tayi, ya zuro kafafun sa k'asa yana mika mata hannu, kama hannun tayi ya tashi, yayi kamar zai fadi ya fado jikin ta, nauyi sosai taji, amma ta daure dan taga take taken sa zai iya cewa ya fasa, a haka suka isa toilet din, ya zauna a gefen bathtub din ta hada ruwan, ta dauko masa brush da toothpaste ta matsa masa ta bashi, kin karba yayi ya bud'e mata bakin wai tayi masa, sake mika masa tayi ya noke yana tashi alamun zai bar toilet din, da sauri ta riko shi, ya koma ya zauna ta fara yi masa, dariya ce take kamashi amma ya kanne, yadda ta daddage kawai zai baka dariya, hannun sa ya dora a saman nata ya karbi brush din, ya karasa, ya bata ta cilla shi a dustbin din toilet din daga nan tayi hanyar fita

 

"Kina fita zan fito nima."

 

Tsayawa tayi ta dawo tana tura baki, ya hau cire kayan sa a gaban ta, tayi saurin juyar da kanta, murmushi yayi ya shiga ruwan da yayi masa daidai da yadda yake so, sai data tabbatar ya shiga ciki sannan ta juyo tana cigaba da dauke kanta ta dauko sponge da sabulu ta bud'e ta ajiye a dan wajen da aka tanada, zama tayi a gefen bathtub din,  taki kallon gefen sa ta juyar da kanta gaba daya hanya, bata yi aune ba taji ya jawo ta cikin ruwan, ta saki kara, ya hade bakin su waje daya ya hana karar tata tasiri.

 

   Sai da suka bata lokaci mai tsawo a ciki sannan suka fito, ta dinga turo baki tana jin kamar tayi masa kuka, ta riga ta gama shiryawa tsaf har kayan da ta saka dama su tayi niyyar sawa amma ya jawo sai ta sake sabon shiri, a wajen shiryawar ma haka tayi ta fama dashi da ya janye mata towel ta nan sai ya janye mata ta nan haka dai yayi tayi har sai data gama cika fam, zata fashe kafin ya kyaleta su shirya a nutse.

   Kasancewar ciki da falo ne dakin, sai tayi ficewar ta, ta barshi a ciki yana karasa shiryawa ta hada masa breakfast din ta ajiye da yazo ci kawai zai yi su tafi. Da waya a makale a kunnen sa ya fito, yayi zaman amsa wayar da ta fuskanci da Musaddik suke magana, sai da ya gama wayar tsaf sannan ya jawo abinci ya soma ci a yangace kamar ba jiran sa take ba, bata dai ce komai ba, ya gama duk bata lokacin da zai yi, sannan ya tashi yana goge bakin sa da tissue. Tashi tayi itama dama tayi ready har da jakarta a kusa da ita, gaba yayi ta bishi a baya, ya murda kofar sojan da yake jiran sa a wajen ya karbi Notepad da wayoyin sa, shi kuma ya zuba hannuwan sa a aljihu suka shiga takawa zuwa wajen da aka tanadar domin parking motoci.

   Bud'e mata kofa yayi, ta shiga ya rufe sannan shima aka bud'e masa nasa bangaren ya shiga suka fita daga harabar hotel din!

 

Bashin Jiya....so sorry banajin dadi ne

 

_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*

 

*_NANA HAFSAT(MISS XOXO) s_*

_SO DA ZUCIYA_

 

*_SAFIYYA HUGUMA_*

_DABI'AR ZUCIYA_

 

*_MAMUH GEE_*

_DEEN MARSHALL_

 

*_HAFSAT RANO_*

_HALIN GIRMA_

 

*_BILLYN ABDULL_*

_TAKUN SAKA_

 

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇

D'aya 300

Biyu 400

Uku 500

Hudu 700

Biyar 1k

 

*_Zaku tura kudin a_*

 

6019473875

*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*

*keystone bank*

 

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

 

08184017082

 

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

 

09134848107

2/12/22, 11:07 - Buhainat: Halin Girma

      32

 

*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_*

https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share

 

*_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_*

https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb

 

*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_*

https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS

 

*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_*

https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw

 

*******�

 

Address din drivern ya dinga bi har suka isa gidan, tun kafin motar ta gama daidatuwa a harabar gidan take kokarin fita, chapko ta yayi yana bata fuska

 

"I'm jealous!"

 

Da mamaki dake kallon sa

 

"Yes I'm jealous, I want my share of love too, inaso naga same action na murna anytime mukayi nisa da juna, inason soyayya, inaso a gatata ni, aji dani sannan a damu dani please."

 

Dariya ma ya bata, ya saki hannun ta yana sake bata fuska shi a lallai yayi fushi, girgiza kanta tayi cikin muryar lallashi tace

 

"I'm so sorry toh, kawai I'm eager ne, ban wani zauna dasu sosai ba, shiyasa kawai."

 

"Shikenan reason din?"

 

"Shikenan, ko baka so naga Mama ta? Kullum fa kai kana tare da Ammi fa, nifa?"

 

"Ba haka bane, banda Mummy ai nake nufi, Mamma, Amaani, Amaan and rest, su nake kishi dasu."

 

Dariya ta sake yi, ta rik'e kofar ta bud'e, ya zuba mata ido kamar bashi da niyyar fitowa, sai da tayi masa alamar da hannu sannan ya bud'e ya fito ta dayan side din, yana karewa gidan kallon.

   Kofar shiga part din suka nufa, yana biye da ita a baya hannun sa sakaye a cikin aljihun sa, daf da zasu kai kofar ta bud'e, Amaani ce a gaba da shegen gudu, tayi kanta tana ihun wallahi itace, kamar zata kada ita, sai da k'yar ya nutsu tana numfarfashi, hango shi da tayi a baya sai kawai tayi wajen sa , ta rik'e masa hannu ta fara zuba masa surutu kamar tayi shekara da sanin sa. Cike da sha'awa yake duban ta, ta rik'e shi gagam har ciki tana bashi labarin da be gane kan sa ba.

  Mamma ce ta fito daga wani corridor, tana sanye da lullubi akanta, fuskarta cike da farin cikin ganin su,

 

"Sannun ku da zuwa."

 

Tace sanda ta karaso falon, idon ta akan Iman dake zaune da Amaan a kusa da ita. Russunawa yayi cikin ladabi ya gaida Mamma din, a daidai lokacin Mummy ta fito itama, ya gaishe ta a kunyace dan kallo daya yayi mata yaga tsantsar kama da Fatin sa, amsawa tayi ita din ma a yanayin kunya irin tamu wadda aka gada tun iyaye da kakanni. Iman ce ta gaishe ta,  ta amsa daga tsaitsaye ta juya ciki, murmushi kawai Mamma tayi dan tasan yadda ta matsu da zuwan nasu, amma ba zata taba nunawa ba, yadda tayi zaka dauka ma bata damu ba sam,nan kuwa tsantsar kara ce irin tata da har take nema tayi yawa.

   Abinci aka shiga jere musu, yayi mata alama da ido akan tafiya zai, ya dauki bottle water guda daya ya mike yayi musu sallama akan zai dawo, mamma ce ta hau korafin me zai sa ba zai tsaya yaci abinci ba, hakuri ya bata akan zai dawo akwai wanda yake jiran sa ne. Shikenan tace ya fice ta harari Iman

 

"Haka ake wa miji? Tashi mana kije kiji."

 

Tashi tayi tana dariya, ta bi bayan sa ta same shi har ya kai wajen mota, tsayawa yayi ganin ta fito ya choge jikin motar sai data karaso sannan ya shiga, ya sauke glass din motar yana kallon ta

 

"Kwana zanyi ko?"

 

"Inji waye? Da yamma zan dawo zuwa magriba."

 

"Dan Allah..." Girgza mata kai yayi tun kafin ta karasa.

 

"Zaki dawo next time, sai na dawo bye."

 

Ya daga glass din ta dan ja baya tana kallon motar har ta fice daga gidan, kamar zatayi kuka haka taji, taja kafarta a hankali ta koma ciki ta samu Mamma ta zuba mata abincin mummy kuma ta dawo falon ta zauna tana wa Amaani fad'a akan rawar kanta.

   Taji dadin zuwan ta gidan sosai, kamar tayi ta zama haka taji, amma tasan tun da yace zai dawo toh zai dawo din, amma taso ya barta ko zuwa da safe ne sai yazo su tafi ko ya turo a dauke ta.

  Ta idar da sallar magriba kenan a dakin Mummy, Amaani ta shigo tace ya dawo, har ga Allah taji babu dadi, ta tashi ta nannade sallayar ta ajiye a gefe ta zauna a saman sofa tana ciro wayarta. Tana zaune har wajen minti talatin babu wanda yazo kiranta, har ta kishingida sai ga Mamma ta shigo, tace ta tashi su tafi yama fita,

 

"Na zata zai barni na kwana."

 

"Kul... Dududu yaushe akayi auren? Kar ma ki soma yi masa maganar kina ji na? Watarana da kanki zaki zo ma"

 

" Wuce muje kar suyi ta jira." Tace tana sakata a gaba suka fito falon, uban kaya ne jibge a gefen falon dangin su shinkafa kayan abinci dai masu yawa, Mummy na zaune tana juya kudi a hannun ta

 

" Kinga wahalar da yayi ko? Kiyi masa godiya nace ba za'a karba ba amma ya dage dole." Tayi maganar tana ajiye kudin a saman center table, bin kudin Iman tayi da ido wanda a kalla zasuyi hundred thousand, sai kayan abincin da yake a dankare awajen, jinjina kanta tayi cike da mamakin sa, ko alama be nuna mata ba balle ta gane shirin sa, dadi ne ya kamata ta fito bayan sun yi sallama da Mummy tana zuba masa ido ta cikin hasken compound din gidan, duk da motar tint ce, amma tana iya hango inuwar sa, cike da karsashi ta karasa wajen motar, dai-dai lokacin da kofar ta bud'e, ta shiga da sallama tana dagawa su Iman hannu.

   Suna fita daga gidan ya matso kusa da ita cikin lallashi yace

 

"I'm sorry na hanaki kwana, kinga gobe da wuri zamu tafi amma next time da kaina zan kawo ki har sai kin gaji."

 

"Laa ba komai fa, dama wasa nake yi, su Mamma ma ba zasu barni ba ai, wai dududu yaushe akayi auren?"

 

"Haka suka ce ko?"

 

"Eh..."

 

"Yawwa kin gani."

 

"Babu komai fa, ni nama manta ma ma na tambaya, I'm sorry."

 

Ta kama kunnenta, zare hannun nata yayi yana jawo ta jikinsa.

 

" Thanks dear."

 

****

Washegari suka dauki hanyar Kano, tun kafin su isa an gama gyara musu gidan su, dama dai ba wani baci yayi ba saboda akwai masu aiki da kula da gidan banda sojojin da suke waje suna gadi, suna isa ya fice tare da Musaddik, anan ta tarar da uban kayan lefen ta, tayi zaman kallon su cike da mamaki, idan kaya na yawa toh ita dai sun mata mugun yawa, ya zatayi dasu? Shine kuma har da siyan mata wasu kayan saboda dai ba'a san wahalar kudin ba. Gajiya tayi da kalla ta saka masu aikin suka kwashe su, suka maida su wani daki guda kafin ta kira Mamma taji abinda ya kamata tayi dasu da mutanen da ya kamata a bawa.

   Slippers ta zura ta zazzagaya gidan nata, wanda yasha kaya na alfarma, har da wani babban garden a baya da pool daga chan gefe shima, gidan yayi kyau amma yayi girma ace mutum daya kwal dan ma ma'aikata masu yawa wanda yawanci daga masarauta suke sai wanda aka turo su daga adamawa. Daki ta koma ta haye gado tayi kwanciyar ta dan bata jin yunwa tasha cornflakes suna zuwa sai kawai ta kwanta da niyyar ta tashi wajen azahar ta dafa masa simple dish dan wata gajiya take ji na nukurkusar ta.

   Ta jima batayi irin baccin da tayi ba, ga sanyin AC da kamshin fresheners masu dadin kamshi da ya cika dakin, hakan ya kara taimaka mata jin dadin baccin sosai har sai da taji ana mata knocking sannan ta tashi bakin ta dauke da addu'a ta yane kanta ta fito ta bud'e kofar, daya daga cikin masu aikin ce Atine, ta russuna ta gaishe ta sannan tace tayi baki ne a falo. Ok tace ta rufe kofar ta koma ta gyara fuskar ta, ta fesa turare ta dauko wayarta ta fito. Yan mata ne su biyu kyawawa dasu masha ALLAH, suna zaune suna kallon TV ta fito,

 

"Sannun ku da zuwa."

 

"Yawwa." Suka amsa a sake, suka gaishe ta sannan suka gabatar mata da kansu

 

"Fulani ce ta aiko mu, kayan gara ne dangin su alkaki dasu bakilawa da dublan, sai gireba da sauran su, tace gashi nan zaku iya tayin baki tunda kun dawo."

 

"Kai mun gode sosai, Allah ya saka da alkhairi."

 

Ta tashi ta bubbude, ta dawo ta zauna tana murmushi ta sake godiya, aikin gidan mace ne kayan gara amma basu bari anyi mata ko daya ba, dama tasan dai ko za'a yi sai dai a gayawa su Mamma suyi mata sai gashi sunce ba sai anyi ba,itama yar su ce kamar Muhammad din.

   Hira sukayi sosai tun tana nokewa har ta saki jiki dasu dan suna da hira ga faram faran kamar sun saba. Tare suka ci abincin da suka zo dashi alkubus da miyar taushe, suka bita kitchen da zata yi ma Moh dan abincin sa, suka tayata sai yamma suka tafi, bayan sun mata alkawarin zasu dawo basa so ya dawo ya same su dan tsaf zai kore su, jin su kawai tayi dan batayi tunanin zai aikata ba, bata san yadda yake tsare musu gida da daure fuska bane shiyasa har yake mamaki dan sun ce ba zasu zauna ya same su ba.

   Suna fita kuwa sai gashi ya shigo, yaga fitar motar su amma basu tsaya ba suka kara mai. Bud'e hannun sa yayi ya tsaya daga jikin kofa, ta tafi a sanyaye ta fad'a jikin sa, ya rungume ta yana shafa kanta.

 

"Sannu da zuwa yallabai."

 

Ta karbi rigar hannun sa suka rankaya cikin falon, sai da ya zauna sannan ya amsa mata sannun ya dora da

 

"Baki kikayi?"

 

"Su umaima ne, daga chan gida aiko su."

 

"Yan rawar kai, tun yaushe suka zo?"

 

" Wajen twelve din rana."

 

" Ah kice kin samu yan hira ko nace yan surutu dan bakin su sam baya shiru."

 

" Naji dadin zuwan su kuwa, sun tayani hira ai."

 

" Sun kyauta da suka tafi kafin na dawo, dan tsaf zan saka yarinya frog jump ba abinda ya damen."

 

Ya fad'a yana kai cup din ruwan da ta zuba masa bakin sa,

 

" Da gaske wai?"

 

" Da gaske mana, suma sun sani ai, kila ma sun fada miki ko?."

 

" A ah." Tace tana dariya

 

" Ya yau din? Ya gidan naki?"

 

" Alhamdulillah, komai yayi Masha ALLAH, Allah ya kara arziki, thanks for everything,

 

" Amin Amin, I'm glad you like it."

 

Yace cikin jin dadin addu'ar ta

 

" I love it!"

 

" Masha ALLAH."

 

***Tun ranar farko da Bashir ya samu damar shigowa dakin har yayi abinda yayi, tun daga lokacin duk dare sai ya lallabo, ranar farkon tana jin su suka haura sama da uwargidan tasa suka fado, sai da k'yar suka daidaita dan shima jan wuya yayi mata ganin idan ta biye masa zai iya cewa su rabu yasa ta kyale shi, taga kansa rawa yake ya samu yarinya karama shiyasa ta kwantar da kanta ta cigaba da bin sa tana so taga iyakar limit din iskancin nasa, tasan sarai yana zuwa dakin da dare amma ta share bata taba nuna masa ba, wani zubin ma akan kunnenta komai yake faruwa amma ta daure dan plan dinta akansa ba na yanzu bane, shigo shigo babu zurfi tayi masa sai ya gama sakankancewa zatayi maganin sa.

   Ranar ma kamar yadda ya saba kawo mata waya suyi magana da Mama haka ya kawo mata, ta karba tana daga kwance da babu wani aiki da takeyi yanzu matar gidan ta rage takura mata, dattijuwar me aikinta da ta tafi gida ta dawo shiyasa aikin ya rage mata sai dai taci ta kwanta ga uban kasalar da take fama dashi ga shegen nacin Bashir da yake hanata sakat, tana shan wuya sosai a hannun sa dan baya daga mata kafa ko kad'an, tun tana masa rashin kunya har tazo ta kyale shi yayi uwar da zai yi, ranar da zata samu hanya kawai take nema wallahi ta tafi ba zata dawo ba ko me za'a yi mata kuwa.

  Wayar ya mika mata bayan ya gama amsawa da toh, suka gaisa da Mama ta take fad'a mata haihuwar Aunty Bilki, tayi murna sosai ana take jin gobe suna kuma a gidan su za'a yi sunan saboda akwai fili sosai

 

"Ki lallaba shi ya kawo ki na dai gaya masa."

 

"Toh shikenan, zan kira." Ta katse wayar ta mika masa

 

"Dan Allah ka barni naje suna gidan mu gobe."

 

"Ki shirya da safe zan mika ki sai na wuce garari na, idan na gama sai nazo mu dawo."

 

Yace ya sa kai ya fice da bishi da kallon mamaki, bata taba tunanin zai yarda haka kai tsaye ba, murna ta hau yi ta dinga zagaye dakin tana jin kamar wahalar ta, ta kare kenan dan ko giyar wake take sha idan taje gida ba zata dawo ba sai dai Abba ya kashe ta.

  Murmushin mugunta yayi yana barin dakin, shi kadai yasan tsiyar da ya shirya ya kuma tabbatar da ko taje gidan toh sai ta dawo da kanta ko Maman ta sakota gaba ta dawo da ita.

 

***Waya suka gama yi da Ya Maryam ta cigaba da shiryawa a tsanake saboda safiya ce, sannan yace ta jira shi ya fita toh dole sai ya dawo zata tafi, tana so taga Abban ta da Marwan da Gaji da sauran yan gidan, shiyasa ta tashi tun wuri ta hau shiryawa yadda zata samu zuwa da wuri ta dade kuma.

   Tana zaune taji shigowar motocin sa, ta yaye curtains din dakin ta ga wasu motoci guda biyu da bata san su a gidan ba, sakin labulen tayi, ta sake fesa turare ta fito suka hadu a falo.

   Tafi ya shiga yi mata dan ba karamin kyau tayi ba, lace ta saka me orange da black yayi mata kyau ya dace da kalar ta, zaunar da ita yayi ya dauke ta hotuna masu kyau sannan yace idan ta gama ta ga driver nan idan yaso zai zo da daddare su dawo tare. Jakar ta, ta dauko ya rakota har wajen motar ya bud'e mata ta shiga, sannan suka fita daga gidan yana tsaye yana kallon su. Tasa motar ya fad'a shima ya bar gidan dan yana da important abun da zai yi. A daidai lokacin Zeenat suka fito da Bashir, ya kunna machine din da ya aro a wajen abokin sa dan Hajiya ta fita da motar ta, kamar tace ba zata hau ba, sai kuma ta hau dan bata da ko biyar din da zata dauki adaidata sahu, tunanin idan taje gida ta karbo masa sam be zo kanta ba.

 

 

_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*

 

*_NANA HAFSAT(MISS XOXO) s_*

_SO DA ZUCIYA_

 

*_SAFIYYA HUGUMA_*

_DABI'AR ZUCIYA_

 

*_MAMUH GEE_*

_DEEN MARSHALL_

 

*_HAFSAT RANO_*

_HALIN GIRMA_

 

*_BILLYN ABDULL_*

_TAKUN SAKA_

 

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇

D'aya 300

Biyu 400

Uku 500

Hudu 700

Biyar 1k

 

*_Zaku tura kudin a_*

 

6019473875

*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*

*keystone bank*

 

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

 

08184017082

 

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

 

09134848107

2/12/22, 11:31 - Buhainat: Halin Girma

      33

 

*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_*

https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share

 

*_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_*

https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb

 

*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_*

https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS

 

*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_*

https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw

 

*******�

A kusan jere suke tafiya da motar Abba da Habib ke ciki shida mama, kasancewar tint ce ya saka basu gane Iman din bace a ciki, suna shigowa layin su Habib ya sake kallon motar yace

 

"Ina tunanin fa Iman ce a motar nan."

 

"Wacce motar? " Mama tace tana waigawa, gabanta ne ya fadi ganin dalleliyar mota a bayan su,

 

" Ta ya akayi ka sani?"

 

" Number na duba. "

 

Ya amsa mata yana tsayawa a daidai kofar gidan, daidai lokacin motar Iman din itama ta tsaya, yayi daidai da isowar Zeenat a saman machine din Bashir. Mutuwar zaune Mama tayi ta kasa bud'e murfin motar balle ta fito, idon ta yana kan motar da ta gama gane wacece a ciki, ta saitin ta Bashir ya zagayo bayan ya faka machine din, ya leko yana cewa

 

" Sannu da zuwa Mama. "

 

Wani abu taji, ta kalle shi a kaikace kamar ta falla masa mari, tayi dauriya ta danne zuciyar ta ta amsa tana jan kofar ganin yana kokarin bud'e mata, matsa wa yayi ta fito idon ta akan Zeenat da tayi wani irin haske, hasken da tana kallon ta, ta gane na menene, kamar wadda aka sage wa guiwa haka ya shiga jan kafarta zuwa cikin gidan, suka rufa mata baya a jere Iman din na magana da Zeenat da take ta kokarin maida hawayen da take jin zasu zubo mata wanda bata san dalilin su ba

 

"Ashe zaki zo?" Tace a sanyaye

 

"Wallahi, ya gida? Ko waya bamuyi ba."

 

"Wayata ta lalace ne. "

 

" Ayya." Kawai tace suka karasa ciki, nan da nan mutanen dake harabar gidan sukayi kan Iman, kowa so yake ya ganta, duk sun rude babu wanda yabi ta kan Zeenat, ganin haka yasa ta sulale ta gudu bangaren su, ta samu Mama a zaune tana kuka wiwi, kukan bakin ciki, kukan dana sani da aka ce keya ce wadda bata da amfani, ta tuna watarana da aka zo akayi sallama da Iman, ranar ce ta farko da aka fara zuwa kuma wajen Iman din, tun basu kai yanzu ba, da kanta ta saka Hijab ta koreshi irin korar wulakanci, ba tare da kowa ya sani ba sai Habib, wanda bayan ta kore shi ne Habib yake gaya mata waye shi, da kuma gidan da ya fito,. Tun daga lokacin ta dauki alwashin dakushe Iman din, ta kara maida ita mara yanci cikin rashin sanin cewa gata tayi mata, babu in da zata shiga rayuwa ta bata wahala musaman irin abubuwan da suka shafi kula da gida.

   Taba ta Zeenat tayi ganin sai sallama take amma bata amsa ba, firgigit tayi tana dawowa tunanin ta, suka rungume juna Zeenat din ta fashe da kuka, bata hanata ba, sai da tayi me isar ta dan tasan kukan zai rage mata abinda take ji, gwara ace kishiyar uwa ke gallaza maka akan ace kishiyar ka ce zata hanaka sakat da sukuni, abinda tayi ne ya juyo kanta amma ta siga ta daban, sigar da bata taba tunani ko tsammani ba.

  Yan uwan Abba ne suka biyo Zeenat din har cikin gidan nasu, da mitar me ya faru zata shigo ta wuce su babu ko gaisuwa, Mama na jinsu bata ce komai ba, dan tasan da biyu suka zo maganar, tana jin Zeenat din tace suyi hakuri, wanda ya saka su jin nauyi da kunya kuma, suka tafi cike da borin kunya.

  Suna fita Iman ta shigo, ta russuna har k'asa ta gaida Mama kamar yadda ta saba, ko ba komai ita a uwa take kallon ta, dan itace tayi mata komai na mahaifiya idan aka cire shekarun haihiwa zuwa yaye, ita ta sani, ko ma menene dai tayi mata wani abu.

  A chunkushe ta amsa, har yanzu akwai haushin Iman din a zuciyar ta, wanda bata jin zata daina sai ko ranar da ta bar duniya, har gobe tana kallon Iman din ta tuna cin amanar da akayi mata, wanda take ganin da gaske Itace baa kyautawa ba.

   Ta dan zauna a bangaren nasu, babu me magana a cikin su, sai jefi jefi da suke magana tsakanin ta da Zeenat wadda take cike da mamakin sauyawarta, tayi sanyi sosai kamar ba ita ba, ta kuma hangi wani abu a idon ta, da take da yakinin damuwa ce. Tashi Mama tayi ta barsu a falon tayi shigewarta daki, domin ta samu damar yin tunanin abinda ya kamata tayi akan auran Zeenat din.

   Bin ta Zeenat tayi, ganin haka ya saka Iman ficewa ta koma bangaren Gaji in da anan me jegon take, ta shiga yan uwa aka cigaba da kuranta ta da yaba ta, kowa yana so ya samu ya kafa kansa ganin cewa yanzu ta wuce duk wani matsayi ta kai in da basu taba tunani ba, shiyasa kowa yake kokarin chusa kansa dan idan wata dama ta taso ko da ta aikin Hajji ne, toh Iman din zata tuna da mutum.

   Wajen azahar sai ga Yaya Maryam tazo, sai da ta biya ta asibitin da take ANC sannan ta tawo shine dalilin rashin zuwan nata da wuri. Jan Iman tayi suka koma gidan su, suka zauna su isu matasa aka hau hirar aure da yadda rayuwar auren take ma baki daya, sosai Iman take daukar haske, tana karuwa da wasu abubuwan tunda sun fita jimawa, bata saka musu baki ba, a tunanin Yaya Maryam ma bata jin su, nan kuwa ta haddace komai akanta.

  

 

***Tare suka shigo da Musaddik, wanda kallo daya zaka yi musu kasan a gajiye suke sosai, babu wanda yayi magana sai da suka huta sannan ne Musaddik ya mika masa wayar sa da ake ta faman kira tun suna hanya, karba yayi ya daga yana kishingid'a a saman kujerar

 

"Ya akayi? Kun duba yadda abun ya samu kansa a cikin part din?"

 

"Mun duba dukka CCTV footage na gaba daya area din, bamu ga kowa ba a kusa da wajen ma, har zuwa kofar shiga shashen, falon kuma babu CCTV kasan, time da za'a saka kace baka so. "

 

" Na sani, shikenan ba damuwa. "

 

Yace yana zare wayar daga kunnen sa, ya ajiye yana murmushi wanda ya saka Musaddik kallon shi

 

" Akwai wanda yake so yayi wasa da hankali na, ko ma waye yasan babu cameras a ciki, target din su iya na wajen ne kawai. "

 

" Me kake tunani? "

 

" I can't say exactly, amma dai akwai wani abun daban ba sarauta ba, ko ma waye yana da matsala da aure na, ba sarauta ba. "

 

" Laila fa? "

 

" Ba ita bace. "

 

" Toh me zasuyi benefiting anan, ban gane komai ba. "

 

" Guy, baka san wanne irin mutane ne suke zagaye da gidan nan ba, da kuma kudurin kowa, zaka sha mamaki amma. "

 

"Ka sansu? "

 

" Almost.. "

 

" Then why are you allowing them to walk over you? Bayan kana da duk damar da zaka yi musu abinda zakayi to get rid of them. "

 

" Ba zai yiwu ba, this is not a military war, wannan fad'an ba ma makami bane, ko na gwajin kwanji ba, sai ka zama very very careful da duk moves dinka, akwai bakin ciki a gidan sarauta, akwai kyashi, da hassada. Masu son kujerar ba mutane bane yan kad'an, suna da yawa kuma kowa zai iya komai domin ganin ya samu abinda yake so"

 

Gid'a kai Musaddik yayi yace

 

" It's harder than i thought. "

 

Murmushi Moh yayi, ya hade hannuwan sa waje daya, suka fitar da sauti me dan kara, ya mike yana zuba hannayen sa cikin aljihun sa

 

"Muje naga Takawa."

 

"Owk." Yace ya mike suka fita

 

***Be samu ganin Takawar ba kamar yadda ya saka rai, ya zauna zaman jiran sa dan yana so ya nema masa alfarma akan tafiyar da za'a yi akan wani aiki gashi har da sunan sa, baya son yayi nisa da gida dan a kalla zasuyi wata guda cif, yasan idan ya samu Takawar ya kira waya za'a iya cire sunan sa, duk da tun daga last yace ya daina nema masa alfarma, tun da shi yaji ya gani dole ne yabi dokar aiki, sai gashi ya dawo yanzu be kuma san yadda zata kaya musu ba, shi kansa kunyar neman alfarmar yake amma kuma baya son tafiya ya bar Iman ita kadai bata gama sanin komai ba.

   Har sukayi la'asar suka dawo Takawan be dawo ba, cigaba da zaman jiran sa sukayi Muhammad har da dan baccin sa,ya bar Musaddik yana kallo dan dama shi mayen kallo ne. Sai goshin Magriba sannan suka ji dawowar sa, alwala suka daura suka fita zuwa masallaci aka yi sallah,.

   Yadda ya dawo da irin wannan lokacin dama babu wani zama da zai kara direct ya wuce gida dan yana bukatar ya huta sosai.

   Shawara sukayi akan kawai su dawo gobe da wuri kafin ya fito zaman fada. Da wannan shawarar sukayi amfani suka tafi, suka wuce kai tsaye gidan su Iman daukota. A ransa ya kuduri zai kaita ya nuna mata dakin da ya zauna har ya kwana aciki saboda ita!

 

***Akwai Yayar su Abba da take turai tare da iyalin ta, sukan dade basu zo ba yawanci sai dai waya suke yi, akwai dan ta Mahfuz zai yi sa'an su Habib ko ya dan d'ara su da kadan, duk ciki shine me zumunci me son dangin sa, tun da ya girma idan ya samu lokaci ya kan zo yayi wata biyu ko daya ya koma, karshen zuwan da yayi ya jima sosai be dawo ba, sai wannan lokacin da yazo. Yaso ya samu bikin da aka ce masa za'a yi, duk da ba wani sanin su yayi ba saboda yawansu sai kuma aka samu yar matsala da ta dakatar da zuwan sai yanzu. Yana da wasa sosai da sakin fuska , abu daya yake hada shi da kowa shine yadda dabi'un sa da al'adun sa suka sha banban da na Malam bahaushe, gashi dama bahaushe ko yaya ka kuskure wajen al'ada wadda ba irin tasa ba be kuma karbe ta ba,toh fa zaka samu matsala dashi. Hakan ce ta kasance ga Mahfuz, yadda yake mu'amular sa tasha banban da tamu, dole ne za'a ga banbanci wanda shi tsakann sa har ga Allah ba da wani abu yake ba

  Tun da ya shigo falon ya dora idon sa akan Iman ya kasa daukewa, be kawo matar aure bace sam, gefen ta yaje ya zauna daf har sai data dan matsa, suka gaishe shi dukka ya amsa idon sa na kanta.

 

"You are beautiful." Yace mata kan sa tsaye, gabanta ne ya fadi, ta kalli Yaya Maryam ta kalli sauran yan dakin, sai kawai ta mike tana tattare jakar ta.

 

"Bari naje wajen Gaji kafin ya zo."

 

Bata jira amsar su ba tayi gaba, ya tashi da sauri ya bi bayanta ya jera da ita yana yi mata surutu, da hausar sa da ba wani ganewa take ba, tana shiga part din Gajin text din Moh ya shigo wayarta,

 

"Muna waje." Yace a text din kawai, sallama tayi wa Gaji kawai dan kuma babu zama, ta juya zuwa nasu gidan ta tarar da Zeenat a zaune tana cin tuwo, nan ma tayi wa Maman sallama tace ta gaida gida. Fitowa tayi rik'e da hannun Marwan, ta koma wajen su Yaya Maryam tayi musu sallama, suka firfita zasu rakata, anan suke ganin ana sauke kayan abinci a irin motar da Iman din ta gani dazu a gida, ranta ne ya bata lallai aikin sa ne, tana jin su Maryam suna maganar sai dai idan shine ya aiko dan cikin surukan gidan babu wanda zai aiko da kayan abinci haka masu yawa. Har gate suka rakata sannan suka juyo,  Mahfuz na ganin zata bita ya tashi ya sake bin ta suka rankaya zuwa waje, kamar tace masa ya koma amma sai ta kasa tana jin nauyin sa. Tun da suka fito idon Moh akan su, ya gama tabbatar da ba Habib bane, ba kuma Khalil bane dan ba zai kara gangancin da yayi a baya ba.  Ransa ne ya baci, ganin yadda suke jerawa yana mata magana da yanayin yadda yake maganar. K'asa hakuri yayi, ya balle murfin motar ya fito daidai lokacin da Mahfuz yake kokarin kai hannu ya bud'e mata kofa, gashi yayi kusa da ita sosai.

 

"Dalla malam baka da hankali ne?" Ya daka masa tsawar da ta saka Iman sakin yar jakar hannun ta, tsayawa Mahfuz yayi yana kallon sa yace

 

"Pardon?"

 

Wani banzan kallo yayi masa, ya zagayo ya kama hannun ta, ya jata zuwa dayan side din motar ya turata ciki, be lura ba sai data bigi ya rufe kofar da karfin sannan ya dawo wajen Mahfuz din dake tsaye rik'e da jakar Iman din da ta fadi cikin mamakin abinda ya harzuka gayen.

 

"Wannan shine last warning dinka akan matata, ko waye kai komai alakar ka da ita, kar na sake ganin ka haka kusa da ita, idan ba haka ba wallahi sai na balla kafarka, nonsense."

 

Be jira abinda zai ce ba, ya bud'e motar a fusace ya shiga ya rufo, Musaddik dake gaba ya juyo zai magana yaga yanayin sa, sai kawai yayi shiru, yace ma driver ya ja, jan motar yayi suka bar wajen.

 

_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*

 

*_NANA HAFSAT(MISS XOXO) s_*

_SO DA ZUCIYA_

 

*_SAFIYYA HUGUMA_*

_DABI'AR ZUCIYA_

 

*_MAMUH GEE_*

_DEEN MARSHALL_

 

*_HAFSAT RANO_*

_HALIN GIRMA_

 

*_BILLYN ABDULL_*

_TAKUN SAKA_

 

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇

D'aya 300

Biyu 400

Uku 500

Hudu 700

Biyar 1k

 

*_Zaku tura kudin a_*

 

6019473875

*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*

*keystone bank*

 

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

 

08184017082

 

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

 

09134848107

2/14/22, 19:05 - Buhainat: Halin Girma

34

 

*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_*

https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share

 

*_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_*

https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb

 

*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_*

https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS

 

*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_*

https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw

 

*******�

Tun da suka dauki hanya babu wani wanda yayi magana a cikin su, ransa a bace yake matuka. Manne da jikin kofar take, cike da mamakin dalilin fushin sa haka, a kalla ya tsaya ya fuskanci abinda yake faruwa kafin ya yanke hukunci haka, abun ma dariya ya so bata, yadda ya jata zuwa cikin motar, lallai da gaske sojoji akwai su da temper, idan ba haka ba, menene abun tashin hankali anan? Tana jin sanda suka sauke Musaddik yana masa sai da safe ya amsa da k'yar, suka ja motar sai gida.

   Motar na gama tsayawa ya balle murfin motar ya fice ko bi ta kanta be ba, jiki a sanyaye ta fito itama, ta bi bayan sa cike da mamakin sa. Bata same shi a falo ba, kai tsaye ta wuce bedroom dan rage kayan jikin ta da suka dame ta, baya dakin kamar yadda tayi tunani, kuma be shigo ba har ta gama sauya kayan ta fito falon ta zauna tana bud'e wayarta. Ta jima a zaune a wajen, sannan ya fito sanye da kajaren wando babu riga a jikin sa, wuceta yayi ya dauki abu a cikin wata drawer a falon ya koma dayan dakin da ya fito. Ya sake dadewa sosai dan har tayi tunanin ta bishi ta gani sai gashi ya fito ya doro gajeriyar jallabiya a jikin sa, yana kamshin turaren sa na hugo boss.

 

"Abincin nan za'a kawo maka ko achan zaka ci?" Ta tambaye shi bayan ya zauna

 

"No ba zan ci ba."

 

Sak'alo tayi tana duban sa, yaki ko kallon sashen da take sai ma fito da waya da yayi yana daddanawa. Tashi tayi ta bar falon ta koma daki cikin rashin jin dadin abinda yayi mata, wannan ai wulakanci ne, me tayi haka? Ji tayi hawaye na kokarin zubo mata,  kokarin maida shi tayi tana daga fuskar ta sama.

   Tana tashi kiran Takawa na shigowa wayar sa, ya daga yana mikewa tsaye

 

"Barka da wannan lokacin Takawa."

 

"Barkan ka dai, kuna lafiya ya iyali?"

 

"Alhamdulillah wallahi."

 

"Toh madallah, alfarma akayi min akan tafiyar da zakuyi, dalilin da ya saka sunanka ya fito saboda ana bukatar jajirtattun mutane kamar kai, kuma kai zaka jagoranci tafiyar,  sannan akwai alkwarin karin girma akan ka bayan an dawo, dan haka nake so ka ajiye komai ka tafi, Allah ya baku sa'a ku dawo lafiya."

 

" Amma..." Yace a firgice

 

"A'ah fa! Bana so naji komai Mohd, na jima ina neman alfarma irin wannan akan ka, komai idan har baka so toh fa an barshi, waya kawai zan, wannan kuwa takanas ya kira ni mukayi magana na kuma bashi tabbacin zaka je, toh kayi hakuri kaje."

 

" Shikenan Nagode Allah ya kara girma, zanyi duk yadda akace."

 

" Yawwa, Allah ya taimaka ya baku sa'a, Allah yayi albarka."

 

" Amin."

 

Ya amsa a dunkule zuciyar sa na wani irin suya, wato sai DG ya riga shi samun Takawa akan maganar ya kuma nemi alfarma yasan Takawa dole ya amsa masa, me ma ya saka shi wai kin tsayawa yaga Takawan a dazu ya tafi? Ai da duk haka bata faru ba. Wani abu me ya tokare masa makoshi, ya jefar da wayar a saman kujerar yana barin falon da sauri zuwa daki.

  Tana zaune a gefen gadon tana tunani ya shigo, ya wuce wajen da jakar sa take ajiye ya ciro flash din, ya dauki system ya sake barin dakin. Hada su yayi da dayan na wajen Iman, ya kunna kowanne yayi copying dinsa akan system din, sannan ya saka su a envelope ya mayar jakar. Tafiyar da zai yi Itace zata basu kafa wanda har za'a iya samun matsala be samu dukka bayanan da yake son samu ba, yanzu dai zai damka wa Musaddik flash din guda biyu, ya ajiye a wajen sa dan sune manyan evidence dinsa idan ya tashi yin abinda ya jima yana shiryawa.

  Wayar sa da ya jefar dazu ya dauko ya kira Musaddik din, sukayi magana sannan ya ajiye yana dafe kansa. Zai iya jure komai amma banda abu biyu, iyayen sa da matarsa, idan har aka samu matsala zai dauki matakin da ba zai ma kowa dadi ba.

   Tun tana jiran shigowar sa har ta gaji ta hakura, ta kwanta tana matsar kwalla, bata ga abin fushi ba sam, bata kuma san ta yadda zata fara bashi hakuri ba, ba wai dan tana ganin ai bata yi laifi ba me yasa zata bashi hakuri, sai dai ta rasa fuskar da zata iya bashi hakurin.

   Chan cikin dare ta farka bayan bacci ya dauke ta da k'yar, ta ganshi a gefen gadon yana bacci hankalin sa kwance, ya riga ya saba mata tun farko tare suke kwanciya, cikin bargo daya amma sai gashi yau, akan abinda bata da laifi akai,yana fushi da ita. Baccin ne ya kaurace mata gaba daya, ta dinga tunanin wai dama haka auren yake kenan? Sai wajen asuba sannan ta samu baccin ya kwanshe ta bayan ta sha kuka ta gode Allah.

   A kanta ya tsaya yana kare mata kallo, yadda ta kwanta sai ta bashi tausayi sosai, be san me ya hau kansa jiya ba, amma ba wai haushin ta yake ji ba, bayan ma wayar da yayi da Takawa zai iya cewa ya manta abinda ya faru, tunanin abinda zai faru idan baya nan shi yafi daga masa hankali har ya hanashi zuwa ya kwanta sai dare sosai.

  Hannu ya kai ya shafi gefen fuskar ta, ta bud'e idon tana salati a hankali, ganin shi da tayi a tsaye akanta yana mata murmushi ya sakata tashi da dan sauri tana gyara jikin ta

 

"Good morning Baby,."

 

Yace kamar babu wani abu da ya faru, bata amsa ba, sai zuro kafarta da tayi ta sakko, ta wuce shi zuwa toilet dan ta makara daga ganin yadda haske ya cika dakin. Hijab ya ciro mata ya shinfid'a mata abun sallah, ya zauna yana jiran fitowar ta. Ko da ta fito bata kalle shi ba, ta tada sallar ta, da ta idar ma sai kawai ta kwanta a wajen tana janyo hijab din ta rufe fuskar ta dashi. Tasowa yayi tsam yayi zaman dirshan a gaban ta, ya janye hijab din yana dagota, hawayen da ya gani a saman fuskar ta yayi mugun bashi mamaki

 

"Innalillah, kuka? Don't tell me kuka kikayi tayi the whole night..."

 

"Ya Salam...Look at your eyes, I'm very sorry, ki yafe min dan Allah."

 

Bayan hannun ta tasa tana share hawayen da suka ki tsayawa, ita kanta bata san na menene ba, kawai tasan she's weak, tana jin wani irin weakness a tattare da ita, she can't take fushin sa a gareta, he's so nice to her ko yaya yayi fushi zai bata wahala sosai. Rarrashin ta ya dinga yi da kalamai masu taushi, har sai da ya tabbatar da kukan ya tsaya, sannan ya taimaka mata suka bar kasan suka koma saman gado.

 

"Dole zanyi fushi, shi zaman aure dama zo mu zauna ne zo mu saba, I can equally make mistake, ina da kishi sosai Fatima, ba kuma wai dan naji a raina wai kin kula shi bane, son da nake miki ya saka, please ki kula sosai. "

 

" I'm so too. " Tace bayan ta amsa masa da toh.

 

" Baki komai ba ai, nasan wacece matata, kawai dai... "

 

" Me?"

 

" Ashe dai ana so na... "

 

Duka ta kai masa ya goce

 

" Allah da gaske, naji dadi sosai, zan biya bashin duk tears din da akayi min asarar su, amma kafin nan, zanyi tafiya, karshen week din nan. "

 

Da sauri ta kalle shi, sai ya kama hannun ta ya fara yi mata bayani yadda zata fahimta

 

" Kinsan yanayin aikin mu dama yadda yake, ni dinma dai kawai dai kawai dai, amma wannan karon ba zan iya kin zuwa ba, dole ne dan akwai Takawa a cikin maganar. "

 

" Dadewa zakayi? "

 

" Uhmm... Ban dai sani ba, amma in sha Allah ba zamu dade yadda kike tunani ba. "

 

" Allah ya kaimu, ya bada abinda aka je nema. "

 

" Amin ya Allah, an koma strike, akwai driver da zai dinga kaiki ya jiraki ya dawo dake, hakan nasan zai debe miki kewa, da ina tunanin ko a chanja school, amma kuma tunda har kun kai 300lv gwara ki karasa ko? ".

 

" Eh hakan yayi. "

 

" Yawwa my wife, yi min murmushi na gani toh."

 

Murmushi tayi, sukayi dariya a tare suka bar komai a bayan su, suka fita domin karya kumallo.

 

***Zaune yake a irin kujerar nan me jujjuyawa, kansa sanye da cowboy hat, sai bakin glasses da ya rufe kusan rabin fuskar, jujjuya yake akai yana busa sigari, daga bayan sa yara ne biyu majiya karfi, kowannen su ka kalla zaka tabbatar da zai iya aikata koma wanne irin aiki ne. Knocking akayi, ya daga kansa yana duban su, kafin ya gid'a kan nasa alamar eh, wanda yake ta bangaren kofar ne yaje ya bud'e yana matsawa baya, suka shigo su biyu mace da namiji, kujerun gaban sa suka zauna, ya cigaba da busa sigarin sa ba tare da yayi musu magana ba, sai da suka dau wani yan dakiku a wajen sannan ya jefar da sigarin ya saka kafa ya murje ta.

 

"Kun samo abinda ya kamata ku samo din?"

 

"Za'a samo dai, komai yana tafiya according to plan, gashi zai yi tafiya."

 

" Tafiya? " Yace yana kallon su

 

" Eh zaiyi tafiya karshen satin nan. "

 

" Wonderful, opportunity me kyau, lallai lokaci yayi da kowa zai samu abinda yake so. "

 

" Menene next? "

 

" Tafiyar sa, let me know when he's gone."

 

" Me zakayi?"

 

" Matsala ta ce wannan, bani da matsala da cikin gidan ku, abu biyu ne suka hada mu zuwa uku, a wannan gabar kowa has to play his on part dakansa. "

 

"Shikenan. "

 

Zaro wata sigarin yayi ya kunna mata wuta, suka mike suka fita, ya bi su da kallo kafin yayi murmushi. Moh zai yi tasting abinda yaji a lokacin da ya raba shi da abinda yafi so, shi abu daya ya raba shi dashi, amma shi zai raba shi da kusan abubuwa uku zuwa hudu masu matukar muhimmanci a rayuwar sa, ko zai mutu sai ya dauki fansa akansa, sai ya dandana masa bakin cikin da be taba dandana irin sa ba.

  Mikewa yayi bayan ya gama zukar sigarin, ya tura kofar wani daki, ya shiga bayan ya kunne flashlight din wayar sa, saboda tsananin duhun da dakin yake dashi. A gaban mutumin da yake kwance magashiyan ya durkusa, yana tallafo kansa, sannan ya haske shi da wayar sa da ta kusan kashe masa ido

 

"Ka kusa samu yancin ka, bayan na tabbatar da na samu duk abinda nake so a wajen shi wanda yafi ma hatta iyayen ka, kayi hakuri aiki ne ya biyo ta kanka, kai kadai ne kafi kowa kusanci dashi, dan haka dole ne kaima ya sha wahala!"

 

"Gwara kayi ta ajiye ni a bakin dakin nan, akan kayi wani abu akan sa, wallahi wallahi kaji na rantse ma ko? Kuda idan ka bari ya taba wani abu na jikin sa, sai ya karar da duk dangin ku!"

 

Dariya ya kece da ita mahaukaciyar dariya, ya saki kansa da ya tallafo ya bige da simintin wajen

 

" Idan yana takama da mulki ne, ko kuma khakin da yake jikin sa, toh bari kaji, babu abinda ya isa yayi min dan nayi nisan da bazaka taba tunani ba, k'asar nan tayi lalacewar da su kansu masu tsaron lafiyar taku ba tsira sukayi a wajen mu ba, shi karamin kwaro ne."

 

Soma takawa yayi har ya kai kofa, sannan ya juyo yace

 

" Daga yau zuwa gobe amfanin ka zai kare, zabi na ne, na barka ka tafi, ko kuma na kare rayuwar ka gaba daya Musaddik Izzeeddin!

 

_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*

 

*_NANA HAFSAT(MISS XOXO) s_*

_SO DA ZUCIYA_

 

*_SAFIYYA HUGUMA_*

_DABI'AR ZUCIYA_

 

*_MAMUH GEE_*

_DEEN MARSHALL_

 

*_HAFSAT RANO_*

_HALIN GIRMA_

 

*_BILLYN ABDULL_*

_TAKUN SAKA_

 

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇

D'aya 300

Biyu 400

Uku 500

Hudu 700

Biyar 1k

 

*_Zaku tura kudin a_*

 

6019473875

*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*

*keystone bank*

 

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

 

08184017082

 

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

 

09134848107

2/14/22, 19:05 - Buhainat: Halin Girma

35

 

*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_*

https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share

 

*_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_*

https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb

 

*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_*

https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS

 

*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_*

https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw

 

*******�

Da wuri Musaddik ya iso gidan, dan basu samu haduwa ba tun ranar da sukayi waya sai yau din da zai tafi, ya riga ya shirya shi kadai yake jira, yana zuwa ya dauko envelope din ya damka masa a hannun sa

 

"Ka kula sosai dan Allah, idan har lokacin da ya kamata yayi, ban dawo ba zan fada maka sai ka damka su a hannun Aji! Dan Allah kar kayi kuskure, ka kula sosai, kai kadai na yarda dakai da wannan amanar."

 

"In Sha Allah." Yace yana rik'e envelope din sosai.

   Ciki ya koma, ya barshi a wajen ya tarar ta gama hada masa jakar sa waje daya, tana gaban jakar ta zabga tagumi har ga Allah bata son tafiyar tasa, amma kuma dole zata hakura saukin ta daya fitar da zatayi school, ga ma'aikata birjik an kara karo wasu ma, gate din ma kuma cike yake da jami'an tsaro da ba dan haka ba, ba zata iya zama a wannan tafkeken gidan ba.

   Tashi tayi ganin ya shigo,ya kalle ta ya kalli jakar sai kawai ya rungume ta

 

"Zanyi missing dinki sosai, take care of yourself for me dan Allah, idan kina bukatar wani abu, reach out to me, idan baki sameni ba, Musaddik yana nan, nayi miki saving number dinshi kema zan bashi naki."

 

" Ai babu ma abinda zan nema, akwai komai."

 

"In case dai."

 

" Owk tam, nagode. "

 

" Yawwa, muje ki rakani. " Ya rik'e hannun ta suka fito har wajen mota, ta tsaya daga gefe bayan ya shiga ya zauna, yayi mata murmushin karfafa guiwa itama ta maida masa zuciyar ta na rauni, daga mata hannu yayi har suka fice daga gidan gaba daya.

 

***Abinda ya faru lokacin da Bashir yazo daukar Zeenat bayan tafiyar Iman, suna barin kofar gidan yana zuwa, adaidaita sahu yazo dan ya maida machine din wa maishi, aikawa yayi a kirata, dan babu waya a hannun ta, Mama na jin sakon kiran ta zira mayafi taje wa Zeenat din tana zuwa, ta je ta same shi a tsaye yana jira ta fito suna magana da me napep din. Be yi mamakin ganin Maman ba, dan dama yasan ba za'a yi komai ta sauki ba, gaishe ta yayi taki amsawa, sai ma cewa da tayi tana bud'e hannun ta

 

"Bani takardar yata."

 

"Ban gane ba Mama?"

 

"Eh ina nufin ka sauwake mata kaddareren auren ka dan ba zata koma ba ku karasa kashe ta kai da tsohuwar  matar ka."

 

" Amma Mama Zeenat tana so na, nima Ina son ta, kiyi hakuri dai ta fito mu tafi."

 

"Wanne so? Bayan yaudarar da kayi har kana tunanin tana son ka?"

 

"Toh ni dai nasan auren soyayya mukayi da ita, kiyi hakuri ki bimu da addu'a kawai."

 

"Ba zan hakurin ba, Malam takardar 'yata kawai nake so ba dogon surutu ba."

 

"Ba zan iya sakin ta ba gaskiya, kiyi hakuri kawai."

 

Sai ya juya ya haye napep din,da sauri ta bishi tana kiran sa, me napep yaja suka bar kofar gidan. Tana juyowa da nufin komawa gida sai ga Abba a tsaye a bayanta, ya harde hannayen sa yana kallon ta ransa a matukar bace, bacin rai da be taba yin irin sa ba tun da aka fara hayaniyar auren Zeenatun, tsoro ne ya shige ta, dan yadda taga bacin rai a fuskar sa zai iya aikata komai.

 

"Dan Girman Allah..."

 

Daga mata hannu yayi

 

"Babu abinda zaki ce min, bana son naji komai!

 

Jikin ta ne ya hau rawa, yayi ciki ta bishi tana son yi masa bayani, ba zai tsaya jin komai ba, ba kuma zai dauki maganar da sauki ba wannan karon, tayi abinda ba zai mata uzuri ba. A zafafe ya shiga falon yana k'wala kiran zeenatu, ta tashi jikin ta na rawa har tana yar da dan kwalin kanta da yake hannun ta,

 

"Me kike yi har yanzu baki tafi ba."

 

"Uhm.. uhm.. dama..."

 

"Karya kike yi, munafuka!"

 

"Minti biyar kachal na baki, ki fice ki koma gidan mijin ki, na fad'a miki!"

 

Be jira ya sake jin ta bakin ta ba, ba kuma zai saurari magiyar da Mama take masa akan dalilin da ya saka tayi abinda tayi ba, yayi gaba kawai ya shige dakin sa ya rufo.

    Kuka Zeenat ta fashe dashi, da gaske bata son komawa gidan Bashir, ya zatayi yanzu? Gashi taga wani irin fushi a fuskar Abban da bata taba gani ba,dama mama so tayi bayan ta kori Bashir din idan Abban yazo tace shi Bashir din ne yace Zeenat din ta zauna a gida zai yi tafiya ya dawo, daga nan sai suyi ta matsa mata har ya sake ta, shikenan Abban ba zai zargi komai ba, amma sai gashi komai ya lalace tun ba'a kai ko ina ba.

 

"Kina da number Bashir ko?"

 

Girgiza kai tayi

 

"Dan ubanki baki haddace number sa ba? Yanzu ya kike so muyi? Dole ya dawo ya dauki ki ku tafi kafin nasan abinda zanyi akai."

 

"Mama ni ba zan koma ba."

 

"Aikuwa sai kin koma, baki ga fuskar babanku ba? So kike yace na tafi gida shikenan ki rasa wanda zai tsaya miki? Tashi maza ki kira bashir ga wyata kice ya dawo, idan yaso sai mu san abinda zamuyi."

 

Kuka ta cigaba da rerawa a hankali, ta karbi wayar ta saka number tasa ta kira, tayi ta ringing amma be daga ba, ta cigaba da jera masa kira amma babu alamun zai dauka. Rasa yadda zasuyi sukayi, har goma saura gashi bata san gidan ba balle idan tafiya zatayi da kanta ta gane. Suna nan a falon ya fito, ya kalle su sannan ya fice  gaba daya.

 

***Bayan tafiyar sa sai taji gidan yayi mata girma da fadi, ta kwanta a saman kujerar falon tayi lamo tana jin cikin ta na juyawa sama-sama. Bacci ne ya dauke ta a wajen bata tashi farkawa ba sai da rana tayi. Sallah ta fara yi taci abinci sannan ta zauna ta dauko littafan ta na islamiya ta shiga duba su, tana muraji'ar na baya, tana so ta cigaba da karatun ta ko ita da kanta ne ta dinga karawa kanta, zatayi amfani da damar duk da sun koma boko amma ba zata kyale na islamiyya ba, akwai wasu littattafi da take son koya wanda dole sai dai ta samu manyan malamai su koya mata, amma bata san yadda zatayi ba. Tana nan zaune yayi mata text message, tayi masa reply sannan ta cigaba da abinda take har zuwa la'asar, gaba daya sai taji ta rasa ma me zatayi, sai kawai ta zagaya baya wajen ma'aikatan gidan ta same su suna hira, suka tashi da sauri suna tambayar ta abinda take so, murmushi kawai cike da mamakin yadda suke girmama ta take ta zauna a wata kujerar roba, tace zuwa tayi zaman cikin ya ishe ta, nan fa suka hau murna suka cigaba da hirar tana sauraren su, a kalla sun debe mata kewa dan bata dawo ciki ba sai bayan da aka kira sallar magriba.

 

    Washegari ta tashi da murnar zuwa school bayan tsawon lokacin da sukayi a gida, jin ta take tamkar sabuwar shiga dan wasu abubuwan ma ta mance su, tasan da yawa duk yau zasu koma saboda dai kowa ya gaji da zaman gidan. A tsanake ta shirya tsaf, sannan tasaka madaidaicin mayafi akan doguwar rigar atamfar da ta saka brown da touches din blue, ta dauki jaka da takalmi da suka shiga sosai ta saka, tayi shigarta ta mutunci ta fito ta nufi kitchen in da ta hanyar ne ake bi zuwa bq, a kitchen ta tarar da Ummimi, tana karasa hada breakfast dinta, ta russuna har k'asa ta gaishe ta, ta amsa a sake tana dudduba aikin.

 

"Zan je school ba jimawa zan ba, idan an gama komai sai a jera a dining, zanyi bakuwa anjima da rana."

 

"Allah ya dawo dake lafiya gimbiya, idan kina bukatar abu ba sai kin zo ba, kira kawai zakiyi ranki ya dade."

 

"Babu komai karki damu."

 

"A dawo lafiya, Allah ya bada sa'a."

 

"Amin."

 

Tace ta juya ta fita, ta samu driver ya gyara motar, sai kawai ta fad'a baya tana tuna rayuwa yadda take a shekarun baya, shekarun da basu gaza biyu ba. Tun da suka isa makarantar duk in da suka wuce sai an kalle su, a department dinsu kuwa kamar an ga nama ko wata sabuwar halitta, dama labari ya riga ya karad'e ko ina amma dama ance gani ya kori ji, wasu takanas suke zuwa su tabbatar da gaskiyar abinda suka ji. Tayi ta zuba ido ko zata ga Zeenat amma ko me kama da ita bata gani ba, har suka gama abinda zasuyi suka koma gida.

   Tun daga ranar kullum sai taje school din ta dawo, sai zaman gidan ya zama mata kad'an, duk dare kuma suke shafewa suna magana da shi a waya, ba wani sosai take jin kadai ta ba, sannan kuma duk sanda take free da rana ko ta dawo da wuri tana zama ta koya wa masu aikin karantun al'qurani da ta lura kusan rabin su basu iya ba, kawai rayuwar su sun taso ne akan hidimtawa gidan sarautar, tun iyaye da kakanni suke a haka har zuwa yanzu babu wani sauyi da ya samu rayuwar su. Hakan ba karamin dadi yake mata ba, a kalla ita ma zata samu lada me dinbin yawa.

   Wasa wasa sai gashi yayi sati uku cif da tafiya, duk sanda ta tambaye shi yaushe zai dawo sai yace mata surprise zai mata kawai, haka take hakura ta kyale shi, kullum cikin shiri take dan tasan zai iya zuwa mata bakatatan, wasu magunguna da momma ta bata wanda yawancin su na fruits ne da madara su take ta faman sha, dan sosai suke mata dadi har ta kanyi mamakin kanta a lokacin da Mamman ta bata , bata wani ji dadin su kamar yanzu ba.

   Wata rana a cikin ranakun da take zuwa school ta kai yamma, ta tashi duk jikin ta babu dadi, ciwo take amma bata san takamainai me yake mata ciwo ba, kamar kar taje school din amma sai ta daure dai, ta shirya ta kira Ummimi ta rakata, tunda dama sai da yace lallai ta dinga tafiya da masu rakata amma bata tafiya dasu. Tare suka tafi yau haka nan taji bata son tafiya ita kadai, suka jirata tayi lecture ta fito wajen biyar na yamma, a gajiye likis gashi ko ruwa bata saka ma cikin ta ba, kaidar tace bata cin abu a school tun da ma, sai dai idan zata dade irin haka taci ko snacks ne shima ba ko yaushe ba, dan mafiya yawancin lokuta rage kudin da Abba yake bata Mama take ta bata kadan, shiyasa ta koyi yadda zata yi karatun haka,sai kawai ya zame mata jiki ko yanzu da take da komai bata damu taci din ba

   Da sauri Ummimi ta karbi Jakarta da kayan hannun ta, ta tayata bud'e mata motar ta zauna sannan ta zagaya ta shiga bangaren ta, bata lura da su biyu ne a gaba ba, har da wani sai da ya gaishe ta

 

"Amarya barka da rana."

 

"Barka dai, ai ban ma lura ba, ina wuni?"

 

"Lafiya lou wallahi, dama wannan gajiya da kuka kwaso, dama munyi waya dashi ne yace na biyo ta makarantar taku sai mu wuce, zasu sauka da karfi shida da rabi, sai mu dauko shi a airport, amma fa yace kar na fad'a miki dan wai so yake yayi surprising dinki."

 

Dariya ta saka

 

"Lallai, ina ta tambayar sa yaushe zai dawo yaki fad'a min, so yayi kawai yanzu ma sai dai na ganshi kenan."

 

" Ai irin wai surprise din masoya."

 

Dariya kawai tayi, bata kawo komai a ranta ba, ganin Musaddik ne, haka kuma sai taji wani yanayi na dokin ganin mijinta, wanda yau ya cika sati uku da kwana biyar cif da tafiya. Hanyar airport din suka dauka, ta kwantar da kanta a bayan da yake saramata sosai.

 

**A word of encouragement to All TTC mother's (Trying to conceive) do not lose hope, Allah yana tare daku, ku cigaba da addu'a, Allah ya baku 'yaya masu albarka da mu baki daya. Baa debe tsammani daga rahmar Allah.

Post a Comment for "HALIN GIRMA 31-35"