KWAI CIKIN KAYA BOOK TWO PAGE 60
*_ƘWAI CIKIN ƘAYA!!_*
Bilyn Abdull ce
Page 60
ASSALAMU ALAIKUM MASOYA MAKARANTA LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR... 🙋🏿♀️🙋🏿♀️INA KUKE NE? 🔊🔊KU MARMATSO, DOMIN ZAMAN JIRA YA KARE, HAZIKAN MARUBUTAN NAN DA SUKA HADA HAZAKA DA KAIFIN TUNANI SUN SAKE ZAGE DAMTSE SUN ZO MU DA WASU SABBIN SALON RUBUTUN SU, WADANDA ZASUWA’AZANTAR, SU NISHADANTAR, KANA SY DILMIYA KU A KOGIN KAUNA, BASU TSAYA ANAN BA SALON RUBUTUN SU YA SAKE ZUWA DA SABBIN TSARE TSARE NA DARUSSA DABAN DABAN, DA KUMA HANYOYIN GYARIN JIKI DA WAJE._
_KADA KU MANTA MARUBUTAN ZAFAFAN DAI SUNE WADANDA SUKA YO MUKU HAR KASHI BIYU A SHEKARAR 2020 DATA GABATA,: WUTSIYAR RAKUMI DA GUDU DA WAIWAYE NA BILYN ABDULL. 2-DAURIN BOYE DA ALKAWARIN ALLAH NA SAFIYYAH HUGUMA.3-BURI DAYA DA QAUNAR MU NA MAMUH GEE-4- SAUYIN KADDARA DA DAURIN GORO NA HAFSAT RANO. SAI 5-KAI MIN HALACCI DA IGIYAR ZATO NA MISS XOXO.._
_A WANNAN SABUWAR SHEKARAR TA 2021 MA HAZIKAN MARUBUTAN SUN SAKE DAWOWA DA WASU SABBIN DA’DADAN LITTATTAFAN NASU:_
_1_
_* SAFIYYAH HUGUMA* MARUBUCIYAR KUNDIN KADDARA DA ABADAN TAZO MUKU DA SABON LITTAFIN TA MAI SUNA: *(SIRADIN RAYUWA)💜*_
_2_
_*HAFSAT RANO* MARUBUCIYAR GUGUWAR SO DA RUHI DAYA, TA ZO DA SALON NATA LITTAFIN MAI SUNA: *(ABINDA KE CIKIN ZUCIYA..*)💘_
_3_
_* MAMUH GEE* MARUBUCIYAR TARAYYAH DA EZNAH, TAZO DA SABON ZUWA MAI SUNA: *(MIN QALB)❤️.*_
_4_
_*MISS XOXO* MARUBUCIYAR NAUFAL DA SAIFUL-ISLAM, TA YUNKURO DA WANI MAI SUNA: *(KIBIYAR AJALI)*💜_
_5_
_SAI MARUBUCIYA *BILLYN ABDUL* WADDA TAYO MUKU KWAI CIKIN KAYA, DA CIKI DA GASKIYA TA YINKURO DA WANI MAI TAKEN: *(YANKAN BAYA)*💝_
_RIGIJI GABJI DUKKAN WADANNAN LAGWADAR DADADAN LITTAFAN BIYAR ZASU ZO MUKU NE INSHA ALLAHU AKAN FARASHI MAI RAHUSA KAMAR HAKA;_
Duka BIYAR 5 zaku samesu akan garabasar naira 700 kacal,
Guda hudu 4 Kuma 500,
Guda uku 3 Kuma 450,
Guda biyu 2 Kuma 400,
Guda daya akan 300.
Ma'ana
Each one is 300
2 is 400
3 is 450
4 is 500
5 is 700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
ACCOUNT NO- *0812652655*
ACCOUNT NAME- *HAFSAT LAWAN GAMBO*
BANK NAME: *ACCESS BANK*
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
*+234 903 234 5899*
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
*09033181070*
Karku Bari ayi Babu ku domin wannnan salon na daban ne
SABUWAR SHEKARA
SABON SALO
TEAM#ZAFAFABIYAR🔥
Page 60
...............Umm-Anum na kuka tana dariya duk a lokaci ɗaya ta nuna tv'n da yatsanta manuniya, cikin wani ƙarfin zuciya ta ɗaga murya wajen faɗin, “Rana dubu ta ɓarawo, ɗaya tak ta mai kaya”.
A take ɗakin yay tsit, suka juya gaba ɗaya suna kallonta a wani irin yanayi mai wahalar fassara a fuskokinsu. Kowa ya gagara cewa komai sai kallonta kawai da suke. Ta share hawayen da suka gama wanke mata fuska tana kallon Ummah babba. “Mariya a kaini wajen baba”. Da ƙyar Ummah babba ta iya gyaɗa mata kai a hankali. Bata ƙara cewa komaiba ta gyara mayafin jallabiyar ta data naɗa tamkar yanda larabawan Saudia keyi, Batool ta ɗakko mata takalmanta zuwa gabanta, dafa Batool ɗin tayi ta saka dan ƙafarta ciwo take mata kaɗan-kaɗan, tun jiya bata gama saki ba har yanzun.
ta maida dubanta ga su Uncle Sulaiman dake tsaye tamkar sojoji, har yanzu babu wanda ya iya gaskata ruɗani da al'ajabin da idanunsu ke gani a zahiri da magiji. Hannayenta🙏🏻 ta haɗe waje guda tana ɗan murmushi, “Ku gafarceni, ganin Mahaifina a yanzu gareni yanada matuƙar muhimmanci”. Bata jira amsarsu ba ta raɓasu ta wuce abinta Batool da Anum da Nabeelah sukabi bayanta.
Da kallo suka bita tamkar wasu wawaye harta fice ita da zugarta. Ummah ƙarama da babba suma sukai yunƙurin bin bayansu. Uncle Sulaiman ne ya sauke nannauyar ajiyar zuciya, cikin sanyin jiki da rawar murya yace, “Hajiya Mariya a ina kuka samu Bilkisu? Tun tsahon wane lokaci kuma?”. Kanta ta girgiza masa tana share guntun hawayenta itama, “Bani da ikon amsa waɗan nan tambayoyin Alhaji Sulaiman, inaga mu bari har sai lokacin da Yayah taso hakan da kanta, na tabbata zatazo ta sameku har gida insha ALLAHU. Mun barku lafiya”. Ta ƙare maganar da kama hannun Ummah ƙarama suka fice suma.
“Uncle wacece ita ɗin wai?”. Shahudah da idanunta ke lullumshewa saboda hajijiyar da take gani ta tsananin tashin hankali ta faɗa tana dafe bango. Saurin ruƙota matar Uncle Sadiq tayi jikinta na rawa itama. “Shahudah!!” ta faɗa daɗan ƙarfi ganin jikin Shahudah ya fara saki alamar neman suma takeyi itama. Ruɗewa ɗakin ya ƙarayi, masu share hawaye suka ƙara ƙarfafa kukansu da sauti, yayinda wasu suke zubewa ƙasa daɓar tsabar shiga ruɗani da abinda ake nunawa har yanzu daga gidan tv.
__________________
STATION
_____________
Da taimakon Jawaad da Qaseem aka fita da Mom zuwa mota, Qaseem ya shiga baya ya riƙeta yana kuka da kiran sunanta da roƙon karta tafi ta barsu, “Mom Please ki tashi, dan ALLAH karki tafi ki barmu muna sonki, idan kika tafi abin zai mana yawa Mom, idan kika tafi wa zamu kalla muji daɗi”. Ya ƙare maganar da kife kansa bisa fuskarta yana cigaba da kuka, shi kansa bai taɓa sanin shi rago bane mai rauni irin haka ba sai a yau, gani yake kaf duniya babu wanda ya kaisa shiga ruɗani da tsananin tashin hankali.
Har Jawaad daya ja motar ya fice daga station ɗin Qaseem nata kuka rungume da Mom. A haka suka isa General hospital, inda suka tadda ƴan jarida da jama'ar gari cike anan ma, har takai da ƙyar ƴan sandan da aka zuba ke control ɗinsu. Burin kowa yaga gawarwaki da mutanen da aka ƙwato wajen su Dad. A haka dai aka samu shiga da Mom ciki da ƙyar. Darajar waɗanda suka kawotan yasa akai mata amsar gaggawa da miƙata wani ɗaki.
Motar su Umm-Anum na shigowa asibitin ana shiga da Mom ciki, gurin a cinkushe yake da mutane, hakan yasa suka rasa hanyar da zasubi su shiga balle susan ta inda zasu fara. Aunty Batool ce tai tunanin kiran Jawaad, dan haka ta ciro wayarta daga bag ta fara nemansa, harta tsinke bai ɗaga ba, bata gajiba ta sake kira, nan ɗinma dai harta tsinken bai ɗagan ba. Kanta taɗan dafe zatai magana sai idanunta suka sauka akan Jawaad dake magana da wasu police su uku da alama suna masa bayani ne akan yanayin da asibitin yake ciki na cikar mutane da ƴan jarida.
“Alhmdllhi ga yayanmu ɗin canma ai”. Dukansu inda take kallo suka kalla, kafin wani ya samu yin magana Anum da Nabeelah suka nufi inda yake, sai dai kafin su ƙarasa aka dakatar dasu a tsawace. Bayani Nabeelah keson ma police ɗin daya tsaidasun amma yaƙi saurarenta, hakan yasa ta fara masa magana da tsiwa dan sun roƙesa amma yana neman cin zarafinsu ma. Hayaniyarsu ta jawo hankalin Jay ya juyo. A bazata yaga ƙannensa, ya ɗan ɗaura hannunsa na dama saman goshinsa da keyi tamkar zai tsage saboda azabar ciwon kai. Da sauri ya kalli police ɗin da suke tare yana nunasu Anum ganin wancan ɗan sandan da suke tare ya ɗaga hannu zai mari Nabeelah amma ta duƙe. “Kaga, cemasa ya barsu suzo”. Amsa masa yay da to, yana nufar inda su Nabeelah suke, yay saurin riƙe hanun ɗan sandan daya sake ɗaga hannu zai mari Nabeelah dan bakinta yaƙi mutuwa saboda haushin baƙar maganar daya faɗa musu dan sunce su ƙannen Jay ne wajensa zasuje. A harzuƙe ɗan sandan ya juya zaiyi magana sai yaga ogansu, saurin gyara yanayinsa yay zai masa bayanin abinda ya faru tsakaninsa da yaran sai yaji ogan nasa yacema su Nabeelah suje wajen Jay ɗin. “Oga kasan mi sukayimin kuwa?”. Murmushi yay masa da ɗan buga kafaɗarsa, “Komi sukai maka kayi haƙuri. ƙanen yallaɓai Jay ne”.
Da kaushin murya Jawaad daya tsare su Nabeelah da rikitattun idanunsa yace, “Miya kawoku nan?”. “Uh...Uhm Yayanmu bamu kaɗai bane, Ummu ce tace a kawota wajen Alhaji babba”. Nabeelah ta bashi amsa tana laɓewa bayan Anum idanunta cike da tsoro.
Da sauri Jay ya hau waige-waige, saiko idanunsa suka sauka akan Batool da su Ummah da suma kallonsu sukeyi. Batare da ya sake cewa komaiba yabar wajen zuwa inda su Batool ɗin suke.
Umm-Anum data rage a mota bata fitoba hango Jay ya nufosu ta fito da ƙyar dan jikinta duk babu daɗi, kallo ɗaya zakaima idanunta kuma kasan tayi kuka sosai, dan sun kumburi sun kumayi jaa.
Sauri riƙeta Jawaad daya ƙaraso yayi, ya taimaka mata ta tsaya akan ƙafafunta sosai tana sauke ajiyar zuciya, “Ummuna miyasa kuka fito? Kallafa ƙafarki ta kumbura?”. Maimakon ta bashi amsa sai tambaya ta jefa masa, “Ina Bilkisu?”. “Amma Umm......” “Ni dai ina yarinyata nace maka?”. Numfashi ya sauke da ɗan ƙarfi yana lumshe idanu sai kuma ya buɗe lokaci ɗaya, “Tana ciki Ummuna, sun saka mata drip ne saboda ta suma acan, amma inama ganin ƙila ta farka yanzun dan tun ɗazun Dr Bello ya sanarmin ta farfaɗo”. “Alhmdllh, babana fa”. Yanzu kam ɗan murmushi ya mata da sumbatar hannunta, “Shiyyasa naga idanunki sun kumbura ko Ummuna, kinyi kuka?”. Kansa ta dungure tana ƴar hararsa, yay murmushi da kama kunnuwansa alamar na tuba.
★★★★
Sun fara shiga ɗakin da aka kwantar da Bilkisu, kamar yanda Jawaad yay hasashe sun iske ta farka, tana zaune jingine da filo wata Nurse na bata abinci da takeci da ƙyar dan warin asibitin yay masifar addabarta, farkawarta amanta biyu saboda warin asibitin, yanzu ma Dr Bello ne da kansa yasa aka kawo mata abincin dan taci tasha magani kafin Jay yazo ya ɗauketa kamar yanda ya sanar masa.
Gaba ɗaya tayi wani zuru-zuru, idanunta sunyi masifar kumbura da ƙanƙancewa, sannan sunyi jajur a ciki. shigowar su Jay yayi dai-dai da zaburarta ta sakko a gadon saboda tahowar amai, Nurse ɗin ta ajiye tray'n abincin da sauri tana ƙoƙarin kamota amma tuni takai toilet. Duk rufa mata baya sukai cikin tashin hankali, sai dai duk a ƙofar bayin sukaja birki, Jay da Nurse ɗin ce kawai suka sami damar shiga. Sosai hankalin Jay ya tashi ganin yanda bily ke yunƙurin amai tamkar zata amayo hanjin cikinta, Nurse ɗin na riƙe da ita tana jera mata sannu da shafa bayanta. Matsowa yay kusa da ita shima ya ruƙo hannunta. Da ƙyar aman ya tsagaita, ya taimaka mata da kansa ta wanke bakinta, sai numfashi take saukewa a wahale, kwantar da ita yay a ƙirjinsa tausayinta mai tsanani yana ratsashi, a ƙasan ransa kuma tunani yake ‘mi taci haka?’.
“Ka kaini gida, banason warin asibitin nan”. Ta faɗa murya can ƙasan maƙoshi tana sake lafewa a jikinsa da shaƙar ƙamshin turarensa da yake ɗan dawo mata da nutsuwarta. Ɗago kanta yay ya saka fuskarta cikin tafukan hannunsa suna kallon juna, “Mi kikaci haka?”. Ya faɗa cikin tashi daskararriyar muryar yana raba idanu akan fuskarta tamkar zai gano abinda ke damunta anan ɗin. Matsawa tai zata sake kwanciya a jikinta tana faɗin, “Banci komaiba, warin asibitinne banaso nidai”.
“Jawaad yaya dai?”. Ummah ƙarama ta faɗa kafin ya samu damar sake tambayar bily.
Da sauri naja baya daga jikinsa dan na manta bafa mu kaɗai bane, bango na dafe saboda jikina babu ƙarfi. Ban iya fahimtar amsar daya bataba dan hankalina baya a garesu, tadai riƙe hannuna ta kamani muka fita sunata jeramin sannu.
Jay da duk damuwa ta sake lulluɓesa ya fita domin son ganin Doctor dan yazo ya duba Bilkisun ko akwai wata matsala data sakata aman ne.
A ƙofar ɗakin sukaci karo da Dr Bello da Nurse ɗin dake tare da bilyn, da alama itace taje tai kiransa. Fuskar Dr Bello washe da murmushi ya miƙama Jay hannu, “Dadyn baby ai bansan ka shigoba ma”. Duk da Jay bai fahimci sunan da yay kiransa da shiba sai yaɗan saki fuska kaɗan amma ba murmushi yayi ba, yadai sassauta ta daga cinkushen da take. Doctor bai gajiyaba ya sake faɗin, “Dama sister ce ke sanarmin madam na amai, wannan babyn da alama soja ne, dan nakula zai wajiga madam da yawa tun yana ɗan ficit”. Yanzunkam dai sosai Jay ya kallesa da alamar tambaya, sai dai ya gaza cemasa komai. Lura da hakan da Dr Bello yayne ya sakashi yin murmushi suka ƙarasa shiga ɗakin da Bily take, inda su Umm-Anum suka zagayeta sunata jera mata sannu, kanta na'akan cinyar Ummah babba.
Sai da ya gaisa da su sannan yayma bilyn sannu, kanta taɗan ɗaga masa kawai alamar amsawa, ya sake kallonta da murmushi ganin tanata faman rufe hannci, juyawa yay ya sake kallon Jay dake tsaye hannayensa duka a aljihu shima yana kallon bilyn. “Congratulations dear Friend, madam na ɗauke da babien mu ɗan sati shida. Ma'ana tana ɗauke da ciki ɗan wata ɗaya da sati biyu”.
Babu shiri Bily ta janye hannunta daga saman hanci tana waro idanu waje, ganin duk yanda suka zuba mata ido suna murmushi yasa taji kunya, saurin juya baya tayi taja gyalen Ummah babba ta rufe fuskarta ƙirjinta na wata irin bugawa da sauri-sauri.
Su Ummah kam fuskokinsu washe da murmushi sunata jerama UBANGIJI godiya da kirari, gaba ɗaya sai damuwar da suka yini da ita ta ɓace ɓat. Ubangayya da tunda aka fara cakwakiyar nan babu mai cewa yaga haƙorinsa a waje a take ya saki wani lallausan murmushi yana mai lumshe idanu, duk wata damuwarsa sai yaji ta gudu, farin ciki ya mamaye gurbinta. Dariyar su Ummah ce ta sakashi buɗe lumsassun idanunsa dake jajur, yay murmushi a karo na biyu yana girgiza kansa ganin iya shegen da Anuwar keyi shi da Anum da Nabeelah. Ya dage sai rawa yake yana waƙar larabawa shi a dole yayi ɗa ko ƴa, yayinda Anum da Nabeelah ke tayashi.
Cikin dariya Ummah ƙarama tace, “Yarona dama haka kake da iya shege ina ganinka wani ustazu?”. Umm-Anum dake murmushi tana kallon Bily da duk abin nan da ake taƙi kallon kowa tace, “Kaɗanma kika gani indai Anuwar ne, dama can Ustaz ɗin da babu Ustazai ne”. Dariya su Ummah da Batool da Dr Bello suka sanya, Jay dai murmushine har yanzu a saman fuskarsa, kunyar iyayensa ta sakashi dakewa abinsa yanata dai kallon bilyn ta ƙasan ido.
Aunty Batool tace, “Lallai ta maganar Doctor babyn nan namu soja ne, inba soja ba wannan gumurzu da akashawo amma ko gezau baiyiba saima nuna kansa da yayi wa duniya”. Sosai nanma suka sanya dariya, Dr Bello yace, “Gaskiyarki Sister kam, ALLAH dai ya inganta, kema saiki daure kiyi aure ki samo mana namu”. Duk kallon Doctor sukai banda Jay da Bilkisu dake ɓoye, Batool ta zuba masa harara. Shiko murmushi yayi abinsa yana sosa ƙeya waishi yaji kunyar su Ummah. Cike da tsokana Anuwar yace, “Su Aunty Batool kodai-kodai gidan Doctor zamu ɓulla ne?”. Duka takai masa ya kauce yana dariya, Doctor Bello ya kama hannun Anuwar yana faɗin, “Yauwa ɗan ƙanina tayani yaɗa manufa”. Yay maganar suna ficewa daga ɗakin.
“A to mukam wannan indai na ƙwaraine ai bashi zamuyi Batool”. Umm-Anum ta faɗa tana kallon Batool ɗin. Ƙasa tai da kanta batace komaiba. Ummah ƙarama tace, “Yayah wlhy bansan ko Dr Bello da wata matsalaba, mutum kirkine ɗan manyan mutane, sai dai babansane ɗan rigima, amma shima bawai ta ashsha ba”. “Ato Alhmdllh, bara nazo na fara shirin aurar da ɗiya kenan”. Murna Nabeelah da Anum suka fara, ita dai Ummah babba batace komaiba, hakama Jay uffan baice ba, yayi kamarma baya a ɗakinne, idonsa gaba ɗaya yana akan motsin matarsa.
★★★★★★★
Koda suka baro ɗakin da bily take da sallama daga Doctor gaba ɗaya sai suka nufi ɗakin da aka kai Alhaji babba, daga shi sai baba maigadi a ɗakin, jikin Umm-Anum har rawa yake, sai da Batool ta riƙeta, cike da sassarfa ta ƙarasa gaban gadon da Alhaji babba ke a ƙwance an saka masa na'urar taimakon numfashi, sosai jikinta ke ɓari, ta durƙushe ƙasa tana kamo hannunta cikin nasa da fashewa da kuka tana kiran sunansa. “Baba kaine haka? ka tashi baba kaga BILKEESUN ka, nadawo gareku baba, baba ka buɗe idanunka ka kalleni dan ALLAH kozanji sassauci babana farin cikina” ta ƙare maganar da ɗaura kanta a gefen hannunsa tana kuka mai tsuma rai. Suma su Ummah hawayen sukeyi har Bily, Batool da Nabeelah da Anum. Anuwar ma hannu ya saka ya ɗauke nasa ƙananun hawayen tare da ƙarasawa ya durƙusa ta ɗayen gefen kakan nasa daya fara gani a yau karan farko na rayuwarsa, Anum tazo kusa dashi ta tsugunna itama tana ɗaura hannunta akan na Anuwar dake riƙe dana Alhaji babba. Jawaad dai yana kallonsu, sai dai bazaka taɓa fahimtar yanayinsa ba, kamilar fuskarsa ta shanye komai.
A hakanli Alhaji babba yaɗan motsa hannunsa dake riƙe a cikin na Umm-Anum, saurin ɗagowa tai tana kallon hannun, ya sake motsashi a karo na biyu tare da kansa. tsitt ɗakin yay duk suka zuba masa ido. Sake motsawa yay fiye dana farko, sai kuma ya buɗe idanunsa a hankali ya sake maidawa ya rufe saboda nauyin da sukai masa, sake buɗewar yayi a karo na biyu, dishi-dishi ya fara hango Jawaad dake tsaye daga can ƙofar ɗakin yana facing nashi, ya ɗan kafesa da kallo tamkar dai yanason gano wanene?. takowa Jay yay a hankali zuwa gaban gadon, ya tsaya kusa da Umm-Anum tare da ɗan ranƙwafawa yanama Alhaji babba murmushi, hannu ya saka da kansa ya cire masa na'urar da aka saka masa. cikin magana a hankali yace, “Tsoho mairan ƙarfe!”.
Karan farko Alhaji babba yay wani ɗan murmushi kaɗan da sake motsa hannunsa sai ya jisu duka biyu an riƙe. “Babah!” Umm-Anum ta kira sunansa cikin sanyin murya. Cikin wata irin faɗuwar gaba Alhaji babba ya juya saitin inda yaji muryar da bazai taɓa mantawaba a rayuwarsa, to kodai mafarki yakeyine har yanzun? Ya ayyana a ransa yana ware idanu akan Umm-Anum dake kallonsa tana murmushi da hawaye.
Ya mata kallon kusan minti ɗaya kafin ya sake juyowa ya kalli Jay, sai kuma ya kalli Anuwar da Anum, ya sake maidawa ya kalli Ummah ƙarama da babba da Batool, Bilkisu da Nabeelah, cike da ƙarfin hali ya yunƙura zai tashi zaune dan ba'a ƙaramin ruɗani ya tsinci kansaba. Saurin riƙesa Jay yayi yana girgiza masa kai. Alhaji babba ya kalesa cikin muryar dake nuna bashi da lafiya yace, “Jawaad mafarkin dana sabane ko? Yo inba mafarkiba a ina nikam zanga mahaifiyarka ido da ido irin haka? Dan ALLAH kaga karka tadani a barcin nan barni nayi tayi ko ALLAH zaisa itama Rahmah da Maryam da Amina da Adamu zasuzo gareni duk mu haɗu anan”.
“Baba ba mafarki ka ke ba, Bilkisun ka ce a gaske gabanka, nice na dawo gareku, ni ce ban mutuba baba”. Umm-Anum ta faɗa tana rushewa da kuka. Ai yanzunkam babuma wanda yaga sanda Alhaji babba ya tashi dingangan zaune yana riƙo hannun Umm-Anum cikin nasa duka, jikinsa sai rawa yakeyi, hannunsa ya ɗaura saman idonsa ya murza, ya kai kuma kan fuskarta ya shafa. Tabbas ba mafarki yakeba Bilkisun sa ce a gabansa, bilkisun daya rasa kusan shekaru ashirin dashida, bilkisun daya fidda rai da gani a wannan duniyar dukda yana tsananin ƙwaɗayin hakan. “Bilkisu dama kina raye?”. ya faɗa da tsananin rawar murya.
“Ina raye baba, ganima ALLAH ya ƙaddara sake haɗuwarmu, na godema UBANGIJINA daya saka ka kasance mai tsahon ran da zan dawo na tadda, da ace na dawo baka raye bazan taɓa daina yima mutanen nan munanan addu'oi ba har randa numfashina zai yanke”. Fashewa Alhaji babba yay da kuka, ya kamo kan Umm-Anum ya ɗaura saman cinyarsa ya rungume yana sake fashewa da kuka mai ban tausayi da tsuma rai.
Da ƙyar Jay da Doctor suka samu damar lallashin Umm-Anum da Alhaji babba, harma dasu Ummah dasu Bilkisu, sai dai fa Alhaji babba ya tubure akan ya warke a sallamesa ya tafi gida, anyi lallashin duniya yace sam baisan wannanba wlhy shifa bazai kwana a asibitin nanba koma mi za'ayi.
Ganin ya rikice musu harda hawaye Jay yace Doctor ya basu sallama kawai, sai su sami likitan dazai dinga zuwa gida yana dubashi babu damuwa. badan Doctor yasoba ya basu sallama.
Jay da Anuwar ne suka kama Alhaji babba aka kaisa har mota, yayinda itama Ummah ƙarama ke riƙe da Bilkisu da keta dauriya da ƙarfafa jikinta dukda batajin daɗinsa sam, sai dai ƙasan ranta wani irin farin ciki takeyi da barin asibitin da zasuyi. Motar ta musu kaɗan, dan haka suka shiga ta Aliyu da suka iso asibitin babu jimawa suma dan an ƙaro jami'an tsaro cikin asibitin saboda mutane dake neman kawo ruɗani, acewarsu sunason suga gawawwakin da waɗanda aka samo da rai ko akwai ƴan uwansu a cikinsu.
Jay bai bisuba, cikin asibitin ya sake komawa inda Qaseem da Salman ke tare da Mom wadda ta farfaɗo amma sun mata allurar barci mai ƙarfi dan jininta ya hau sosai, Doctor ma yace badan ALLAH ya taƙaita mata wahalaba irin wannan faɗuwar da tayi zai iya sakawa ta kamu da paralysis. Sai da suka ɗanyi magana da Qaseem da shi kansa idan da za'a bashi gadon an taimakesa sannan Jay ya fito. Daya fito ɗinma wajen su Jabeer ya tsaya sukai magana sannan ya amshi key ɗin mashin ɗin ɗaya daga cikin jami'insu yabi bayan su Alhaji Babba.
_____________________
Dr Tayyeb Hospital
_________________________
Shahudah dai suma tai a wajen, sai da cikin ƴan matan family ɗin wata tai ƙarfin halin shafa mata ruwa sannan ta kawo numfashi, hakama matar Uncle Nasir ita sai dama aka bata gado, ƴaƴansa nata kuka maiban tausayi da saka zukatan mai kallonsu rauni. Kosu Uncle Sulaiman sai da suka share hawaye dan tsananin tashin hankali. A yanzun kam sun fahimci zaman asibitin sam bazai yuwu a garesuba, dan haka suka tattara inasu-inasu suka nufi gida, dan anma hana kowa shiga wajen Mama Badiyya dama, ba'ason ai mata wata hayaniya ko kaɗan.
Sun iso gida suka iske waɗanda suka bari anan cikin matsanancin tashin hankali suma, ciki harda Mama Atika da tafi kowa shiga ruɗani ganin halin da babba ɗanta yake a ciki da surukinta, tayi bala'in yin wujiga-wujiga da ita tamkar wata taɓaɓɓiya, dan sai surutai take, fitsari kuwa ba'a magana, tayisa a zane sau babu adadadi batare da tasan yanama zuba ba. Sai da ƴan asibiti suka isone suka fargar da ita halin da take ciki.
Tabbas bayyana irin kalar ruɗanin da wannan ahali suke ciki ɓata lokacine, sai dai na bama kowa gari ya ƙiyasta a ransa. Gashi an turo jami'an tsaro sun zagaye sashen Uncle Nasir ɗin babu mai shiga kamar yanda akaima gidan Dad shima.
_______________________
Ba ahalinsu Jawaad ne kawai a cikin ruɗaniba, duk ahalin dake da nasaba da waɗanan mutane yau hankalinsu baya tare da tunaninsu, anje kuma duk an zagaye gidajensu da jami'an tsaron sintiri, babu mai shiga babu mai fita. Waɗanda suka tsinci kansu a wani hali kuwa sai dai likitoci ake tura musu cikin gidajen suna dubasu.
Sosai ƙasarma gaba ɗaya take a hargitse bawai jihar da abin ya faru kawaiba, idan ka buɗe tv da redio babu wani magana saita wannan tashin hankali daya faru. Masu jaje nayi masu ALLAH wadai nayi, waɗanda suka jima suna zarginsu kuwa suka shiga maimaita ai dama a rina. Ƴan uwansu masu mu'amula dasu da suka rasa wasu mutanensu da suka rasu ta wasu hanyoyin tuni suka fara yayibo hujjoji da zarge-zarge suna ɗora musu (Kusan ɗan Adam kamar jira yake🤦🏻, abinda ma ba haka yakeba sai ya maidasa hakan🙄🚶🏻😏).
Masu ƙara gishi da magi a teburan masu shayi da gidajen suna da biki kuwa harda faɗin wai tukunya tukunya aka ringa fiddowa na farfesun mutane da gasashshen nama daga gidan😂, jini kuwa drom-drom sai kace wani mangyaɗa🤣. Aifa nayi ya samu a bakunan ƴan bani na iya, kowa burinsa ace shine ya fara kawo labarin🤒.
___________________________________
ƘARAMAR HUKUMAR GWANSU
_________________________________
Gidane madaidaici mai ƙyau, dan kuwa ko'ina na cikinsa mulmule yake da suminti, sannan an shafesa da fenti ruwan madara da ganye mai haske, ƙal yake da shara sai ƙyalli fasassun tiles ɗin da aka saka a tsakar gidan yake da ɗaukar ido. Yarone da zai iya kaiwa shekara uku ke barci kwance a ƙaramar katifa ta yara a tsakar gidan babu riga jikinsa saboda yanayin zafi, sai wani da bazai wuce shekara shida ba tsaye jikin ƙofar fita daga soron gidan yanata kumburi alamar wani abun akai masa.
Matashiyar mace da bazata gaza shekaru ashirin da huku ba ta fito daga matsakaicin kicin ɗin dake tsakar gidan ɗauke da tukunya alamar abinci ta kwashe, bayanta goye da jaririya ƙyaƙyƙyawa tanata barcinta hankali kwance. Tunkuyar ta ajiye inda alamu suka nuna wajen wanke-wanke ne tana mai harar yaron dake laɓe jikin ƙofar. “Wlhy kabari na kamaka a gidannan Fharhan sai na maka dukan da ko ubanka ba ganeka zaiyiba, karkazo ka ɗauki abincin su Innata ka kakai musu tunda ni na aikeka gidan su Musbahun har aka dakeka”.
Sake tura baki yayi gaba yana share ƴar ƙwallarsa, “To Umma ni kije ki amsomin ball ɗina, inaba hakaba ni bazankai abincinba kuma”. “Karka kai dan ALLAH kaga yanda zan kirɓa namanka a gidan nan mara mutunci..........”
“Yaya?! yaya?! dai”. Da gudu yaron da aka kira da Fharhan ya nufi mai maganar daya shigo yana faɗin, “Oyoyo Abbanmu”. Buɗe masa hannayensa yay ya shige jikinsa, ya ɗagashi sama yana dariya da faɗin, “Babana duk faɗan da nai maka akan yima Umma laifi bakajiba ko?”. Yaron ya ɓata fuska yana kallon Umman tasa dake tsaye tanama mijin nata kallon mamaki, yace mata wannan satin bazaizo weekend ba, amma kuma sai gashi a bazata da yamma liƙis. “Abbamu buguna zatai fa”. “Laifi kamata ai ko?”. Girgiza kai yaron yayi, kafin yayi magana ta matso inda suke ta ɗauka leda viva daya ajiye ƙasa lokacin da zai ɗauki Fharhan. “Sannu da zuwa”. Tafaɗa har yau da mamaki tattare da ita. Murmushi yay mata, yasa ɗayan hannunsa ya shafa kan yarinyar dake goye a bayanta. “Mai gadon zinarina barci akeyi?”. “Ai tunda naimata wanka ta ɓingire, irin wannan zuwan bazata haka”. Murmushi yayi batare da ya bata amsaba ya ida shiga gidan yana faɗin, “Banga na hannun damar Inna ba?”. “Gashi can yana barci”. Ta bashi amsa da nuna masa inda ɗayan yaron ke barci. Sauke Fharhan yay ya kama hannunsa suka nufesa, saida ya shafa kan yaronsa sannan ya zauna gefen tabarmar da aka ɗaura katifar. Itama ledar ta ajiye taje ta kawo masa ruwan sha. Sai da ta ajiye sannan ta sake kallon Fharhan, “Kazo ka kaima su Inna abinci karka bari na sake maimaita maka wlhy Fharhan ”. Baki ya tura zaiyi magana Abbansa ya hararesa, “Kanason na ɓata maka rai ko?” da sauri yaron ya girgiza masa kai, “Ɗauka abincin ka wuce, ka faɗama Inna muma muna nan zuwa gidan”. Da mamaki ta kallesa, sai dai bata iya cewa komaiba har Fharhan ya ɗauka kular abincin su inna ya fice daga gidan.
“Amma daga dawowarka kake.....” katseta yay da faɗin, “Firdausi babban al'amarine ya kawoni gida, zo kiga abinda na gano”. Babu musu ta nufesa, ya ɗago daga danna wayar da ya keyi ya miƙa mata wayar yana faɗin, “Ko zaki iya gane wannan?”. Da saurinta ta amshi wayar, hoton da taci karo da shi ta tsatstsare da idanu, kusan mintuna uku tana kallonsa cike da nazari ko ƙyaftawa batayi, da sauri ta zabura tana zaro idanu waje da ɗora hannunta saman baki, “Abban Fharhan wlhy kamar Bilkisu fa”. “Kama ko itace?” “Wlhy bana ko tantama Bilkisu ce wannan, ko wane irin canjawa zatayi a rayuwa bazan gaza ganeta ba, dan ALLAH ina ka samo mana Bilkisu? Bayan shekarun da muka ɗauka cikin nemanta babu ko labarinta”. Tai maganar tana zama kusa da shi cike da zumuɗi. “Nima yau na ganta Firdausi, a media naci karo da hoton yana yawo a dalilin abinda ya faru, tana cikin tawagar jami'an tsaron da suka nuna bajinta wajen kamo miyagun mutanen nan yan cultism, kinganta anan tare da mijinta ranar aurensu, shima jami'in tsarone”. “A...ab... Abban Fharhan wai kana nufin Bilkisun ce ta zama jami'ar tsaro kuma tai aure?”. “Wlhy kuwa haka na gani, auren nasu bai wuce wata huɗu ba akace, amma watanta kusan biyu kenan da tarewa, shiyyasa nake faɗa miki ki ringa ɗan shiga yanar gizon nan amma kinƙi, koba komai zaki san abubuwa da yawa da duniya ke ciki, yanzu hakama bakisan abinda ke faruwa a ƙasarba yau ɗin?”. “A'a na sani, dan ɗazun su Luba sunzomin barka kasan sanda na haihu tana Niger, to shine suke labarin, hakan yasa na buɗe redio anan naji komai”. Murmushi yayi ya sake miƙa mata wayarsa dake ɗauke da hoton Bilkisu da Jawaad a ranar dinner ɗinsu lokacin da suke wasan bindiga. Sosai Firdausi ta saku wani ihun farin ciki, ta rungume mijinta tana mai fashewa da kuka, “Wlhy itace Abban Fharhan, ashe zan sake ganin bily a duniyarnan. Abban Fharhan dan ALLAH muje gidan baba, wlhy nasan zaifi kowa farin ciki a yau, bashi da wani buri daya wuce gamo da Bilkisu, wannan shine burinsa, da fatansa a kullum”.
Babu musu ya amince, ta ɗakko mayafi da kayan da za'a sakama Abbas dake barci, shibe ya amsa ya saka masa, ita kuma ta shiga da kayansa ɗaki ta kulle ƙofar, ta kullo kicin da ɗakin da suke saka kayan abinci da tarkace, ɗaukar Abbas daketa barcinsa yay a kafaɗa suka fice a gidan, saida ta kulle sannan suka ɗauki hanyar gidan Baba a ƙafa da yake babu nisa sosai.
Sun iske Fharhan nata bama inna labarin abinda akai masa a gidan su musbahu abokinsa kuma maƙwaftansu, tanata lallashinsa ita kuma. Sai dai shigowar su firdausi yasata maida hankali a kansu, Abban Fharhan ya kwantar da Abbas a gefen tabarmar da suke sannan suka zauna suna gaisheta.
“Wai dama kazo garin Muktar?”. “A'a inna, zuwana kenan”. “To, shine kuma kuka taho nan? Lafiya dai ko?”. “Alhmdllh inna sai alkairi”. “To masha ALLAH, ai haka akeson ji”.
Kamar yanda ya nunama firdausi hoto haka ya nunama Inna itama, kwatankwacin ruɗanin da Firdausi ta shiga innama haka ta tsinci kanta a ciki, da sauri ta shiga ƙwalama Baba dake ɗakinsa kira. Fitowa yay da ɗan hanzari dan dama bai jima da shigaba wanka ya fito yake kimtsawa dan dawowarsa kenan daga kasuwar ƙauye da yake zuwa yanzun yana sana'ar kayan miyarsa.
Shikam ai ganin Bilkisu sai ya rikice fiye da zatoma, musamman dayaga hotunan waɗanda su Bilkisun suka kama, ya share ƙwallar data taru masa a cikin ido yana faɗin, “ALLAH mai iko, ALLAH mai hikima buwayi gagara misali. Muktar kayi haƙuri, dolene zuwa gobe mu koma birni tare da kai kuwa”.
“Baba har dani dan ALLAH”. Firdausi ta faɗa tana share ƙwalla. Inna tace, “Wlhy nima kam ba'a barina baya, dolene naje ganin ɗiyata”. Itama muryarta da rauni a ciki tai maganar.
A take babu wani ɓata lokaci suka yanke hukuncin tafiya birni gobe idan ALLAH ya kaimu koda kuwa idan sunje Alhaji lado da Jazuga zasu salwantar da rayuwar tasu kamar yanda suka faɗa musu a baya.
____________________________
Tunda muka baro asibitin saina samu ƴar nutsuwa, dan yanzu banajin aman sam, sai dai kawai rashin ƙwarin jiki da damuwar dake cike taf da ƙirjina harma da ruɗani, ganin duk abinda ya faru nake tamkar a mafarki zan farka zuwa anjima naji ba hakaba.
Mun yada zango a gidan Alhaji babba, inda muka iskesa zagaye da jami'an tsaro har yanzun, dan ba'a basu izinin barin gidanba. Aliyu na ajiyemu ya juya da cewar zaije ya nemo mana abincin da zamuci.
Kasancewar magriba tayi ba zama mukayiba, da yake bayan ɗakin Alhaji babba akwai isasun ɗakuna a gidan sai kowa ya samu wajen shiga a wadace, ni dai sakani Ummah ƙarama tayi nai wanka da ruwa mai ɗumi, kamar yanda Anuwar ya taimakama Alhaji babba shima yay wanka dan ya ƙara samun ƙwarin jikinsa.
Bani da wasu kaya a gidan dan haka na rasa yaya zanyi, saina maida na jikina na fito, salloli ake bina tun daga zuhur har mgriba da akeyi yanzun, gashi kayan jikina bana tunaninma zasuyi salla.
Ina cikin wannan hasashen Anum ta shigo ɗauke da leda, ajiyewa tai a saman gadon tana murmushi, “Ga kaya yayanmu ya kawo miki”. Kallonta nai da sauri, mamaki sosai a fuskata, “Yazo gidan ne?”. Kanta ta jinjina min, “Yazo yanzun nan shi da abokan nan nasa na wajen bikinku, amma sun fita massallaci, Ummah tace ki saka kiyi salla kizo kici abinci”. Kai kawai na iya jinjina mata, na miƙe nayi duk yanda tace, ina saka kaya ina kallon cikina dake a shafe tamkar babu kayan ciki ma, amma a haka ake maganar akwai ɗan mutum a ciki. Bansan murmushi ya suɓuce minba, na ɗaura hannuna akan cikin naɗan shafa.
Lokacin dana kammala rama sallolin dake kaina anata kiran sallar isha'i, dan haka na gabatar itama. ban fitaba, na kwanta a saman gadon ƙafafuna a ƙasa fuskata na kallon silin ɗin ɗakin, idanuna a lumshe suke, yayinda hannayena duka buyu ke cikin rigata ina shafa cikina, ni kaɗai nasan mi nakeji a lokacin, ina farin cikin samun ƙaruwar da ALLAH kaɗai ke wadata bayinsa da ita, gefe kuma inajin ɗacin tsintar wanda zuciyata take girmama da daratawa bayan iyayen firdausi fiye da kowa a duniya cikin mummunan hali. Tabbas da ace wanine yazomin da wannan labarin akan Dad bazan taɓa gaskatashiba koda kuwa ace Mijina ne, sai dai kash, nice da idanuna na gansa, da kunnuwana na jisa, ba'a cikin mafarkiba ko magagin barci, ba'a labari daga bakin wani ba. Haɗiye ɗacin daya tokare maƙoshina nayi daƙyar ina buɗe lumsassun idanuna jin ƙamshin turaren dana fi ƙauna fiye da kowanne a duniya a yanzun.
Jay daya jima da shigowa yana ƙare mata kallo harya gaji ya ƙaraso inda take ya durƙusa a bakin gadon. A hankali ya kwantar da kansa saman cikinta bayan ya janye hanayenta, ya lumshe idanunsa dake cike da nauyin damuwa dana gajiya.
“Kin bayyana a ranar da tarihi bazai taɓa mantawa da itaba Little Beejay, rana mai cike da ruɗani kala-kala da ban al'ajab, ina roƙon ALLAH ya raya mana ke cikin aminci, ALLAH yasa ki zama hasken idaniyarmu da al'ummar MANZON ALLAH (S.A.W) baki ɗaya, kizama madubi mai haska addinin musulinci a kowace irin nahiya, kizama jaruma irin Mamanki.....”
Murmushi ya suɓucemin babu shiri saboda jin sambatun da yakeyi, hannuna nakai saman kansa na fara shafawa a hankali ina sake faɗaɗa murmushi na, shi kaɗai ya ragemin yanzu a duniya sai gudan jininmu dake a cikin ciki, muryata da ɗan rawa nace, “Nidai insha ALLAH Little Jay ne”.
“Tab, yarinya ban yardaba”. Ya faɗa yana ɗaga kansa da sauri da hawowa saman gadon ya zauna, yunƙurawa nai zan tashi ya riƙeni, maidoni yay jikinsa ya kwantar dani saman ƙirjinsa. Sai da na shaƙi ƙamshinsa na lumshe idanu sannan na buɗesu a kan fuskarsa ma'abociya kamala da kamewa ina murmushi. Shima murmushi yay min kaɗan yana kafeni da jajayen idanunsa, ya duƙo da fuskarsa dai-dai tawa ya sumbaci goshina da laɓɓana. Sake lumshe idanu nayi da kai hannuna saman kumatunsa ina shafawa a hankali har zuwa bayan kunnensa. “Thanks you Sweet Love” na faɗa a can ƙasan maƙoshi batare dana san shauƙi ya kwasheniba nai suɓutar bakin. Idanu ya ɗan waro alamar mamaki, cikin sarƙewar halshe yace, “Mi ki ka ce?!”. Cusa kaina nai a ƙirjinsa wani masifan kunya na lulluɓeni, ya ɗago fuskata da sauri yana faɗin, “Please Miemaa sake faɗa naji”. Ƙara ɓoye fuskar nayi da ƙyau. “Pleaseeeeeeee”. Ya faɗa a wani irin yanayin daya saka tsigar jikina tashi na sake ƙanƙamesa. “Sweet Love” na sake faɗa a hankali. “Oh my God, wannan rana ta musamman ce a gareni” ya faɗa da sake ƙanƙameni yay baya muka faɗa saman gadon ina jikinsa. “Lilly kinzo da tarin sauyi” ya sake faɗa yana shafa cikina da lalubar bakina ya haɗe da nasa.
Karan farko a rayuwata dana fara maida masa murtanin abinda ya kemin kaina tsaye babu wani kunya kojin ɗar, a take ya haukacemin jikinsa sai tsuma yakeyi, munyi nisan kiwo sosai dan da gaske neman kaiwa inda yafi ƙauna yake nemanyi, ALLAH ya ceceni a bazata akai knocking ƙofar ɗakin.
Nice na fara ƙoƙarin zare jikina daga garesa a wale, amma duk da haka ƙoƙarin maidoni ya keyi, na sake ja baya sosai ina sauke tagwayen numfashi da sauri-sauri da gyara rigata, sake knocking ɗin akayi, sai dai narasa ta yanda zan amsa, dan inhar nayi magana sai angane halin da nake a ciki, gashi kuma bansan wanene ba. Juyawa nai na kallesa, yana kwance a yanda na barsa idanunsa a rumtse yana sauke nasa numfashin shima, nasan tabbas yanajin buga ƙofar da akeyi, amma ya share abinsa hankali kwance. Yunƙurawa nai zan miƙe naje na buɗe yay saurin riƙo hannuna, sake juyawa nai na kallesa, yanzu kam ya tashi zaune, ya zaunar dani saman cinyarsa sannan yay gyaran murya batare da ya kalleniba. Daga wajen Nabeelah tace, “Yayanmu ance kufito aci abinci”. Ajiyar zuciya na sauke a hankali, shikuma yace, “Uhhum”. Daga haka bai sake maganaba, Nabeelah ma haka saita bar wajen kasancewar tasan halin kayanta.
Kallon juna mukayi, yaɗan kaɗamin idanunsa da suka ƙanƙance yana cika bakinsa da iska ya furzar. Bance komaiba na maida kaina na duƙar. Shima bai sake cewarba ya ɗagani daga cinyar tasa bayan ya shafa cikina. Matsawa nayi gefe ganin na samu ya sakeni, batare da yace dani komaiba ya nufi bayi.
Ƙarar ruwa kawai na jiyo alamar wankama ya keyi kenan, na ɗan dafe kaina ina jinjina kaina, tunanin kar aga bamu fitoba ai zaton wani abunne ya sakani saka hijjab ɗina na fita ni, idan ya fito ya iskeni a can.
Tunda na fito suketa jeramin sannu, Umm-Anum ta kamo hannuna ta zaunar a kusa da ita. Ɗan kallon Alhaji babba dake gefenta nayi na gaishesa, ya amsamin da kulawa tare da sakamin albarka da doguwar addu'a akan namijin ƙoƙarin da muka nuna a jejin can dan a cewarsa yanzu ya ga komai a labaran dare da suke sake maimaitawa. Kasa cewa komai nayi nidai, na juya na gaida Umm-Anum itama dasu Ummah babba, sai Yaya Anuwar da Aunty Batool da Aunty Haneefa, Aunty Saudah da sukazo suma babu jimawa, Anum da Nabeelah kuma na basu hannu mukai musabaha.
Babu wanda ya tambayeni boss har aka fara zuba abinci a babban faranti kamar yanda Alhaji babba ya buƙata, muna shirin fara ci sai gashi ya fito sanye da kayan daya haɗo cikin nawa da Anum ta kaimin ɗazun. Ɗan kallonsa nayi ya zubamin harara, na ɗauke kaina ina haɗiye murmushin dake neman suɓucemin. Zama yay tsakkiyar Anuwar da Ummah ƙarama, shima yay bismilla kamar kowa ya saka hannu.
Muna gab da kammala cin abincin wayarsa ta shiga vibration, da farko kalla yay zai ɗauke kansa, sai kuma ya ɗauka wayar da ɗan zafin nama yana ja baya daga gaban abincin, babu wanda yasan mi aka faɗa masa ya mike da ɗan hanzarinsa yana faɗin, “Zanje office, na manta shaf munada meeting wlhy”.
“Meeting a daren nan Muhammad?”. Alhaji babba ya faɗa yana kallonsa.
“To ya zamuyi baba? Akan case ɗin mutanen nanne, kasan manyan ƙasar sunyi caa akan batun, gefe kuma al'ummar ƙasar suma da zafi-zafi suke buƙatar suga hukuncin da za'a yanke, gashi a kuma a dalilin faruwar al'amarin allura na neman tono garma”.
Murmushi Alhaji babba yayi yana faɗin, “Garmuna ma, dan ta wuce guda ɗaya. ALLAH ya bada nasarar ƙulla alkairi to, amma shiga ɗaki ka ɗakko magani kasha, wannan kan naka daga gani ciwo yakeyi”.
Baiyi musu ba ya nufi ɗakin Alhaji babban ya ɗakko maganin, ruwa ya ɗauka a inda muke yasha sannan yay mana sallama ya fice. Muka rakashi da addu'a mukuma.
Bayan kammala cin abincin zaman hira akai duk da gajiyar dake tattare da kowa, Umm-Anum ta fara bamu labarin rayuwar da ta tsinci kanta bayan barinta gida. Ma'ana sanda hankalinta ya dawo jikinta ta ganta a ƙasa mai tsarki, sai dai kuma ta gagara tuna komai daya danganci rayuwarta ta baya, da inda ta fito, da ahalinta.
Kuka kowa ya keyi hawaye shaɓe-shaɓe, duk da nariga nasan duk wannan tunda mu an faɗa mana sanda mukaje saudia nima saida nai kukan. Ummah babba ma ta labarta mata yanda abubuwa suka faru bayan barinta gida. irin neman da akaita mata da tashin hankalin da Mama maryam da Alhaji babba da Rahmah dasu kansu suka shiga, harma da ƴan uwan mahaifin boss. Rasuwar Mama Maryam da Auran Rahma.
Sai dai bayan wasu shekaru kuma sai kowa ya haƙura aka cigaba da binta da addu'a dansu tunaninsu koma ta rasune. Itama taci kuka, muma muka tayata.
Har kusan ƙarfe biyu na dare bamu kwanta ba. dan da ƙyar Anuwar dasu Aunty Haneefa suka lallaɓa Alhaji babba ya yarda zai kwanta ya huta daboda jikinsa, gashi Doctor yace ya samu isashen barci.
Muma duk tashi mukai mukaje muka kwanta kowa zuciya babu daɗi. cikin amincin ALLAH ni dai inama kwanciya barci mai nauyi yay awan gaba dani.
___________________________
Tafida family house
______________________
Lokacin da labari ya isa kunnen mama Atika akan ganin Umm-Anum sai tahau surutai tamkar wadda ta zare, tun su Uncle Uwaisu na ɗaukal al'amarin matsayin ruɗani harya koma basu tsoro. Dan sosai neman fita take daga hayyacinta.
Sake ruguntsumewa gidan yayi da tashin hankali, babu mai iya fahimtar yaren wani. Batun yunwa kuwa ai an manta da sunanta a wannan gida yau, dolefa aka danƙarama Mama Atika allurar barci ta ɓingire, har dare basa tare da nutsuwarsu, barema da Qaseem suka iso gidan Mom da itama take a jangwaɓe, ta tada hankalintane akan a maidata gida batason kwanan asibitin shiyyasa Qaseem ya kawota nan dan can gidan zamansa tashin hankali kawai zai ƙara mata.
Itama dai Mom maganar dawowar Umm-Anum ta nema maidata ruwa, dan ruɗani ta sake komawa ciki fiye da tunani, al'amarin sai ya sake bama su Uncle Sulaiman da basu san komaiba mamaki, a ganinsu dawowar Bilkisu cikin ƙoshin lafiya abin ayi murnane bawai tashin hankaliba, amma yarasa miyasa abin ke neman zama wani iri ga wasu daga cikin ahalin nasu?. Bashi da mai bashi amsa, dan haka yay gum da bakinsa kawai.
Saboda meeting ɗin da za'ayi shima dai Qaseem baro musu gidan yayi, sai da ya fara zuwa gidansa ya watsa ruwa yay sallar isha'i sannan ya nufi station batare da yay tunanin neman abinciba ma, dan shi sam a yinin yau bama abinciba ko ruwa sai ƙishirwa ta kaisa maƙura yake nemansa yasha.
______________
STATION
____________
Ɗakin meeting ɗin yay tsitt, tsumayen shigiwar oga kwata-kwata (Director General) daya iso garin a yammacin yau kawai sukeyi, kusan mintuna goma sai gashi ya fito tare da wasu manyansu. Duk miƙewa sukai tsaye domin girmamawa a garesu, suka ƙame tare da sara musu.
Shima murtani ya maida musu sannan ya zauna da nuna musu alamar suma su zauna. Zama duk su Jay sukayi, bawai matsayin rank ɗin Jawaad ya kai ai zaman wannan meeting ɗin da shi bane, kawai ƙwazo da suka nuna akan aikin ya kai shi ga shiga wannan tawagar, dan gaba ɗaya gurin manyansune nacan ƙololuwa, sai su Sir Ahmad dasu Qaseem, sai dai shi Qaseem ma gaba ɗaya yama kasa shigowa ɗakin meeting ɗin, koda yazo sai ya maƙale a office ɗinsa ransa duk a dagule.
An buɗe taron da addu'a a ɓangarorin addinan biyu, kafin D.G ya nuna kujerar data rage babu kowa cikin alamar son sanin wanda ya kamata ya zaunata. Sir Ahmad ne yay masa bayanin Qaseem, an ɗaga waya za'a kirasa Jawaad ya miƙe tsaye yana ɗaga hannu, damar magana Oga kwata-kwata ya bashi. “Sir ina neman alfarma”. “Muna saurarrnka”. “Sir Qaseem yana cikin tsananin ruɗani, inaga zamansa tare damu a wajen nan kamar zai ƙara tunzura tunaninsane ga wani abu daban, a ɗazun har mummunan hukunci yaso yankema kansa. mizai hana ai masa alfarmar barinsa kawai”.
Tsit ɗakin yay alamar jiran amsa daga bakin Oga. Sai da yaja kusan mintuna biyu kafin ya jinjina kansa yana gyara abin maganar gabansa. “Maganar Cpt gaskiyane, kasancewar abinda zamu tattauna ɗin yanada nasaba da mahaifinsa akwai damuwa, kuma shi jami'inmu ne daya taka rawar gani a wannan hukumar, ya cancanci koda sau ɗayane a nuna masa hallacin hakan”. Duk kawuna suka jinjina, inda wasu kuma a cikinsu hakan bai musu daɗi ba, dan su kam basuƙi ama kori Qaseem ɗinba daga hukumar gaba ɗaya.
Jawaad ne ya fara bayani akan matakan da sukabi dangane da kamasu akan dukanin bayanan sirri da suka samu, sai abubuwan da suka samo a gidan kama daga mutane zuwa wasu abubuwan daban, sai kuma adadin su Dad da suka kasance su 22 idan aka haɗa da shugabarsu data kasance mace. Sai ayyukansu da muƙaman wasunsu a cikin siyasa da kasuwancin wasunsu.
Bayan ya kammala ya miƙa takardar da dukkan bayanan suke ciki ga Sir Ahmad, wanda shi kuma ya miƙama D.G.
Amsa yay ya duba na tsahon wasu mintuna kafin ya ɗago yana kallonsu. “To duk kunji bayanai ga jami'inmu, mi zaku iya cewa ku?”. Hannu wani ya ɗaga aka bashi iznin magana.
“Sir ina ganin kawai mu miƙasu kotu mana, dan dukkanin bayanan da Jay ya bayar an samu mutanen nan dasu a zahiri kuma duniya duk ta gani, a ganina bama buƙatar wasu hujjoji kuma”.
Jin jina kai D.G ya shigayi, amma baice komaiba. Wani ya sake ɗaga hannu shima aka bashi izini.
“Ni kuma Sir a ganina kamar kaisu kotu ba mafita bace, dan za'a iya amfani da siyasa wajen kuɓutar dasu, ƴan ƙasa kuma su cigaba da kallonmu da laifin daba namuba, kawai mu riƙesu a wajenmu har iyakar rayuwarsu”. Nanma dai kawuna kawai suketa jinjinawa, wanima ya sake miƙewa shima ya faɗi ra'ayinsa. Haka sukaita faɗar ra'ayinsu ta kowanne fanni, inda maganganun su duk suna akan turbar gaskiya da kuma muhimmanci mai ƙarfi, shi dai Jay baice komaiba ganin duk manyansane keta magana, saida kowa ya lafa sannan D.G ya kallesa da kulawa. “Bakace komaiba Jawaad, bayan kuma kaine jami'in dayasan sirrin case ɗin nan fiye da kowa a cikinmu”.
Iska Jay ya zuƙa ya fesar, kansa a ƙasa yace, “Sir ai kune iyayenmu, zaku hango abinda mu sam bamu iya hangosa ba, duk hukuncin da kuka yanke muma zai zama dai-dai a garemu”.
“Hakane Jawaad, amma kuma da kuke ƙasanmu zaku iya bada shawara mai amfani da zatafi wadda mu zamu kawo, domin ku a yanzu kuke ganiyar ƙuruciyarku da kaifin tunani, sannan kuke shiga lungu da saƙo akan kowacce matsala, kune kuke ganin komai dangane da al'umma, kune kuke fita farautar masu laifi cikin kowanne irin runtsi da ƙalubale, mu muna office zaune, idan kun bada shawara ai bazai zama kuskureba”.
“Hakane Sir. To nidai idan har shawarata bata sauka a layiba ina ganin kaisu kotun shine babbar mafita, amma kafin hakan ya dace a faɗaɗa bincike dangane da masana'antunsu, da wajejen ayyukansu, akwai business da wasu a cikinsu ke gudanarwa a cikin ƙasa da wajen ƙasa, mizai hana musan mi suke fitarwa da shigowa ne? Masu ayyuka a gwamnati musan wane irin aiki suke gudanarwa a ofisoshinsu suma, daga haka mu basu damar neman lauyoyi muma mu samu namu ƙwararren lauyan. Hujjata anan itace dukansu waɗanan mutanen akwai zargin fyaɗe akansu wanda sam bama asan adadinsaba, sun lalata yara da yawa da mummunan aikinsu, ciki harda ƴaƴan ƴan uwansu. Duk yanda muke tunanin kare kanmu ga al'umma bazamu fitaba sai anyi komai akan idanunsu.........”
“Tayaya za'ai komai akan idanunsu?, fili kakeso a ɗiba a tara duka talakawa ai zaman kotun a gabansu komi?”. Wani ya faɗa aɗan fusace yana kallon Jay ɗin.
Murmushi Jawaad yay yana mai girgiza kansa, “Ba haka nake nufiba yallaɓai, abinda yasa na kawo wannan maganar ta al'ummah saboda idanma muna gudun manyan ƙasar zasubi ta ƙarƙashin ƙasa wajen saye alƙalan da zasu gudanar da wannan shari'a muryoyin ƴan ƙasa zai daƙile hakan, sannan suma manyan zasu tsorata domin inba waɗan nan jama'ar ai babu su, musaman idan mukai dubi da mafi rinjaye a cikinsu wannan shine hawa na farko da sukayi. sunason komawa na biyu, bazasu so sunansu ya ɓaci ba ai kodan mulkin da suka ɗanɗana suke kuma ƙulafuci da ƙwaɗayin komawa”.
Sir Ahmad dake murmushi ya kalli D.G, “Sir Jay yazo da maganar hankali, dominfa wannan faɗan sam ba namu baneba, faɗane tsakanin al'ummar ƙasa da waɗanan mutane, idan kuma har mukai tunanin shiga ciki wajen kare mutuncinsu to lallai zamu fuskanci ƙalubale harma a ringa zargin muma da namu dalilin mara ƙyau a ƙasa, amma idan min fidda komai ga al'umma muka kuma nuna musu suma sunada ƙarfin iko akai su kansu alƙalan zasu shiga hankalinsu sosai, sannan ƴan siyasa bazasuyi wani tasiriba wajen yaɗa farfagandar da suka saba. Kaga mun jefi tsuntsu biyu da dutse ɗaya, mun kuma ƙarama hukumarmu kima da daraja a duniya baki ɗayama ba wanan ƙasar kawai ba”.
“Wannan gaskiyane wlhy” wani ya faɗa cike da goyon baya akan zancen su Jawaad da Sir Ahmad.
D.G yace, “Okay, inaga to zamu tsaya a wannan matsayar, zuwa gobe sai mu yanke hukuncin daya dace ko ya kukace?”.
Duk kawuna suka jinjina masa cike da gamsuwa. Daga haka taron ya tashi. lokacin ƙarfe kusan uku na dare.
Jay baibar station ɗinba saida yaje office ɗin Qaseem ya fiddosa, shine da kansa ya kaisa har gida sannan ya wuce gidan Alhaji babba, ya iske duk sunyi barci, dan haka ya wuce ɗakin da yake tunanin Bilkisu na a ciki. Kwance ya sameta ita kaɗai a saman gado ta cure waje ɗaya kamar maijin sanyi, yay ɗan murmushi da cire kayansa sannan ya raɓa ta gefenta ya kwanta tare da turata cikin jikinsa. A take ta shaƙi ƙamshinsa, sai ta gyara kwanciya kawai ta lafe tana mai sauke tagwayen ajiyar zuciya kamar wata mage.
Murmushi ya sake saki mai sanyi, ya sumbaci kanta yana sauke tasa ajiyar zuciyar a jere.
________________
WASHE GARI
____________________
Washe gari ta kama Lahadi, tunda safe Jay ya samu kira daga Gimbiya Munaya akan takawa da kansa zai yoma su Abbu rakkiya gidan Alhaji babba.
Hakan ba ƙaramin mamaki ya bama Jawaad ba, dan haka ya sanarma dasu Alhaji babba halin da ake ciki, su kansu sunyi mamaki, to amma idan akai dubi da matsayin su Abbun a wajen Takawa hakan ba komai bane face girmamawa.
★★★★★
A family house ɗin su Jawaad ma sun wayi gari da shirin zuwa gidan Alhaji babba wajen Umm-Anum kamar yanda Uncle Sulaiman ya bada shawara shi da wasu a cikin sauran ƴan uwa.
★★★★★
Ɓangaren su Firdausi ma tun da farar safiya suka kammala nasu shirin na nufowa birni, sai dai su saɓanin ƴan masaurata da familyn Jay ne, su gidan Jawaad sukai shirin zuwa tamkar yanda Muktar mijin Firdausi yay ƙoƙarin sama musu adireshi a daran jiya ta dalilin wani abokinsa ɗan sanda.
★★★★★★
Maman Amina ma sun tashi ne da shirin nufar gidan Alhaji Babba kamar yanda Jay ya kirasu ya sanar musu suje dan Mama Safara'u ta gana da Umm-Anum.............✍
“Hummmmmmm!!!!! Wannan shine ake kira da ga wuri ga waina, to masu karatu, idanfa bakusan gariba to ku saurari daka, dan yanzu zamusan ma'anar ƘWAI CIKIN ƘAYA. su wanen ƘAYOYIN? su wanene ƘWAYAYEN?. Amsoshinku na'a page 61, saiku shirya kuma domin yin gangamin tafiya gidan ALHAJI BABBA mu gani wace wainar za'a toya shinnnnnnn?🚴🏼🚶🏻😢.
Masoya ZAFAFA 2021 fa sunata gagarumin shiri da yafi rukunin farko dana biyu da suka kawo muku a baya, mun shirya shiri na musamman domin ƙayatar daku da nishaɗantar daku da daɗaɗan labaranmu a wannan karonma, naga baƙwa motsawa😪, bayan kuma gagarumin shirin da muketa shiri dominku🤗.
ALLAH ka gafartama iyayenmu🙏🏻😭.
Post a Comment for "KWAI CIKIN KAYA BOOK TWO PAGE 60"