Skip to content Skip to sidebar Skip to footer

HALIN GIRMA 21-25

 


1/31/22, 19:12 - Buhainat: Halin Girma

      21

  

Ta kofar ya koma ya fice bayan ya tabbatar da ya isar mata da sakon da yake son isarwa, yana kallon yadda tayi laushi sosai ta bishi da kallo har ya fice gaba daya.

   Kai tsaye wayar sa ya dauka ya kira Bashir, ya daga yana tafiya zuwa shashen Takawa dan yana son ganin shi

 

"Ya akayi Bashir?"

 

"Barka da warhaka Ranka ya dade"

 

" Barka dai, ya taro?"

 

" Mun gode Allah, an kawo amarya yallabai."

 

" Yayi kyau, Allah ya baku zaman lafiya, ka kula da ita sosai kar naji wani abu mara dadi, karka kuma taba yarda mahaifiyar ta ko wani yace zai taka ka akan matar ka."

 

" In Sha Allah ranka ya dade, hakan ba zata faru ba."

 

"Yayi kyau, sakon ka na wajen Musaddik."

 

Godiya ya hau yi dan dama abinda ya saka kiran kenan. Cilla wayar yayi a aljihu sanda ya isa sashen Takawan da ya zata ya jima da isa a adamawa.

 

***A tsorace take tun bayan da mutane suka yaye, yan matan biyu da aka barta dasu suma basu wani jima ba suka cikawa wandon su iska dan ba zasu iya zaman ba, babu kalar ma da bata yi musu ba akan su zauna amma suka ki, a cewar su idan suka zauna basu san uban da zai maida su gida ba su ba samari masu mota ba ga unguwar da shegen nisa kafin kaje titi. Haka tana ji tana gani suka yi tafiyar su suka barta. Tasha kuka kuwa kamar ba zata mutu, ta dinga tsinewa Bashir albarka taji kamar ta gudu ta bar garin ma baki daya.

   Tana nan a zaune cikin duhu taji ana saka mukulli a kofar gidan, tashi tayi da sauri tana zaro ido,a duhu take dan dama da wayar ta, ta haska kuma babu charge ta mutu tun dazu.

   Shigowa yayi yana haske gidan da wayar sa, ya shigo ciki ya dalle ta, tayi saurin kare fuskar ta tana cewa

 

"Waye!" A tsorace

 

"Amarsu ta ango."

 

Wani abu ne ya tokare mata a makoshi jin muryar sa, tayi kansa da sauri ta hau kai masa duka tana kuka

 

"Allah ya isa ban yafe maka ba, Allah ya isa."

 

Rik'e hannun nata yayi da karfi ya juyar da ita ta dawo tana jingina da bayan sa

 

"Ni kike wa Allah ya isa? Lallai ma yarinyar nan."

 

"Allah ya isa na fad'a mugu, macuci maha'inci."

 

Juyo da ita yayi ransa na soyuwa amma ya danne kamar be ji komai ba, ya dalle mata baki da bayan hannun sa, yayi murmushi yana sake haske ta

 

"Duk abinda ma zaki ce ki fad'a amaryata."

 

Kuka ta shiga rusa wa da karfi, ganin zata iya jawowa a jiyo su a makota ya sakashi jawota ya shiga sumbatar ta, ta dinga dukansa tana harbin sa a kafa amma ko a jikin sa, sai da ya gajiyar da ita sosai sannan ya saketa yana murmushin, a kalla ya rage zafi dan yasan ba lallai Hajjaju ta yarda ta barshi ba.

   A wajen ta duk'a tana kuka, ta dinga jin kamar ta mutu ta huta da abinda take ji, tana jinshi yana waya har ya gama kafin ya dagata tsaye ya rik'e hannun ta a cikin nasa su shiga barin gidan.

   Mota ce a kofar gidan irin wadda yake zuwa wajen ta zance, bud'e mata gaba yayi ta shiga ya rufe sannan ya zagaya ya shiga mazaunin driver ya tada motar suka bar unguwar.

   Tafiya sukayi da dan nisa har suka iso unguwa, gangarawa taga yayi zuwa wata doguwar hanya suka dinga tafiya kafin su isa kofar wani babban gida, horn taga yayi da sauri me gadin ya bud'e gidan ya shiga da motar ciki. Tunanin ta ne ya tafi wani waje daban, ko dai Bashir gwada ta yake yana so yaga yadda zatayi idan ya kaita wanchan gidan shiyasa ya kai ta? Ko kuma dai duk shiri ne. Murmushi ya sakar mata ta cikin hasken da ya hasko cikin motar bayan ya tsaya a gaban ginin gidan.

   Sauri taga yayi ya bud'e motar sanda wata babbar mata hamshakiya ta nufo su cikin wata irin kwalliya, ta sha ado sosai tana walwali, katuwar gaske ce dan zatayi biyu ko ma ukun Bashir din idaan aka hade shi da Zeenat din waje daya.

    Kafin ta kai ga garasowa Bashir din ya isa wajenta. Yayi kamar zai zube a k'asa a gabanta, ta riko shi tana masa murmushi, ware ido sosai Zeenat tayi tana tunani toh ko Maman shi ce? Karasowa tayi daidai kofar da Zeenat din take ciki ta bud'e mata tana sakar mata murmushi

 

"Amarya."

 

Ta kira ta tana sakin hannun Bashir din ta kama na Zeenat din tana jawo ta daga ciki.

 

"Sannu da zuwa kanwata, sannu sannu."

 

"Kanwata?"

 

Zeenat ta maimaita sunan tana bin Bashir da kallon neman karin bayani amma sai taga ya fuske kamar be ganta ba. Takawa suka shiga yi har zuwa cikin gidan wani babban falo da yasha kawa sosai. Wasu mata ne hamshakai suma kamar matar farkon suka tarbi Zeenat din suna tafi, ita dai Zeenat gaba daya kanta ya kulle jira take su samu kebewa da Bashir ta tambaye shi me yake faruwa. Zaunar da ita matar tayi ta ja hannun Bashir din sauran mstan suka hau shewa da dariya, bin su Zeenat tayi da ido har suka haura sama, zuwa anjima kad'an sai gata ta sakko ita kadai babu Bashir din cikin shigar kayan bacci ta karaso falon ta kalli sauran matan tace

 

"A rakata dakin ta ko?"

 

"An gama Lay, an gama."

 

Suka tashi gaba daya, daya ta kama Zeenat din suka nufi wata hanya da take a bayan kafar benen dake falon, wani dogon corridor ne suka bishi har zuwa bayan dakunan gidan, sai wani daki guda daya a wajen da kofar sa tana kallon kofar da suka fito, nan taga an bud'e, sannan sun shiga gaba daya ciki.

   Katifa ce a k'asa karama kamar ta yan boarding sai wata karamar kujerar roba fara, suna shiga kamar jira dama suke matar da ta shigo da ita ta wurgar da ita a saman kujerar har sai da kanta ya bugu da bango, tayi kara saboda zafin da taji kafin wadda suke kira da Hajiya Lay (Layuza) ta rankwafo akanta tana mata kallon tsana tace

 

"Ke dan yar iska ce ke, har kin isa mu hada miji daya? Kin isa nayi sharing dake? Karamar yarinya da bata fi sa'ar yata karama ba, kece kishiyata ko? Toh ni ko a zamanin kuruciya ban zauna da kishiya ba balle yanzu da nasan ciwon kaina nasan abinda nake so, dan haka nan dakin da nake ajiye masu aiki nane kuma na sallame su dan yanzu basu da amfani, sai ki cigaba daga in da suka tsaya, shara wanke wanke, wankin undies dina da girki, komai ma dai da kika sani."

 

Gaba daya kwakwalwar Zeenat ta gaza gane me matar take cewa, ji tayi kamar wani yare take mata na daban da bata sanshi ba, ta dinga jujjuya kanta tana son gasgata abinda taji akan Bashir din, yana da mata dama? Mata babba kamar wanna da ta yi sa'ar uwarsa? Abba ne ya fado mata, sanda ya kirata yake mata magiya kamar ba Mahaifin ta ba, ya kaskantar da kansa yana rokon ta akan ta rufa masa asiri ta hakura da Bashir amma ta shafawa idon ta toka, ta kekeshe kasa tace taji ta gani, yanzu ta yaya hakkin Abban ta zai barta? Tun a ranar farko ta fara fuskantar wannan tashin hankalin.

   Firgigit tayi sanda taji saukar abu kamar ruwa asaman fuskar ta, ta saka hannu ta shafa da sauri tana daga kanta

 

"Kinji abinda na fad'a miki ko?"

 

A hankali ta daga kanta alamar eh, ta daka mata tsawa tace

 

"Baki zaki bud'e kiyi min magana bana son rainin wayo."

 

"Naji." Tace tana barin kwallar da ta taru a idonta ta shiga sakkowa saman fuskarta. Dariya suka kwashe da ita, suka juya suka fita suna cigaba da zantuttukan su mara sa dadi ji.

 

***Bangaren amarya Iman kuwa komai na tafiya daidai, ta dade batayi bacci ba tana tunanin Moh da kalar soyayyar sa me tsayawa a zuciya, koman sa abin so da birgewa ne tun daga maganar sa har yadda yake tafiyar da ita. Da k'yar ta samu bacci ya dauke ta bayan ta gama tunanin nasa. Tun asubah da suka farka basu koma ba, kana jin yadda hayaniya take tashi a masarautar kasan akwai gagarumin shirin da ake yi. Shiryawa suka hau yi ita ta fara wanka sannan su Khadija suka yi. Suna fitowa falon suka tarar da abinci a jere na alfarma yana jiran su, nan suka hau kai suka ci suka yi nak, sannan aka turo tafiya da Iman din shashen Fulani. Alkyabba aka sake saka mata sannan suka fito kanta na k'asa tana jin yadda take shan gaisuwa kamar ta tsaya ta amsa amma yan matan nan sunce mata ksr ta tsaya amsawa haka sarautar take.

   Da murna Fulani ta tarbe ta yau din ma, ta saka aka kaita har uwar dakin ta in da mutane suka dinga shigowa suna ganin ta wanda suke da kusanci da gidan. Ta jima sosai anan har suka soma jin tashin kidan kwarya in da adaidai lokacin su Mamma suka iso sai dai babu Mama, gaisuwa aka sake kafin a rakasu in da ake kidan kwaryar aka nuna musu wajen zaman su, kafin daga bisani a rako Iman din wajen itama.

   Da yamma kuma aka dawo ciki aka sake shiryawa in da aka nufi hall din dan gabatar da bikin da kuma kyaututtukan da aka shiryawa Iman din.

  Sakon Maimartaba ne ya samu Fulani akan yana son ganin Matar Muhammad din dan a yau zasu wuce komai dare, mamaki ya kama Fulani dan a yadda suka shirya kwanaki uku zasuyi a nan din kafin su tafi adamawar, bata sani ba Muhammad din ne da kansa yaje ya samu Takawan ya roke shi akan a rage bidiar dan shi kam ya gaji sosai, take kuwa ya amince har ma ya sanar da Bubu tun a daren jiyan.

   Maimakon a wuce da ita hall din sai aka fara kaita wajen Takawar. Kanta a k'asa sosai kwarjinin sa ya cika wajen ta yadda kowa ya kasa sakewa, nasiha ya soma yi cikin maganar sa da ta saka jikin kowa mutuwa, yayi musu fatan alkhairi sannan ya kare da sake jan hankulan mutane akan yadda rayuwar ta zama, basu dade a wajen ba, suka fito kowa na yaba karamci na Maimartaba da ya karbe su hannu bibiyu ba tare da nuna banbanci ko wani abu ba.

   A gaggauce akayi taron, saboda tafiyar da zasuyi, sosai iman ta samu kyaututtuka masu tarin yawa a yan awowin da basu gaza biyar ba, kowa so yake ace shine yafi, kowa so yake ya burge Fulani da Maimartaba, dan kowa ya san yadda muhammad din yake a zukatansu.

 

***Motoci ne guda uku suka dauke su zuwa airport din daga su Mamma sai wasu yan uwan Abba su uku shikenan wanda zasu adamawar, shima saboda bikin da zasuyi ne suma badan haka ba da babu me zuwa. a lokacin Moh sun dade da isa suna zaune dasu Musaddik ana hira a wani kebantaccen wuri.

   Zuwan su da aka dan suka dauki hanya babu wani bata lokaci. Ita kadai ce a wajenta, babu kowa a saman duk suna k'asa sai ita kadai kwal har ta dinga tunanin dalilin da ya saka aka kawo ta nan din ba abarta wajen su Mamma ba. Kamshin turaren sa ne ya amsa mata tunanin ta, ya karaso ya zauna kusa da ita yana kashe mata ido. Kayan jikin sa ta kalla wanda suka kasance na sarauta, sai takalmin kafarsa da akayi da fatar zaki yayi kyau sosai shigar gidan sarauta, babu hula akan sa ya rik'e ta hannun sa, sumar sa ta fulani ta sha gyara ya fito a bafulatanin sa sosai.

   Shi din ma shigar ta yake kallo, yana kuma yaba yadda komai ta saka sai yaga ya karbe ta yayi dai-dai da ita.

 

"Ba magana?" Yace bayan ya gama kallon nata

 

Mirgina kanta tayi gefe tayi masa murmushi tace

 

"Sannu da zuwa toh."

 

"Yawwa."

 

Yace yana jingina da kujerar jirgin sosai, be sake magana ba sai dai yanayin sa ya nuna mata kamar akwai damuwa, tasan yadda yake mata dan haka yau din sai taga kamar bashi ba, bata sani ba ko sarautar ce ta motsa. Satar kallon sa ta dinga yi sai taga ya kulle idon sa yayi kamar me bacci. Duk sai taji ta takura ta kuma damu, taba shi tayi kad'an, ya motsa amma be bude idon nasa ba, sai kamo hannun ta da yayi ya sakalo shi ta tsakanin nasa hannun ya harde su waje daya, kusan rabin jikin ta ya sauka a nasa, bata sake attempting komai ba har zuwa sanda suka iso jirgin ya sauka suka fito still hannun sa na sarke da nasa.

 

 

  

***Kafarta a mike take tana sauraron bayanin da take mata, ko motsi batayi ba, kamar bata jin me take cewa har ta kai karshen bayanin tayi shiru tana kallon ta. Sai da ta dauki lokaci me tsawo kafin ta gyara zama, ta bud'e hannun ta, ta mik'a mata shi, jikinta na rawa ta ciro kwalbar da take nannade a gefen zanin ta, ta saka mata a cikin tafin hannun ta. Jujjuya shi tayi tayi a hannun nata tamkar me son gano wani abu.

 

"Turare ne ranki ya dade, a jiki kawai ake shafa shi bayan haka babu wani abu."

 

"Kin tabbatar da abinda kika ce?"

 

"Allah ya taimake ki, yadda nayi miki bayanin haka yake, yace kar ayi wasa dashi, sannan kuma kar ayi sakacin da za'a samu matsala."

 

"Rik'e." Ta mika mata, da sauri ta karba tana damke wa a hannun ta sosai.

 

" Kin tabbata babu wani abu da ya faru tsakanin su?"

 

" Na tabbatar, sai da ya nuna min komai kafin ya bani, yau zasu iso sai kiyi kokari kafin su tare a sabon bangaren su dan naji rad'e rad'in bikin ba zai dau kwanakin da aka tsara ba, bisa umarnin Sarki."

 

Murmushi tayi me kyau, ta dawo ta zauna bayan ta ciro wata karamar riga ta karata a jikin ta,sai kuma ta ajiye tana mikar da hannun ta baya.

 

" Kinyi kokari, kina da kyauta me tsoka idan har na samu biyan bukata."

 

" An riga ma an samu gimbiya, ki kwantar da hankalin ki."

 

"Tukunna dai."

 

" Me yayi saura? Yan awoyi ya rage miki ki samu abinda kike so gimbiya ta."

 

Jikin tagar dakin ta karasa, ta daga labulayen tana kallon harabar gidan da yadda hadiman gidan ke kaiwa da komowa a tsakanin bangaren Moh din da na Ammi, tasan duk shirin tarbar bakin ake, hankalin kowa ya riga ya koma chan dan haka zatayi amfani da damar ta isa bangaren Moh ta yi zaman jiran dawowar shi!

 

 

Rano💕

 

*_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*

 

*_NANA HAFSAT(MISS XOXO)  s_*

_SO DA ZUCIYA_

 

*_SAFIYYA HUGUMA_*

_DABI'AR ZUCIYA_

 

*_MAMUH GEE_*

_DEEN MARSHALL_

 

*_HAFSAT RANO_*

_HALIN GIRMA_

 

*_BILLYN ABDULL_*

_TAKUN SAKA_

 

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇

D’aya 300

Biyu 400

Uku 500

Hudu 700

Biyar 1k

 

*_Zaku tura kudin a_*

 

6019473875

*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*

*keystone bank*

 

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

 

08184017082

 

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

 

09134848107

 

 

 

1/31/22, 19:14 - Buhainat: Halin Girma

      22

 

*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_*

https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share

 

*_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_*

https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb

 

*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_*

https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS

 

*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_*

https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw

 

**********

Tamkar rana haka harabar masarautar take, komai an shirya shi an tsara saboda shirin tarbar su. Tafiya sukayi doguwa a ciki kafin su kai wajen manyan gine-ginen cikin masarautar.

   Ba mota daya suka shigo daga airport din dashi ba, shiyasa ma bata ganshi ha a sanda suke fitowa daga mota. Cikin rakiyar hadiman shashen Ammi da na gidan ma baki daya suka isa babban falon nata, da aka kawata shi matuka ana jiran isowar su. Kamar yadda suka samu tarba ta musamman a Kano haka aka karbe su anan dinma. Hakan ya kara bawa su Mamma nutsuwa da tunanin irin yadda Iman din zata samu kanta a gida irin wannan wanda yake cike da abubuwan da ba lallai ta iya dauka ba.

   Bayan sun huta an gabatar musu da abinci ne Ammi ta saka aka rakasu masaukin su, wanda aka ware musu tun kafin isowar su. A gajiya kowa yake dan haka suna zuwa kowa ya mike aka shiga maida maganar yadda aka karbe su da irin sa'ar da Iman din tayi.

   Tana jin su bata tanka ba, hankalin ta ya tafi sosai wajensa tana son jin yadda yake dan ta tabbata da akwai wani abu da ya rage masa walwala.

 

***Tun isowar su ta samu labari wanda dama abinda take jira kenan, ta shirya tsaf babu Kuma abinda zai hanata aiwatar da abinda tayi niyya shiyasa ma bata bari Kilishi ta sani ba balle har ta hanata.

   Shigar sa shashen nasa bayan ya bar wajen Bubu hadimar ta, ta sanar mata wanda dama ta saka ta ne ta saka ido tana ganin ya shiga ta fad'a mata.

   Tashi tayi tana gyara gashin kanta da ta saka ribbon din tayi sako-sako dashi, ta daura babbar Alkyabba akan kayan da suke jikin ta da ya kasance karamar riga ce mara hannu iyakar ta guiwa kawai, sai dogon wando a k'asan da ta saka saboda yadda zai zama ko ina na jikinta ya rufe.

   Turaren da yake cikin Jakarta ta ciro, ta dunkule shi a hannun ta, ta fita ta kofar bayan cikin rakiyar amintacciyar hadimar ta. Tafiyar dake tsakanin bangaren Moh din da nasu da akwai tazara dan haka yasa suka bi ta baya har suka isa. Idon ta, ta daga ta dubi bangaren bedroom dinsa amma sai taga dakin babu haske sai sauran dakunan. Zagayo wa sukayi zuwa gaban ginin masu kula da kofar suka tashi ganin ta, da ido sukayi magana da daya, ya girgiza mata kai alamar eh sannan yace

 

"Yarima na jiranki gimbiya Lailah."

 

Jin haka ya saka dayan saurin bud'e mata kofar, ta kutsa kanta ciki kai tsaye tana jin kamar anyi an gama ta samu cikar burin ta.

   Tafiya ta ke a cikin falon tana kallon komai, yadda aka sauya komai kamar ba part din da take shigowa a duk sanda ta ga dama ba, babban hoton da ke manne a jikin bangon dakin ta kurawa ido tana matsawa gaban sa. Iman ce a jiki, ita da Moh ranar da aka daura aure, sunyi masifar kyau kamar kayi musu magana su amsa. Wani bakin ciki ne yazo ya tokare mata a makoshi, taji kamar tayi wurgi da hoton ya tarwatse a wajen amma sai ta daure, ta maida hannun ta baya tana nufar bedroom din nasa in da tasan zata same shi.

   Kafin ta karasa ta hango glass cup a k'asa a farfashe, ta durkusa ta dauki ragowar tana kaiwa hancin ta, murmushi tayi tana da yakinin komai ya zama daidai, everything is in order kamar yadda ta tsara. Hakan ya saka ta wucewa Kai tsaye ta murda kofar dakin ta kutsa kanta ciki tana zare alkyabbar da take jikin ta, ta zame a wajen ta fadi.

   Muryar sa da ta soma bacewa yayi kokarin cewa

 

"Waye!"

 

Yadda yayi maganar ya saka ta sake tabbatar da komai yayi daidai, basu yi mata shirme ko shiririta ba. Karasawa tayi jikin gadon, ta kai hannu ta taba shi ta hasken bedside lamp da ke kunne, take kallon sa, idon sa yayi masifar komawa ciki yana lumshe su tamkar wanda yake shirin yin bacci irin baccin da yafi karfin sa yake neman kai shi k'asa.

 

"Waye?" Ya sake maimaitawa da k'yar kansa da yake juya masa ya shiga kai masa sakon mayen kamshin da yaji ya karad'e dakin,kamshin da ya dauke shi zuwa wata duniya ta daban, a take yaji komai ya hargitse masa, ya mike da k'yar yana duban ta cikin ido, gaba daya komai ya chanja masa,ta juye masa Iman dinsa gaba daya. Hannu ya kai zai taba ta, ta saka karbi ta tura shi baya ya fad'a saman gadon!

 

***Text message ne ya shigo wayar ta, ta bud'e da sauri tana fatan ya kasance daga shi, kamar yadda tayi tsammani, shi din ne kuwa,

 

_"A rako ki shashe na."_

 

Haka kawai sakon ya kunsa, kifa wayar tayi tunanin yadda zata fara fadawa Mamma yace a rakota bangaren sa. Da kunya sosai bata kuma jin zata iya,shiru tayi tana wassafa abun a ranta, zuciyar ta na ce mata kawai ta kira mamma ta fad'a mata ai ba wani abu bane, wata zuciyar kuma na ce mata a ah. Ta na nan zaune har aka dau tsahon wani lokaci, sakon ya sake shigowa irin na dazu a karo na biyu, sai dai banbancin lokaci. Amaani ta kira suna zaune suna cin snacks da juice, ta bata wayar tace ta kaiwa Mamma. Sai ta kifa kanta tana jin nauyin Mamma. Tana jin sanda Mamman tazo kanta, tana sababi

 

"Yanzu haka ake gaya miki anayi Iman? Mijinki yana kiranki tun dazu kika yi shiru. Kunyar me? Zamani ya chanja kinji? Tashi maza ki gyara jikin ki, ga masu kula dake nan da yawa daya sai ta rakaki, tashi maza kina kara bata lokaci."

 

Tashi tayi kunya na nukurkusar ta,ta dinga sunne kai taki yarda su hada ido da Mamman, tana kallon ta, ta fito mata da wasu kayan tace ta sauya, sannan ta kawo mata wani abu a cup da madara ta bata ta shanye, ta faffesa mata turarurruka masu kamshi sannan suka fito in da yan matan ke zaune, da sauri suka tashi su biyu, suka sakata a tsakiya suka nufin bangaren Moh din da yake da dan tazara da wanda aka sauke su.

   Babu kowa a kofar, kai tsaye ta shiga su kuma suka samu waje daga wajen suna jiran ta dan tace musu ba jimawa zatayi ba, babu kowa a falon babu motsin komai, dakin farko ta bud'e da sallamar ta, baya ciki, sallama take amma ba da karfi sosai ba, a tunanin ta ko ya shiga toilet ta zauna jiran shi, shiru shiru babu alamar sa, ta kasa kunne ko zata ji karar ruwa a toilet sai taji kamar shesshekar kuka, sake kasa kunnen tayi sosai ta tabbatar da abinda taji, sai ta fara tunanin aina take ji, dakin da yake karshen falon ta kalla, babu alamun haske a ciki amma kuma tabbas da ga nan ne sound din yake fitowa. Tashi tayi ta nufi dakin tana taraddadin abinda zata tarar. A hankali ta tura kofar, ta leka da kanta kafin ta shiga da jikin ta gaba daya, tana gama shiga wutar dakin ta kawo, kwakwalwarta ta dauke kamar yadda ake dauke wutar nepa, idanun ta suka sauka akan Moh yayi ruf da ciki a saman gado yana bacci cikin kwanciyar hankali, boxer ne kawai ajikin sa dgaa shi babu komai. Da sauri ta maida kallon ta kan matar dake zaune a kasan tiles din dakin, kanta babu dankwali gashin kan nata da ya hargitse ya barbazu har zuwa saman fuskar ta, shigar jikin ta kawai ta kalla tayi saurin dauke kanta tana kokarin barin dakin, sai dai bata kai ga barin wajen ba dan ko taku biyu batayi ba, taji sanarwa shigowar Maimartaba, bayan sanarwa ne taji shigowar sa.

   Karuwar kukan Laila ya sake sakata cikin yanayin da ta shiga, har Maimartaba ya karaso bakin dakin tana tsaye kamar an dasa ta, bata san me zatayi ba. kallon ta yayi kafin ya maida kallon sa cikin dakin, yayi musu kallo daya wani abu me dacin gaske yana tokare shi a goshi. Juyawa yayi sai a lokacin kwakwalwarta ta kai mata sakon waye wanda ya shigo din, da sauri ta zube a wajen ta gaishe shi cikin muryar ta da take rawa sosai.

   Be amsa mata ba, sai daga mata kai da yayi ya juya ya fice yan rakiyar sa suka bi bayan sa cikin tunanin dalilin zuwan Bubun shashen Moh.

    Kasa daga kafarta tayi daga wajen, ta jingina da bangon dakin tana karanto duk addu'ar da tazo bakin ta, ji tayi kamar ana mata magana, ta dago tana kallon cikin dakin

 

"Amarya! Kinyi farin gani ko?"

 

Me zata ce? Shiru tayi tana maida idonta ta rufe shi ruf tana kokarin ajiye abinda ta gani din da kuma abinda zuciyar ta take haska mata waje daya.

 

"Anya? Anya kuwa? Muhammad? Me ya faru? Me yake shirin faruwa? Wacece wannan din?"

 

"Karki wahalar da kanki tunanin wacece ni, sunana Laila, gimbiya Lailah."

 

Yawu me karfi ta hadiye, ta hau kokarin daidaita kanta waje daya, shigowa taji an sake yi, ta daga idonta da sauri wannan karon wata babbar mata ce ta shigo a hargitse, tayi saurin yin kan wadda ta kira sunan ta da Laila tana rik'e ta, tana kallon yadda Lailan ta cigaba da rusa kuka kamar Allah ya Aiko ta, matar na bata baki jikin ta na rawa sosai. Daga ta tayi da sauri, ta yafa mata mayafi ta rik'e hannun ta, suka zo daidai in da Iman din take tsaye, matar tayi mata wani mugun kallo, ita kuma Laila tayi mata murmushin da ta tsaya mata a rai. Fita sukayi tayi saurin zuwa ta sakawa kofar key, ta dawo ta durkusa a k'asan falon ta shiga kuka, kukan da take ta kokarin rikewa dan bata son su ga weakness dinta, dama chan ita mutum ce me taurin zuciya da wuya kaga weakness dinta, shiyasa yanzun ma ta daure har suka fita.

   Sai da tayi kuka sosai sannan ta tashi ta share hawayenta, a kalla zata so taji ta bakin shi, kar ta yi judging dinsa da abinda ko a musulunci babu hujja, dan bata gansu suna aikata wani abu mara kyau ba. Duk da ta na kokarin karfafa jikinta da zuciyar ta akan ta bari taji komai, amma kuma jiki da zuciyar ta ta sunyi sanyi, sanyin da take jin kamar komai ya kare mata, kasan zuciyar ta tana jin zafin sa, tana jin haushin sa amma kuma bata da damar yanke masa hukunci.

   A yan awannin da tayi a cikin gidan nasu ta fuskanci akwai wani Babban al'amari da ya shafi Moh dinta. Tana jin kamar gadar zare aka hada masa har ma da ita. A nutse take duk da abin ya kadata, dan babu matar da zata ga wata mace a dakin mijinta cikin yanayin da taga Laila ba tare da taji komai ba, sai dai ta yarda da addu'a dan haka ta dage sosai har ta soma jin nutsuwa na saukar mata.

   Bata san dadewar da tayi a wajen ba, taji kamar motsi a dakin, ta tashi ta dubo cikin rashin sa'a ta cire takalmin ta, ta taka glass din da yake fashe a wajen, kara tayi hakan ya farkar da Moh gaba daya, ya mike da sauri kansa yayi wani irin sarawa da be taba jin irin sa ba, jiri yaji yana neman kayar dashi yayi saurin komawa ya zauna yana dafe kan, bayan kamar sakan goma ya mike a hankali ya fito.

   A durkushe ya ganta tana rik'e kafarta da har ta fara jini, da sauri ya karaso ya durkusa a gabanta yana kama kafar

 

"Me ya same ki? Me kika taka."

 

Kokarin janye kafarta tayi, ya sake kama kafar ya rik'e yana kallon kafar cikin tausayawa.

 

"Cika min kafata."

 

Tace ba tare da tasan me yasa ba, kawai ganin sa ya sakata jin haushin sa. Kin cika mata kafar yayi, sai ma daukar ta da yayi gaba daya duk da yadda yake jin sa babu kwari, ya ajiye a gefen gadon ya dauko first aid box din sa yazo ya durkusa a gabanta ya gyara mata kafar Allah ya taimaka kwalbar bata shige ba.

 

"Yaushe kika zo nan? Ya akayi nayi bacci? Me ya faru aina aka samu kwalba a wajen nan har kika taka? Ina masu kula da wajen?"

 

Ya jero mata tambayoyin cikin son tuna wani abu, da Ido kawai yake bin sa kamar me son karantar sa, sai dai bata ga komai ba sai tsantar gaskiyar sa a yadda yake maganar. Janye kafarta tayi ta mikar da ita a saman gadon, ya dawo ssman gadon ya zauna yana jan kafar ya dora akan cinyar sa.

 

"Bacci ne ya dauke ni bayan na sha juice daga nan kuma bansan me ya faru ba, kin dade kina jirana? Da baki tashe ni ba?"

 

"Bana so na katse maka barci ne." Tace ganin duk ya damu, ajiyar zuciya ya sauke yana matsowa ya gyara mata kafar yadda zata ji dadi, ya mannu a jikinta.

 

" Kiyi hakuri, kaina ne naji yana min ciwo sosai shine kawai nazo na dan huta bansan zanyi bacci ba."

 

" Ba komai."

 

Tace tana rufe idon ta

 

" Bacci?"

 

" Umm."

 

Tace a gajarce dan bata son doguwar magana tana son tattara bayanan da ta samu ta hade su waje daya kafin wayewar gari.

 

Tashi yayi ya fita bayan ya maida rigar sa,  ya hau k'wala kiran ma'aikatan wajen, da sauri ya shigo yana raba ido, masifa ya fara yi masa akan dalilin barin kwalba a hanya, hakuri yayi ta bashi yayi saurin gyara wajen sannan ya fita.

   Ji yayi duk jikin sa yana masa ciwo, chan k'asan zuciyar sa kuma wani irin feeling ne da be san dalili ba, ji yake kamar idan har be samu abinda yake so ba zai iya rasa ransa, yana wanka yana tunani har ya kammala ya fito daure da towel iya ka guiwar sa, kallon in da take kwance yayi, ta dunkule waje daya kamar me jin sanyi.

   Kaya ya saka sannan yayi sallah ya duba wayar sa yaga misscalls da yawa, ganin dare yayi ya saka shi ajiye wayar ya hawo gadon yana juyo da ita tana kallon shi. Hawaye ya gani a saman kuncin ta, ya saka hannu cikin mamaki yace

 

"Kuka?"

 

Kamar wadda take jiran kiris ta shiga rera shi sai dai babu sauti, rikicewa yayi ya hau tambayar ta menene, bata amsa masa ba, ta cigaba da kukan ta wanda ita kanta bata san me yake sake tunzura ta take kukan ba, da farko ta zata zata iya daurewa sai daga baya ta gane duk dauriyar ta wannan ya wuce in da take tunani, kishin mijinta ne ya sakata kuka. Magiya ya cigaba da yi mata akan ta fad'a masa dalilin kukan ta amma taki, rungume ta yayi a jikinsa yana lallashin ta amma kamar kara ingizata yake, ya rasa yadda zai, ga wani irin abu da yake jin yana taso masa. Kasa daurewa yayi ya hade bakin su waje daya, da karfi tayi kokarin turashi ta amma ta kasa!

 

 

 

Rano💕

 

*_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*

 

*_NANA HAFSAT(MISS XOXO)  s_*

_SO DA ZUCIYA_

 

*_SAFIYYA HUGUMA_*

_DABI'AR ZUCIYA_

 

*_MAMUH GEE_*

_DEEN MARSHALL_

 

*_HAFSAT RANO_*

_HALIN GIRMA_

 

*_BILLYN ABDULL_*

_TAKUN SAKA_

 

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇

D’aya 300

Biyu 400

Uku 500

Hudu 700

Biyar 1k

 

*_Zaku tura kudin a_*

 

6019473875

*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*

*keystone bank*

 

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

 

08184017082

 

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

 

09134848107

 

 

1/31/22, 19:15 - Buhainat: Halin Girma

      23

 

*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_*

https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share

 

*_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_*

https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb

 

*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_*

https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS

 

*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_*

https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw

 

*******

A hankali ya shiga bin ko ina na jikinta yana aika mata da sakonnin shi, kukan da take na taba shi, yana jin har cikin kansa, sai dai ba zai iya controlling kansa ba, abinda yake ji yafi karfin ikon sa, ba kuma zai iya tsere masa ba.

   Da fari ta dauka babu wani abu da zai mata sai son ganin ya rarrashe ta, amma daga baya sai taga abin yana chanja salo. Jikinta ne ya hau rawa ta ko ina, ta sauya akalar kukan nata zuwa magiya da rokon sa, baya jin ta, idan ma yaji ta baya tunanin zai iya yi mata abinda take so din.

   Juyo ta yayi ta zama a saman sa, ya sake hautsina ta zuwa kasansa , ya ajiye mata dukkan karfin sa, ji tayi kamar numfashin ta na janye wa daga jikin ta, ta dinga jansa tana kuka tana kiran sunan sa, yadda yake kissing dinta kamar mayaunwacin zaki ya sake tsorata ta,shi kansa jikin sa rawa yake,ga wani karfi da yake ji ya zo masa wanda be taba jin irin shi ba. Kayan jikin ta ya shiga janyewa yana wurgi dasu ta kowanne angle, har yayi nasarar rabata da komai. Idanun sa da suka rine sosai ya zuba mata yana kallon ta, wani abu yana kaiwa da komowa a tsakanin wuyansa.

 

"I'm so sorry."

 

Ya furta mata da k'yar kafin ya shiga aiwatar da abinda yayi niyya.

 

   Sama sama yake jin ta, cikin muryar da ta shige ciki saboda kukan da ta sha,  kamar mafarki haka yake jin abun, juyowa yayi da k'yar ya dune ta, tana kwance agefen sa taci kuka har ta gode Allah.

 

"Subhanallah!"

 

Ya furta yana tashi, abinda ya faru ya shiga dawo masa akai, ya akayi haka? Bayan yayi ma kansa alkawarin zama so gentle, yadda yasan ba zai bata wahala sosai ba, what has gotten in to him? Me yayi mata?

  Rik'e ta yayi yana kokarin daidaita kansa ya samu damar kwantar mata da hankali

 

"I'm so sorry dan Allah, dan Allah kiyi hakuri ki yafe min, bansan me ya hau kai na ba, this is not me, bani bane ba."

 

Bata da karfin da zata kwaci kanta, sai kawai ta lafe a jikin sa tana jan numfashi. Kanta ya dinga shafawa a hankali a hankali, yana jin wani irin son ta, na saka shigar sa. Idan har abinda kwakwalwar sa ta dawo mata dashi gaskiya ne, toh lallai sai yaci uban Lailah, dole ne yayi mata abinda ko a hanya ta hadu dashi ba zata nuna ta sanshi ba.

  Idonsa a rufe yana tariyo abinda ya faru, tabbas ya ganta a tsaye a kansa, lokacin da baccin da be san na menene ba dauke shi da sauri. Tunanin sa ne ya koma baya, zuwa sanda ya shigo ya tarar da juice akan table din da ake ajiye masa, a gajiya yace amma ya tsaya ya sha daga nan ne ya fara jin wani abu me karfin gask yana taso masa, sai wani irin bacci me nauyi da be taba jin irin sa ba.

 

"Desire pills?"

 

Ya furta yana kokarin tashi, k'ara tayi mara sauti ya tuna tana jikin shi, yayi saurin komawa ya zauna yana sake gyara ta.

 

" I'm sorry."

 

Ya saka hannu ya goge mata hawayen da suke sauka a fuskar ta. Tsawon minti talatin yana a haka yana tunanin abubuwan da suka faru a daren, tabbas koma menene an shirya masa abu ne, be san ya akayi ya bada kafa ba, har aka yi galaba akansa. Tashi yayi bayan ya gyara mata kwanciya, ya shiga toilet ya gyara jikin sa, sannan ya fito, ya taimaka mata, ta tashi tana ciccijewa sai dai taki yarda su hada ido, ta hade fuska sosai a dole haushin sa take ji, haushi biyu ne suka hadu waje daya, ta kasa manta abinda ya faru farko da na karshen.

  Toilet din ta shiga sai taga ya biyo ta, ta dube shi tana tsaye gaban bathtub din, ta marairaice fuska, yi yayi kamar be ganta ba, ya rufe kofar ya karaso ya durkusa yana taba ruwan.

 

"Ka fita."

 

Ta fad'a muryar ta babu karfi, banza yayi kamar be ji ta ba, ya ciro towel a cikin jerin sabbin towels din dake jere a cikin wata drawer, sannan ya dauko brush da toothpaste ya saka mata a jiki ya ajiye a gefe ya hau nannade hannun rigar sa. Kamar ta rusa ihu haka taji, ta rasa yadda zatayi ta hanashi, bata ga alamar ma zai hanun ba, sai kawai ta hakura ta zubawa sarautar Allah ido, bata san rashin kunyar namiji ta kai haka ba. Sai da ya gama abinda yayi niyya ya tabbatar yayi mata yadda zata ji dadin  jikin ta sannan ya kyale ta ya fito yana jawo mata kofar.

   Kwanciya ta sake yi a cikin tub din ruwan na ratsa ta, gefe tana tuna abinda ya wakana tsakanin su. Murmushi tayi, duk kalaman sa na dawo mata daki daki, abu daya ne ya tsaya mata har take kokarin alakanta shi da abinda ya faru kafin nan, idan har shi din ba mutumin kirki bane, idan har wani abu ya faru tsakanin sa da Lailah, ba zai sha wahala wajen neman hanya ba.

   Saurin kawar da tunanin tayi kunyar kanta na kamata kamar yana wajen, da wanne idon zata koma wajensu Mamma ma wai tukunna, da wanne idon? Kwankwasa mata kofar yayi ganin ta dade, sai ta tashi tana karfafa jikin ta, ta dauro towel din bayan ta goge jikinta ta fito kanta a k'asa. Ajiyar zuciya taji ya sauke bayan ya kare mata kallo, hankalin sa yaki kwanciya tunanin sa ko yayi mata illa ne, sai yaga akasin haka, be sani ba ko duk cikin dauriyar da ya gane tana da ita bane. Lokacin sallah ake kira a cikin masallacin cikin Masarautar, daga jikin kofar ya tsaya be fita ba, yana kallon ta har ta gama ta saka doguwar jallabiyar sa daya ajiye mata a gefen gadon, murmushi yayi ya fice kansa sanye da farar hula da ake kira da tashi ka fiya naci ya dora doguwar riga irin wadda ya dauko mata.

   A sahun farko ya samu Kamal, daga liman sai shi, hakan ya bashi mamaki amma ya share, bayan an idar suka gaisa a tsattsaye ya fice yana son komawa ya ga halin da take ciki. Sun hadu da Bubu amma be masa magana ba, ya dai ce masa ya sameshi idan garin ya gama wayewa, sai dai yanayin fuskar Bubun ta saka shi tunanin akwai wani abu me girma.

   A saman sallayar ya tarar da ita, ta kwanta akan hannun ta ta mik'ar dashi, karasawa yayi ya daga ta, ya maida ta saman gadon yana zama a gefen ta. Rufe idon ta tayi da sauri jin ya matso da fuskar sa daidai saitin tata. Iska ya fitar me zafi, ya tashi ya kashe wutar dakin ta dawo ya hawo gadon ya kwanta.

 

"Me ya faru?"

 

Yayi mata tambayar kai tsaye, yadda yayi sounding zaka gane daga muryar sa, maganar yake so suyi, shiru tayi bata ce komai ba, dan bata san me zata ce ba, tace masa ta same shi da wata a daki ko me? Ta yaya ma zata fara?

 

"A lokacin da kika zo dakin part din nan, wani ya shigo? Ko kinga wani a ciki?"

 

Nan din ma shiru ta sake yi masa, kasan zuciyar ta na ce mata kar ta yarda,kawai zai yi amfani da innocent dinta ne ya nuna mata kamar be san komai, daga gefe kuma wata zuciyar na ce mata ta fad'a masa watakila be sani ba, watakila so ake a hada su, tunda har yanxu bata san komai akan sa ba, ba zata iya dorar da wani abu ba balle har ta iya judging dinsa, kawai dai a matsayin ta na mutum me tunani , tana kyautata masa zato.

   Birkitota yayi da karfi muryar sa na fita da dan karfi akan dazu yace

 

"Tell me, me ya faru? Wani abu ya faru? Kin samu wata ko wani da kika zo? Wani ya fad'a miki wani abu ne? Me ya faru!"

 

Kuka ta samu kanta da fashewa da, ya tashi da sauri yana kunna wutar dakin, ya dawo ya tashe ta zaune suna fuskantar juna, zuwa lokacin ya ji yana neman loosing temper dinshi.

 

"Kalle ni, look at me! Menene? Me ya faru da ban sanshi ba? Tell me, waye yazo?

 

" Maimartaba ne yazo."

 

" Maimartaba!?" Ya furta da dan karfi cikin yanayin dake nuna tsantsar mamakin sa

 

"Me yazo yi a part dina? Me yace? Me ya faru? Wani abu ne ya faru while i'm sleeping?"

 

" Eh." Ta daga masa kai, tsugunawa yayi a wajen yana tattaro dukkan nutsuwar sa, gabansa na faduwa da abinda zata ce dan yasan ba karamin abu bane zai kawo Bubu part din sa.

 

" Believe me, bansan komai ba, kamar yadda babu alkalami akan me bacci, na rantse miki bansan me ya faru ba."

 

Goge fuskar ta, tayi da hancin ta a jikin sa, ta dago tana kallon kasa tace

 

" Naga wata Laila a nan."

 

Ta nuna wajen da Lailan ta zauna

 

" Lailah!? "

 

"Eh."

 

"Ehen, sai me?"

 

"Tana zaune a wajen tana kuka sosai, daga nan sai Maimartaba ya shigo, sannan ya tafi sai kuma wata mata ta shigo ta daga ta suka fita

 

   Abu ya hadiye me karfi, ya yi kokarin ganin be yi wani abu ba, a hankali yaji kamar ana masa rad'a

 

_Be calm Moh, be calm."_

 

Kamar wanda aka saka abu aka bubbuge ma guiwa haka ya zube a wajen, zai tolerating komai amma banda fushin Bubu, shi za'a wa wannan kazafin? Abinda be taba tunani ko shaawar aikatawa ba, Zina? Shi Muhammad shi aka yiwa wannan sharrin? Saboda yayi kamar be san wani abu yana faruwa ba, shine har aka samu damar yi masa wannan kullin?

  Tana ankare da yadda ya shiga kaduwa, tana kuma ganin yadda Adam apple dinsa ke hawa da sauka tsakanin makogwaron sa, idon sa kadai zaka kalla ka tabbatar da ransa yayi masifar baci.

   Sai da yayi kusan minti goma be ce komai ba, ba dan bashi da abinda zai ce din ba, sai dan yadda mamakin Iman din ya hanashi komai, be zaci haka daga gareta ba, idan wata ce, ba zata iya daukar abinda ta gani ba, har ta tsaya jiran shi, ya ga kokarin ta sosai kuma ya jinjina mata, hakan ya kara mata matsayi a zuciyar sa.

  Girgiza mata kai yayi yana kama hannun ta

 

"Kin yarda dani?"

 

" I don't know." Tace tsakanin ta da Allah

 

"Bansan yadda zan dauki abun na ajiye ba, all I know shine I'm hurt, more than yadda nayi tunanin I ll be."

 

Folding hannun nata yayi a cikin nasa ya damke.

 

"I promise to make everything right, koma menene we will over come it, in sha Allah, together we will build tomorrow, I promise you that!"

 

Shiru sukayi babu wanda ya sake magana, ko be ce ba, ko be ba ita zata gano komai, zata gane kafin ma ya gane, tana da kaifin tunani, sannan tana karantar komai kafin tayi judging din mutum.

   Kwanciya tayi ganin suna zaune kowa da abinda yake tunani, ganin ta kwanta sai ya mike ya fita, ya nufi part din Ammi duk da lokacin garin ke karasa yin haske. Ya san tana zaune har lokacin tana azkar kamar yadda ta saba a ko da yaushe.

   Yadda ta ganshi ya shigo jikin ta, ya bata babu lafiya, katse abinda take tayi ta mike tana kallon sa har ya karaso

 

"Lafiya Babana?"

 

"Ina kwana Ammi?" Ya duk'a k'asa ya gaishe ta, kafin ya amsa mata tambayar ta

 

"Ba lafiya ba Ammi, yarinyar nan Laila tayi abinda zan nuna mata ko ni waye, ganin kamar ban san me take ba ya bata damar aikata abinda ta aikata wanda zai zame mata dana sani, dama chan Ammi kece kike hanani, saboda zumunci amma not anymore."

 

"Me ya faru?!"

 

"Bubu be sanar dake komai ba?"

 

"Be ba, me ya faru?"

 

Iyakar abinda ya sani ya sanar da ita, jikinta yayi sanyi, ta kuma san Bubu zai iya daukar kowanne mataki akan muhammad din, tun da be taba sanin wani abu daya danganci Laila din ba da shi, ita kawai da Muhamamd din ne suka sani sai Kilishi.

 

"Babu abinda zai faru, kai dai ka rike gaskiya, zatayi halin ta."

 

"Shikenan, zanje naga Bubu, zanji me zaice."

 

"Allah ya taimaka, zanyi magana dashi nima in sha Allah."

 

Fita yayi ita kuma ta zauna a wajen tana hango abinda zai je ya dawo.

 

Kasancewar safiya ce, shiyasa ya shige kai tsaye wajen Bubun, a lokacin ya fito wajen shashen bayan sallah yana duba wasu littattafan sa. Sai dai yau ya kasa yin komai, tunda aka fito masa da littafan ya kasa taba ko guda daya, balle har ya karanta, abinda ya gani jiya yayi masifar girgiza shi, ya kada shi sosai, har yayi furucin da yake jin idan har Muhammad be wanke kansa a tsawon kwanaki biyar ba, ko da yana da gaskiya ya zama dole ya auri Lailah tun kafin maganar ta fito waje, a jita a ko ina.

    Aji ya samu da maganar a lokacin dan ji yayi yana neman faduwa k'asa, sai dai yadda yayi tunanin maganar zata taba Aji sai yaga akasin haka, yana zaune kem fuskar sa bata chanja ba ko kad'an, har sai da Bubun ya kasa daurewa ya tambayi Aji dalilin da be ji abun ba, murmushi yayi yace.

 

"Ahmadu kenan, da Muhammad da Laila su dukkan su nawa ne, ni na haifi iyayensu na kuma san kowa a cikin su, na san abinda kowa zai aikata da wanda ba zai aikata ba, duk da yanzu ance baa shaidar mutum, amma ni zan shaidi Muhamamd ko aina ne, lallai akwai wani al'amari bayan abinda kai din ka gani."

 

"Amma kuma komai ya nuna, a yadda na ganshi naga Lailan, bani da hujjar kare shi ko yarda dashi, idan har nayi haka sai naga kamar banyi wa Yaya adalci ba, mutane zasu ce ko dan babu shi. "

 

" Duk abinda zakayi karka tuna mutane dan dama su baa raba su da abin fad'a, kayi gaskiya kawai. "

 

" Toh ta yaya zan yarda da Muhamamd be aikata ba? Da wacce hujja zan yarda dashi? "

 

" Ka bashi lokaci, ya kare kansa, idan har ya amsa laifin sa shikenan, idan kuma ya kawo hujja gamsasshiya toh."

 

" Idan har muhammad ya kasa kawo hujjar bai aikata abinda ni da mahaifiyar Laila muke tunanin ya aikata ba, nayi alkawarin aura masa ita a tsakanin kwanaki hudu! "

 

  Dawowa yayi daga tunanin yadda suka kwashe da Aji yayi, ya bata rai sosai sanda Moh ya dire a gabansa, cikin girmamawa ya gaishe shi, amma sai yaki amsawa, ya kausasa murya yace

 

" Ban kiraka nan dan ka gaishe ni na amsa ba, ban kuma kiraka nan dan muyi doguwar magana ba, me ya faru tsakanin ka da Lailah? "

 

" Babu komai Bubu. " Yace kai tsaye dan dama ya riga ya shiryawa tambayar

 

" Babu komai? "

 

" Eh babu, duk abinda ka gani sharri ne, bansan komai akai ba. "

 

" Waye shaidar ka? "

 

" ALLAH! "

 

Ya fad'a kai tsaye, shiru Bubu yayi, ya dauki wani lokaci kafin yace

 

" Ka dauki alaka ta da kai ta d'a da mahaifi ka ajiye a gefe, ka kalle ni a matsayin alkali da aka kawo min kara ka, na baka nan da kwana hudu ka kawo min kwakkwarar hujja, idan har kwana hudu ya wuce babu komai, nayi maka alkawarin aura maka Laila! "

 

" Aure?!!! "

 

" Aure, tashi ka bani waje."

 

Jikin sa a sanyaye ya tashi, ya fice cikin sauri sauri ya nufi part din Lailan, yana tafiya yana huci, ji yake kamar ya dauko bindiga ya harbe ta, mutanen da suka fara fitowa wanda suka kasance masu aikace aikace a tsakanin parts din suka hau mamakin ganin Moh a irin lokacin shi kadai babu wani tare dashi. Be same ta a bangaren nata ba, tana bangaren Kilishi,juyawa yayi zuwa bangaren Kilishi yana ayyana kalar rashin mutuncin da zai yi musu.

     Sai da ya kusa zuwa sai kuma zuciyar sa tace yaje yayi musu me? Yafi karfin haka, ba girman sa bane, dan haka sai kawai ya koma nasa part din yana lissafin kwanaki hudun da Bubu yace, yasan zai iya yin komai ba kuma sai karya alkawarin sa ba, idan kwanakin suka cika bashi da wata hujja. Abu na karshe da zai iya shine auren Lailah, gwara ya hakura da komai akan ya aure ta.

    Bacci ya sameta tanayi, baccin da yasan na wahala ne, duk tausayin ta ya kamashi, shi da yaso ta huta sosai kafin ta fara sanin komai amma sai gashi daga shigowar ta gidan ta fara da karo da abinda yafi komai muni. Peacefully take baccin,fiye da wanda tayi jiya, a kalla yanzu ta samu kwanciyar hankali bayan ta sanar masa da abinda yake damun ta, yasan tayi dauriya sosai.

   Kissing goshin ta yayi, ya gyara mata kwanciyar ya koma dayan side din ya kwanta da tunanin kwana hudu

 

Rano

 

*_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*

 

*_NANA HAFSAT(MISS XOXO)  s_*

_SO DA ZUCIYA_

 

*_SAFIYYA HUGUMA_*

_DABI'AR ZUCIYA_

 

*_MAMUH GEE_*

_DEEN MARSHALL_

 

*_HAFSAT RANO_*

_HALIN GIRMA_

 

*_BILLYN ABDULL_*

_TAKUN SAKA_

 

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇

D’aya 300

Biyu 400

Uku 500

Hudu 700

Biyar 1k

 

*_Zaku tura kudin a_*

 

6019473875

*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*

*keystone bank*

 

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

 

08184017082

 

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

 

09134848107

2/1/22, 10:25 - Buhainat: Halin Girma

      24

 

*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_*

https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share

 

*_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_*

https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb

 

*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_*

https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS

 

*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_*

https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw

 

Sai da rana ta daga sosai sannan ta farka, da sauri ta mike tana mamakin dadewar da tayi tana bacci ita da ya kamata ta koma wajen su Mamma. Sakkowa tayi tana jin jikin ta da dama-dama, ta shiga takawa a hankali zuwa toilet din dakin,ta wanko fuskar ta, ta fito ta gyarata sannan ta cire jallabiyar tasa ta maida kayan ta, ta ajiye masa a gefen gadon ta fito zuwa falon. Tunanin yadda zata iya komawa wajen su Mamma take da kuma yadda zatayi da kunyar da take ji daga zuwa ta dawo sai kwana bayan ba haka ya kamata ba a ganinta. Abin takaicin ma bata dauko wayar ta ba balle ta kira, tana tsaye tana tunanin yadda zata fita taji maganganu a kofar part din,wajen window ta isa, ta daga curtains din tana son ganin komai. Gabanta ne ya fadi, tayi saurin cika window din a daidai lokacin da taji suna karasa maganar su. Kyakkyawa ce ajin farko, kana ganin ta kaga bafulatanar adamawa, yau ba kamar jiya da ta soma ganin ta ba, tana cikin shiga me kyau harda Alkyabba, tayi kyau fuskar ta fes alamun tana cikin farin ciki. Kokarin daidaita kanta tayi sanda taji an turo kofar an shigo, idonsu ya hadu lokaci daya, wani banzan kallo Lailan ta watsa mata tana karaso wa ciki a gadarance, ta samu saman daya daga cikin kujerun falon ta hakimce baiwar ta,ta gyara mata k'asan rigar sannan tace ta fita ta basu wuri. Tana fita ta kalli Iman irin kallon sama da k'asa kafin tace

 

"Barka da rana amaryarmu."

 

"Sannu." Kawai Iman din tace ta juya zata bar wajen amma sai ta dakatar da ita

 

"Nace ba, ya kika ji da kwanan bakin ciki? A ranar farkon ki a dakin mijinki?"

 

"Bakin ciki kuma? Na me kenan?" Ta tambaya Kai tsaye kamar bata gane me Lailan take nufi ba

 

"Na abinda kika gani mana, bakin gani, kinga true color din so called mijinki ko?."

 

" Ohh, wannan wasan kwaikwayon wai? Yayi kyau sosai ya kuma tsaru yadda ya kamata, sai dai shi actor din be san kan wasan ba dan be ma san me yake faruwa ba, shine kawai matsalar film din amma yayi kyau."

 

"Me kike nufi?" Tace a hasale tana mikewa tsaye

 

" Abinda kika sani shi nake nufi, kin dauka zan yarda da banzan plan dinki? I'm not an illiterate, I can tell when someone is lying, beside mijina ba zai taba aikata abinda kika ikirarin ya aikata, and i trust him yadda bakya tunani."

 

"Wow! Wow!! Wow!!! Sannu da kokari, I love your confidence, amma wanne irin sani kikayi masa haka? Da har zaki bashi irin wannan yardar? Kinsan waye namiji kuwa?"

 

" It doesn't matter yaushe na sanshi, all that matters now shine, miji na ne, kuma nayi trusting nashi, dari bisa dari."

 

" Shikenan, sai muga yadda zakiyi depending mijin naki at this critical condition, let's see how far you can go...."

 

" Kwana hudu kachal kike da, idan har baki samu way out ba. Ki shirya karba ta a matsayin kishiyar ki, sannan na fitar dake ta karfin gaske, dan baki da waje a gidan nan, captain nawa ne right from the start kuma he will always be mine."

 

Murmushi Iman tayi mata, tana jin wani irin tsana da haushin Lailan, tana jin zata iya komai, idan tace komai tana nufin komai domin taga ta fitar da shi daga koma menene, akwai babban kalubale a gabanta, amma ba zata karaya ba, duk wanda ya rik'e Allah da addu'a ya gama, da ikon Allah sai tayi galaba akan duk wani makiyin su. Ta daina shiru, duk wanda yace mata kule! Zata ce masa chas! Ita kanta bata san tana da courage din da zata iya maida mata martani ba, sai gashi.

 

Juyawa tayi ta koma bedroom din dan ba zata cigaba da bata lokaci akan wadda bata tunanin tana da hankali ko kad'an. Wayarta ta gani ajiye a saman chest of drawers ta dauka ta kira Mamma da k'yar, sukayi magana ta ajiye ta zauna tana lissafin rayuwar da zatayi a irin wannan gida, tuna sanda ake mata fad'a irin na bankwana tayi, wata Babar su Abba tana ta jaddada mata hakuri da kuma shirya wa duk wani kalubale na gidan sarauta, karta bari a takata kar kuma ta cuci kowa, akwai makirci sosai wanda zata gamu dashi amma idan ta nutsu tayi hakuri da karfin addu'a Allah zai bud'e mata komai.

   Bata jima a zaune ba taji ana mata knocking, ta tashi ta bud'e ta fito, russunawa tayi har k'asa da sauri ta gaishe ta, kunya ta kama Iman din ganin Matar da zata yi kusan sa'ar Mama tana gaishe ta a haka. Kaya ta mika mata cikin girmamawa tace ta chanja zata rakata bangaren Fulani (Ammi) juyawa tayi ciki, dan dama kayan jikin ta sun dame ta sosai. Sai da ta shirya tsaf  sannan ta fito, ta lura Laila ta jima da barin falon sai dai mayen kamshin da take yana nan a falon. Kai tsaye shashen Ammi suka wuce wanda sai a sannan ne ta sake karewa fadar gani sosai. Anan suka tarar da su Mamma da wasu mutanen wanda da yawan su kana kallo zaka gane alakar su da gidan saboda yanayi na kama da suke da juna. Shigowar su ya saka kowa maida hankali kanta kowa na son ganin amarya, tunda jiya babu wanda ya samu ganin ta saboda dare. Kanta a k'asa taki yarda ta dago saboda yadda take jin kamar ta nutse, a tunanin ta duk sun san daga in da ta taho, bata san Mamma bata fad'a ba sun dai barshi a zuwan sun barota ne tana shiryawa. Sai da duk suka lafa ne aka zazzauna sannan ta gaida Mamma da take kallon ta da murmushi, murmushin da ita kadai ta san ma'anar sa, hakan ya sake saka Iman din cikin jin kunya.

  Sanda ta shigo Ammi bata falon, tana zaune suna magana da Amaani ta dawo, da sauri Iman din ta zamo daga kujerar ta gaishe ta, ta rik'e ta, ta mik'ar da ita tsaye tana amsawa a sake sosai, sannan ta saka a raka Iman din part din Kilishi.

   Hannun ta cikin na Amaani suka shiga, babu kowa a falon farko sai wata baiwa guda tana goge-goge,wadda ta rako su ce tace su zauna sannan ta nufi kofar ciki don sanar da zuwan su. Jim kad'an ta dawo ta tsaya a gefe, zuwa wani lokaci Kilishin ta fito, fuskar ta kadaran kadahan ba zaka gane komai ba, Iman bata kalle ta ba, ta gaishe ta cikin girmamawa ta amsa a yatsine bata ma zauna ba.

 

"Hari wannan din itace sirikar tamu?"

 

"Itace ranki ya dade."

 

"Lallai sannu yarinya, shi ko Muhammad ya rasa wa zai dauko mana sai yar karamar yarinya haka? Ko da yake ra'ayin sa ne ai, ba kuma a san ya akayi ba dai, ko da yake dama dai yaran talakawa sai a hankali, idon su idon me arziki sai in da karfin su ya kare, sannu kinji? Allah ya bada zaman lafiya."

 

Sai ta juya

 

" Hari naga amarya, ki gaida uwar dakin naki."

 

Wani abu ne ya tokare wa Iman a makogwaro, idan har ta fahimci maganganun matar tana nufin asiri tayi ta aure shi kenan, a fakaice ta ci mata mutunci babu gaira babu dalili, bayan bata san ta ba, idan banda jiya sai yau ne karo na biyu da ta taba ganin ta. Ajiye ta tayi a daidai mazaunin da da ajiye Laila, ta kuma kuduri aniyar zama dasu daidai da yadda suka zaba.

  Daga nan sai suka wuce bangaren Aji da Hajja, amma a mota saboda tazarar dake tsakanin bangarorn biyu, sosai taga karamci da girmamawa dan Adam, Hajja kamar ta goye ta saboda murna, ta dinga tsokanar ta da ta kwace mata miji da rana tsaka, murmushi kawai Iman din take, hakan ya janyo suka dade sosai a bangaren har zuwa sanda taji sallamar sa, ta dago suka hada ido sanda yake shigowa ciki, jamfa da wando ne a jikin sa kalar sararin samaniya, ya tsaya iya kar guiwar sa, kansa sanye da hula me kalar duhu, yayi kyau sosai, da sauri ta janye idon ta kunyar abinda ya faru daren jiya na hasko mata, murmushi yayi me kyau ya karaso ya zauna kujerar dake fuskantar ta. Hajja dake nade a saman wani cushion me laushi ta tabe baki tana dubanss

 

"Saboda rashin kunya shine ka biyo bayanta ko?"

 

"Toh ya zanyi? Kin rik'e min ita kin hanata tafiya."

 

"Ah lallai, shine ka biyo baya kazo kaga ni, toh ba zan cinye ta ba ai."

 

"Kai yar tsohuwar nan kin fiye rikici wallahi, kishi ne nasan yake damunki ba wani abu ba."

 

Dariya tayi tace

 

" Ai na bar mata kai tuntuni, kuje ku karata nima Amadu na ya ishen."

 

A tare duk suka yi dariya, ya kashe mata ido daya tayi saurin dauke kai kamar bata ganshi ba.

 

" My wife!"

 

Yayi kiranta a hankali karaf sai a kunnen Hajja, ta banka masa harara ya sosa kai

 

"Dan nema, kin hadu da aiki kinji Fatima, mijin nan naki bashi da kunya sam, bari kiga na tashi, taso yan mata muje na baki wani abu ki bar wadannan."

 

Tashi Amaani tayi tabi Hajjan, suna shigewa yayi saurin komawa kusa da ita.

 

"Ka ganka ko?"

 

"Me nayi?" Ya tsare ta da ido yana marairaice fuska

 

"Gashi nan ka kori Hajja."

 

"Rigimar tace kawai fa, mun saba irin haka da ita."

 

"Toh ka koma chan ka zauna."

 

" Wai kunya ta kike ji? Ko kunyar Hajja?"

 

" Both!" Tace tana kauda kanta

 

Murmushi yayi kawai

 

" Kinsan me? Bubu ya bani kwana hudu na kawo masa gamsasshiyar hujja, idan ban kawo masa ba, zai aura min Laila."

 

Sak tayi, duk da Laila ta riga ta fad'a mata amma ji daga bakin sa ya sakata shiga yanayi,

 

" Karki damu, hakan ba zai faru ba, I promise you that!"

 

" Allah ya bada sa'a." Tace a sanyaye

 

" Zan je Abuja anjima ko gobe da safe zanyi kwana biyu, na dawo"

 

" Tafiyar ba zata bamu matsala ba?"

 

" In sha Allah."

 

" Shikenan, Allah ya kaimu ya dawo da kai lafiya."

 

Tayi shiru tana tunanin yadda zata taimaka masa ta taimaki kanta dan ba zata taba iya zama da Laila ba a yanayin ta.

 

***Idan tace tayi bacci a ranar tayi karya, tun bayan fitar matar gidan da kawayenta bata sake nutsuwa ba, kuka take tun tana yi da hawaye har ya zama babu hawayen sai suya da zuciyar ta, take kamar zata fito. Da asubar fari taji ana buga kofar dakin amma a hankali, tashi tayi da k'yar tana jin jiri jiri saboda yunwar da ta kwaso ta zare sakatar dakin. Da sauri ya shigo ciki ya maida kofar ya rufe yana kallon ta, matsawa tayi baya tana masa kallon tsana

 

"Karka matso nan wallahi zan iya illataka, ka maida ni gidan mu wallahi ba zan zauna anan ba."

 

"Rage muryar ki dan Allah, kar taji, kiyi hakuri zan yi kokari naga na lallabata ta bar mu, mu koma gidan mu dan wallahi a matse nake, kinsan dai mutum da sabuwar amarya."

 

"Wallahi bazan koma ko wanne gida ba, gidan mu zaka mayar dani ka sake ni kuma, ba zan zauna da kai ba na tsane ka."

 

Saurin damkota yayi, ya toshe mata baki yana hade jikin su waje daya

 

"Idan kina daga murya wallahi zamu dade a haka, idan ta gano na sato hanya nazo ni dake duk ba zamu fita ba, yanzu ki kwantar da hankalin ki, ki bita duk yadda tace zan dinga shigowa nan din da asubah tunda bata tashi da asubah sai gari yayi haske sosai."

 

Fizge kanta tayi tana masa mugun kallo

 

"Na tsane ka, na tsane ka Bashir har bansan iya adadin tsanar da nayi maka ba, Allah ya isa cutar dani da kayi, kasan dama kana da mata amma shine ka auro ni, wallahi sai ka sake ni ko na jawo maka abinda zaka dade kana dana sani."

 

"Baby!" Yaji muryar hajjajun tasa tana k'wala masa kira, jikin sa ne ya hau rawa yayi hanyar fita hankalin sa a tashe,kafin ya karasa ta turo kofar cikin shigar kayan bacci masu shegen kyau, tayi musu wani kallo kafin ta kama hannun sa tana murmushi

 

"Kana nan ashe, toh wuce muje ko?"

 

"Toh;" yace yana yin gaba.

 

"Ke kuma, ki fito ki fara min aiki kafin gari ya gama wayewa, akwai menu na kalolin abincin da nake son gani kullum a saman dining bana kuma so ki wuce karfe goma baki gama komai ba."

 

Ta juya tana karkada mata mazaunanta ta buga kofar. Hawayen bakin ciki ne suka sakko mata, ta share tana shiga dan kurkutaccen bandakin da ke gefen dakin ta dauro alwala da k'yar sboda yadda yake wani shegen wari ta shinfid'a dankwalin ta, tayi sallah akai sannan ta bi ta hanyar zuwa kitchen din dan ta tabbata idan har ta sake muguwar matar ta dawo bata fito ba zata iya nada mata shegen duka babu abinda ya dameta gashi babu me kwatar ta dan shi kansa Bashir din ba abakin komai yake ba.

  Menu din ta dauka tana kallo, babu abu daya daga cikin kalolin girke-girken guda biyar da ta iya a ciki, tasan dai tabbas Iman tana yi musu dukka a gida amma ita bata taba ko da sha'awar gwadawa ba, daga indomie sai tea sune kadai take yi, sai yar taliya ko macaroni shima ba kullum ba, duk wani girki me wahala kamar su tuwo da sauran su.

 

*_ZAFAFA BIYAR 2022🔥_*

 

*_NANA HAFSAT(MISS XOXO)  s_*

_SO DA ZUCIYA_

 

*_SAFIYYA HUGUMA_*

_DABI'AR ZUCIYA_

 

*_MAMUH GEE_*

_DEEN MARSHALL_

 

*_HAFSAT RANO_*

_HALIN GIRMA_

 

*_BILLYN ABDULL_*

_TAKUN SAKA_

 

*_Zaku biya kudin wainnan daddadan labaran Kamar haka_*👇👇

D’aya 300

Biyu 400

Uku 500

Hudu 700

Biyar 1k

 

*_Zaku tura kudin a_*

 

6019473875

*MUSAA ABDULLAHI SAFIYA*

*keystone bank*

 

*Sai shedar payment dinki a*👇👇👇

 

08184017082

 

*Kokuma katin waya na MTN anan*👇👇

 

09134848107

2/1/22, 10:25 - Buhainat: Halin Girma

      25

 

*_ZAFAFA BIYAR FACEBOOK LINK👇🏾_*

https://www.facebook.com/groups/494948898814888/?ref=share

 

*_ZAFAFA BIYAR INSTAGRAM LINK👇🏾_*

https://www.instagram.com/invites/contact/?i=u8e91axrluzc&utm_content=nj79azb

 

*_ZAFAFA BIYAR WATTPAD LINK👇🏾_*

https://www.wattpad.com/1178725798?utm_source=android&utm_medium=whatsapp&utm_content=share_published&wp_page=create_on_publish&wp_uname=ZAFAFABIYAR&wp_originator=Rf3bdM1DxoE6rtr%2FpmofDT2LwC%2FVfwSkcdyq99bn0JQs6Y4vrnr66bh9cxKlfOuPfF5VyLoSKGor57378NB4Zb%2FxLxcsULfA0VJvg4flaQvgAACdVin4LPGGN8XRDxBS

 

*_ZAFAFA BIYAR TELEGRAM LINK👇🏾_*

https://t.me/+SBu4brdnI29hSBfw

 

***Ta dade a kitchen din tana jujjuya yadda zata yi, gashi lokaci na tafiya dan har kusan bakwai ce zatayi, barin kitchen din tayi ta wuce ta fara gyara falon, duk da ba wani datti da yayi amma sai da ta sake share shi ta bubbuge kujerun ta tattare komai ta ajiye a gefe har da rigar baccin da ta gani a jikinta dazu. Daga nan ta sake komawa kitchen din kawai ta yanke shawarar tayi abinda zata iya, ta dauki indomie ta dafa da egg sannan ta dafa ruwan tea ta jera musu akan dinning din ta wuce dakin da yake a mazaunin nata da tunanin yadda zata samu waya ta kira gida, ko kuma ta samu hanyar da zata bar gidan dan bata ga alamar Bashir zai kyaleta ta sauki ba.

  Tana zaune tana sak'awa da warwarewa aka turo wata yarinya kiranta, kamar ba zata tashi ba, sai kuma ta mike tabi bayanta tana taraddadin abinda zata tarar. Matan jiya ne jere akan dinning din, sai uwar gayyar daga gefe ta hade rai sosai tana mata mugun kallo, tun kafin ta karaso ciki ta hau surfa mata ashar

 

"Saboda tsabar ke yar iska ce, abinda nace ki dafa daban abinda kika dafa daban ko? Zo nan."

 

Kin zuwa tayi, ta k'ame a wajen tana kallon su

 

"Ji yadda ta tsare mu da ido Hajiya Lay, amma dai yarinyar nan bata da kunya."

 

"Ku barta, bata san wacece Layuza ba, zan koya mata hankali."

 

Bud'e baki Zeenat din tayi, tace.

 

"Ke nake aure ne wai ko shi?"

 

"Kutmelec! Ni kike wa wannan tambayar?"

 

"Toh ai naga dai iyaye na Bashir suka aura min ko? Me yasa kike nuna kamar ni din me aiki ce a gareki, ni bansan ki ba, bansan wacece ke ba kawai zaki dinga nuna iko akaina "

 

"Lallai yarinya, kinyi babban kuskure da har zan fad'a ki mayar, toh dake da Bashir din duk a karkashi na kuke, kuma baki isa ki hada miji dani ba wallahi, kinyi kad'an ace kece kishiyata, dan haka yanzu baki da maraba da me aiki a gidan na, kuma dan ubanki dole kiyi duk abinda nace, na samu labarin komai da yadda auren ya kasance, shegen kwadayi da son zuciyar uwarki dake ya jawo miki, dan haka ki wuce ki yi abinda na saki kafin na taso na yi miki mugun dukan da zaki kasa tashi wallahi."

 

" Ai da kawai daidaita mata shegen bakin nan nata akayi gobe ba zata sake fad'a ki fad'a ba."

 

" Barta, zata gane kurenta."

 

Zumburo baki tayi, ta ki barin wajen ita a lallai basu isa ba, ganin haka ya saka Hajiya Layuza tasowa aikuwa tana ganin haka ta kwasa da gudu bata tsaya ba sai data kai dakin tayi saurin saka sakata tana maida numfashi.

 

***Tagumi Mama ta rafka, duniyar gaba daya ta daina mata dadi tun bayan da ta tabbatar da babu wani abu da zata iya dan Abba sai da ya sake jaddada mata akan duk wani abu da ya samu auren Zeenat toh ta tabbatar da mutuwar nata auren, ada taso suyi duk wacce zasuyi amma daga baya sai tayi wa kanta fad'a ta hakura ta zuba wa sarautar Allah ido, gashi ta kikkira wayar Zeenat din amma ko da yaushe bata shiga, takanas ta tura Habib ya je har kofar gidan amma sai ya tarar a rufe, abinda ya kara daga mata hankali kenan, ta saka Abba a gaba tana kuka dole ya dauki waya ya kira Bashir din, ya kuma yi mata handsfree dan taji. Maganar an je an ga gidan a rufe Abban yayi masa nan ya shaida masa ai suna family house dinsu sai sun danyi kwanaki zasu dawo gida haka al'adar gidan su take, addua Abban yayi musu daga nan ya kashe yana kallon Maman da tayi tsuru tana ji har suka gama.

 

"Kin dai ji ko? Ko kuma address din gidan nasu zan baki?"

 

"A ah." Tace a sanyaye tana mikewa. Cigaba da aikin gabansa yayi dan be ga dalilin da zai saka ta tada hankalin ta ba, bayan sun riga sun aurawa Bashir din basu da ikon bibiyar in da duk zai kaita.

 

***Zuwa yamma masarautar ta cika sosai, duk wanda Ammi ta gayyato sun hallara, yan mata ne kyawawa masu aji suka fi yawa sai manya tsirari wanda Ammi ta barsu sai ranar nadin dan kar ya zama an takure mutum, Ba'a dau lokaci aka shiga gabatar abinda ya tara su, saboda a ranar su Mamma suke so su wuce. Tsarin daban ne da duk wani taro da akayi na bikin, Muhammad da be niyyar attending ba, amma ganin abinda ya faru ya sakashi shiryawa cikin shigar da yasan zai burge Iman dinshi, wanda be san iya adadin yan matan da suka sake faller masa ba a ranar. Yana zaune kusa da ita daf ya dan karkace yana fuskantar ta, yana mata magana k'asa-kasa, tana jin sa sarai amma ta fuske dan ta gama gane shi so yake suyi abin da zata sha kunya dan taga kamar shi be san kunya ba sam. Daga nesa ba zaka gane yanayin da suke ciki ba, zaka dauka yanayin zaman nasa na mulki ne, sai ka matso sosai zaka gane kan abun. Shigar da Laila tayi a wajen ta kusan fin ta Iman din, babu laifi Allah ya hore mata kyau ba kad'an ba, dan sanda ta shigo wajen sai da gaban Iman ya fadi ganin uwar kwalliyar da taci kamar wata dawisu, kai tsaye wajensu ta nufo tana tafiya tana karkada kowanne lungu da sako na jikin ta, kamar bishiyar da iskar rani ke kadawa haka ta dinga karkada jikin ta har ta karaso wajen fuskar ta a washe ta matsa daidai saitin Capt Muhammad ta rankwafo tana nunawa camera man sign din ya dauke su.

  Da ido Muhammad yayi masa alamar idan ya dauki hoton sai dai wani bashi ba, sum-sum ya bar wajen hakan ya bata wa Laila rai tace

 

"Capt wanne irin wulakanci ne wannan?"

 

"Baby kinga waccar da ta shigo yanzu?" Yayi kamar be ji ba, ya matsa jikin Iman din yana nuna mata wata,

 

"Kanwar Ammi ce, itace Aunty Fatima."

 

"Ok wadda ka bani labarin ta ko!?"

 

"Yea ita."

 

"Allah sarki, she's nice."

 

"Sosai." Sai ya sake kai fuskar sa jikin ta sosai

 

"Baby perf din nan akwai kamshi, i just love it, yayi dadi."

 

"Thanks dear." Tace tana smiling

 

Bakin ciki ne ya tuke Laila, tayi saurin barin wajen kafin zuciyar ta, ta buga. Tana barin wajen sukayi wa juna murmushi.

 

A gajiye suka koma cikin gidan bayan an gama taron, su Mamma sun jima da tafiya dan haka part din Ammi aka maida ita, daga nan Ammi ta saka mutane da yawa suka yi mata rakiya zuwa nata part din da ta riga ta tare tun a jiya ba tare da Ammin ta sani ba, sai gobe za'a rakata wajen Bubu idan ta huta shi ma baya nan yau sai goben zai dawo.

   Masu kula da bangaren da duk wani abu da ya shafe ta Ammi ta nuna mata, suna isa kuwa suka shigar da kayan su dakunan su dake bayan part din suka shigo suka fara aikin gyara shashen, suka gama suka saka masa turaren wuta sannan aka jere musu abinciccika masu rai da lafiya. Sai da suka tabbatar babu wani abu da zata bukata sannan sukayi mata sallama suka tafi.

   A gajiye take sosai amma kuma dole tayi wanka dan sosai Mamma ta jaddada mata muhimmanci wanka da gyara jiki, cire kayan jikin ta tayi, ta zari towel daya ta daura ta nufi toilet din, wanka tayi ta hado da alwala ta fito tana sharce kanta. Wayarta ce tayi kara ta dauka tana dubawa, Mommy ce ke kiranta, tunda aka fara bikin basuyi magana ba, sai dai ta jisu da Mamma suna yi, zama tayi tana daga wayar dadi na cikata

 

"Mummy barka da dare."

 

"Iman... Kuna lafiya?"

 

"Lafiya lou mummy, dama yanzu nake so nazo na kira."

 

"Ko? Toh gashi na kira ni ai, ya sabon waje?"

 

"Alhamdulillah."

 

"Mamma ta sanar dani duk yadda abubuwan suka kasance, nasan kuma duk abinda ya kamata ki sani ta sanar dake, dan haka ita rayuwar aure yar hakuri ce, sannan duba da irin gidan da kika samu kanki, sai kinyi hakuri kin kuma zama me lura sosai."

 

"In Sha Allah mummy."

 

"Yawwa, ki kula sosai da mijinki da duk abinda kika san yana so, karki ga tarin ma'aikata ki sakar musu kula da mijinki, duk wani abu da ya danganci mijinki ki taske kiyi shine hanyar samun ladan ki, kuma hanyar aljannar ki."

 

" In Sha Allah Mummy, nagode sosai."

 

"Ki ajiye kunya ki kula da mijinki sosai, banda sanyin jiki da lalaci."

 

A kunyace tace

 

"Toh mummy."

 

Turo kofar akayi, yana sanye da 3quarter wando babu riga a jikin sa, saurin dauke kanta tayi tana amsawa mummy bayanin da tayi mata akan wasu magunguna da ta saka mata a bag dinta. Gabanta yazo ya tsaya k'yam yana karewa cinyoyin ta dake bayyane saboda kankantar towel din. Tsugunawa yayi a gabanta ya saka hannu ya shafa saman cinyar ta ta, tayi saurin janye su tana jan numfashi,

 

"Kina ji na Iman?" Mummy tace jin kamar attention dinta ya tafi wani wajen.

 

"Am.. am ina ji Mummy."

 

Ta amsa a firgice ganin ya kai hannu jikin towel din ya janye, da sauri ta saki wayar bayan ta danne power button din, ta mike tana rik'e towel din. Idonsa a shanye yake kallon ta

 

"Zanyi wanka."

 

Yace yana shigar da idonsa cikin nata, kasa matsawa tayi daga wajen, sai jan towel din take a dole sai ya sauka ya rufe bayanta. Bata taba jawowa zai shigo a lokacin ba, ta yi tunanin ma ya tafi, sai ganin shi tayi. Dariya ta bashi,yadda ta hakikance a dole sai ta saukar da towel din.

 

"Zanyi wanka." Ya sake maimaitawa yana folding hannun sa, kamar ta dora hannu a ka tayi ta kurma ihu ta shiga takawa zuwa toilet din tana cigaba da jan towel din. Ji tayi an rungume ta, ta baya ya dora kansa a saman kafadarta.

 

"Me kunya, kunyar me kike ji?"

 

"Ba komai."

 

"Shine kike ta jan towel din bayan halal dina ne, sai a barni na more kallon kayana ko?"

 

"Uhum".

 

" Emana. " Ya sake tura kansa wuyan nata sosai,yana jujjuya kan, hakan ya haifar mata da kasala, ta dinga kokarin zamewa amma ya hanata, a dole ta kyaleshi yayi budurin sa. Sai da ya tabbatar da tayi laushi sosai sannan ya jata zuwa toilet din. Mamakin rashin kunyar sa take, shi ko a jikin sa babu abinda ya dame shi, ita kuwa kamar ta shide idan ta kalleshi a hakan sa, da k'yar ta samu ya barta bayan ya kara tattabe ta, ta samu ta fito ta barshi a ciki, a gurguje ta shirya ta saka kaya ta tada sallah ko da ya fito tana sallah sai kawai ya shirya shima ya fita falo dan cikin sa ya fara kiran yunwa. Zaman jiranta ya dinga yi jin shiru bata fito ba ya leko ya kirata, dan baya so a kara kwana be bata labarin komai ba, a kalla hakan zai saka ta sake yarda dashi ta kuma taimaka masa dan ita kadai ce ta fara ganin Laila sanda ta shigo part din. Tsattsakurar abincin tayi tace ta goshi dan da gaske tsoro take ji, tsoron kar yace zai sake yi mata irin abinda yayi mata jiya, ba zata iya dauka ba, shiyasa tana gama ci ta sulale ta gudu ta kwanta ta kudundune a dole tayi bacci. Sai da ya gama komai sannan ya biyo ta dakin ya yaye abinda ta rufan yana shigewa jikinta.

Post a Comment for "HALIN GIRMA 21-25"