KWAI CIKIN KAYA BOOK TWO PAGE 57
Bilyn Abdull 📚:
Page 57
______________________________
SHAHUDAH
_______________
Saukar su Umm-Anum ƙasar haihuwarta tayi dai-dai da komawar Shahudah gida. Mom da Aamilah ne kawai a gidan, Dad ya fita tun bayan barin su Jay gidan. Waya Mom keyi da Mama Atika. A take ta saki wayar ƙasa ta tarwashe bisa tiles jikinta na tsananin tsuma.
Shahudah da ke cikin wani yanayi kamar ba'a hayyacintaba ta ƙaraso cikin falon tana tangaɗi ta zube saman carpet. Da ga Mom har Aamilah zubewa sukai a
gabanta jikinsu na rawa, sai kuma Aamilah ta miƙe da sauri taje ta leƙa waje. Babu kowa sai maigadi daya taimakama Shahudah ta shigo ya juya zai koma wajen gate. Komawa falon Aamilah tayi bayan ta rufe ƙofar ruf ta garƙama mata key. Ta koma wajen su Mom da gudu tana faɗin “Mom ita kaɗaice fa wlhy babu ɗan iskan”.Mom tace, “Nashiga Uku ni Aysha, Shahudah daga ina kike haka? Miyayi miki ne?”. Bata da mai amsa mata waɗanan tambayoyin dan Shahudah sai faman lumshe idanu kawai take. Mom ta ƙanƙameta a jikinta ta fashe da kuka tana jama ɗan-fir'auna mugayen addu'oi. Suna cikin haka akai knocking ƙofar, duk ɗagowa sukai suka zubama ƙofar falon ido kawai, sai dai daga Mom ɗin har Aamilah babu wanda ya iya motsawa. Shiru ba'a sake bugawar ba, hakan yasa suka share suka maida hankalinsu ga Shahudah.
Salman dake buga ƙofa ganin ba'a buɗeba sai ya zagayo ta kitchen, shikansa ba ƙaramin mamakin ganin Shahudah yay ba, jikinsa har rawa yake wajen ƙoƙarin kiran Dad ya sanar masa Shahudah ta dawo.
Cikin mintuna ƙalilan sai ga Dad a hargitse kamar zai tashi sama, yanda yake buga ƙofar kawai kasan babu lafiya, Aamilah ta buɗe masa tana matsawa ta bashi hanya, da sauri ya shigo. A gaban Shahudah ya durƙushe tare da maido kanta jikinsa idanunsa na kaɗawa lokaci guda dan ɓacin rai. “Shine ya kawota?”. Yay tambayar yana kallon Mom. “Nima ban saniba Dadynsu, shigowarta kawai muka gani ita kaɗai. Leɓe Dad ya taune da ƙarfi, ya kalli Salman dake tsaye cikin damuwa shima, “Kai Salman kiramin Dr Tayyib, ke kuma Aamilah kiramin maigadi, ai bazai rasa sanin wanda ya ajiyeta ba”.
Babu jimawa maigadi da Aamilah suka dawo falon, cikin girmamawa Maigadi ya rusina yana gaida Mom. Bata amsa masaba, sai Dad ne ya jefa masa tambaya, “Yaya akai Mamana ta dawo gidan nan?”. “Wlhy Alhaji ban saniba, kawai naji nishin mutumne a jikin gate, shine na leƙa nama zata ko yaran nanne masu addabama mutane, sai naci arba da ita kwance jikin gate ɗin, sai kuma ƙurar mota da nake zargin a ita aka ajiyeta”. Ran Dad ya ƙara digunzuma sosai, yay ma maigadi nuni da hannu alamar ya tafi kawai.
Maigadi na fita Dr Tayyeb na isowa gidan, bai zaman ɓata lokaciba ya shiga bama Shahudah taimakon gaggawa bayan an kaita ɗakin Mom an kwantar a gado. Duk wani taimakon da ake buƙata Dr Tayyeb ya bata, ya kuma tabbatar musu da cewar babu wata matsala normal zata farka insha ALLAH, ruɗanine ya sakata shiga wannan halin kawai. Hakanne ya basu ƴar nutsuwa, har suka kira su Mama Atika suka sanar musu dawowar Shahudah ɗin.
Normal Shahudah ta farka a safiyar yau kamar yanda Dr Tayyeb ya sanar musu, kasancewar ɗaki ɗaya, gado ɗaya ta kwana da Dad da Mom sai suka baibayeta da tambayoyi akan abinda ya faru da ita?. Tsaf ta kwashe yanda akai ta sanar musu.
“Dad ashe shiɗin ba mijina bane, tunda ya tafi dani wani gida ya kaini kawai ya ajiye bamma sake ganinsaba sai bayan kwana huɗu, ya sanarmin a randa aka ɗaura mana aure a ranar Bb ya saka shi ya sakeni, yace dan kawai yana ganin mutuncinsa yay hakan, amma badan Bb bane wlhy ko za'a kashesa bazai sakeni ba, kuma koda ya sakeni badan na taɓa zama matar Bb ba da bazai ƙyaleniba sai ya ketamin mutunci, wai Bb yana da kimar da bazai iya mu'amulantar abu shima yayi hakanba, Mom wlhy Bb mutumin kirkine, dan ALLAH ku bashi haƙuri mu koma aurenmu kamar da, ALLAH yanzu na amince zan haihu ko nawa yake so”.
Mom da Dad da mamaki ya cika suka kama hannayenta cikin nasu, cikin zafin rai Mom tace, “Zaki koma gidan Jawaad kuwa Shahudah, zaki koma kodan shegiyar yarinyar can tasan asirinta ai
kin banzane, namiki alƙawarin a yau ɗin nan basai gobe ba za'a maida aurenku da Jawaad”. “Mom da gaske? Dad kaima kuma ka yarda da hakan?”. “Ɗari bisa ɗarima kuwa mamana, duk abinda kikeso a duniyarnan saikin samesa ko minene shi, duk abinda Momynku ta faɗa kisa a ranki ya gama tabbata”. Rungume Dad tayi tana fashewa da kukan jin daɗi, suma suka rungumeta cike da so da ƙauna harma da tausayinta.
Gari na ƙarasa wayewa Mom ta ɗauki Shahudah suka tafi family house ɗinsu.
______________________________
BEEJAY
______________
Da ƙyar muka iya tashi sallar asuba, musamman ma ni da jikina ke ciwo ta ko ina, idanuna sunmin nauyi sosai na rashin barci da kukan da na sha. To nidai bansan randa zan zama jarumar ba, duk yanda zan fasaltama mai saurarona zai ga kawai nacika rakine da ragwanta, amma ni kaɗai nasan sirrin al'amarin kawai.
Da taimakonsa mukaje bayi badan bazan iya tafiya da kaina bane, hakan kawai shi yaso shiyyasa ya kamani muka shiga tare. Tare mukai wankan da bamu samu damar yi ba saboda tsabar barcin da yaci ƙarfin idanunmu, muna fitowa ya fice daga ɗakin.
Tsaye nai ina tunanin ta'ina zan fara ne? Bani da wani kayan sakawa a ɗakinsa sai abinda baza'a rasaba, tunanina ne ya katse jin motsin mutum da sallama ciki-ciki, ya ajiye kayan dake hannunsa kusan kala bakwai, sai leda da alamu ya nuna kayan barci dana cikine a ciki, ajiyar zuciya naɗan sauke, bai jira cewataba ya sake ficewa.
Ana idar da sallar asuba ban zaunaba, ina ƙoƙarin tashi ya shigo ɗakin da sallama, da alama ko azkar bai zauna yiba balle ai maganar motsa jiki, jallabiyar jikinsa kawai ya zare ya ajiye ya haye gado, matsawa nai na gaishesa, batare da ya amsa minba ya jawo hannuna na faɗo kansa, “Ouch” ya faɗa a hankali alamar yaji zafi, ɗan kallonsa nai sai kuma na kumbura baki. Hancina yaja yana wani lullumshe idanu, ya birkiceni na koma ƙasa fuskokinmu daf da juna muna shaƙar iskar numfashin junanmu. Cikin yin mar-mar da idanu na tsoro nace, “Ina kwana?”. Shiru yay kamar bazai amsaba yanzunma, yanata ƙarema fuskata kallo, ya sumbaci goshina yana sake ɗagowa da ƙoƙarin saka idanunsa cikin nawa amma naƙi yarda da hakan. Saima ɓata fuska nai ina faɗin, “Abinci zan ɗora fa”. “Da wane ƙarfin?”. Ya faɗa a ƙasan maƙoshi, dan koni dake daf dashi badan ina kallon lips ɗinsa ba ba lallaine na fahimtaba. “Da nawa mana” na bashi amsa nima ciki-ciki. Nauyinsa ya ɗan sake sakemin yana faɗin, “Oh ni kika raina kikema raki dama kenan?”. Tuni idanuna sun fara tara ƙwalla, “ALLAH zaka kasheni”. Nai maganar a rarrabe dan na fara sauke numfashi da ƙyar. Yi yay kamar zai ƙarasa sakarmin nauyin sai kuma ya ɗagani yana dunguremin kai. Nannauyan numfashi na sauke ina lumshe ido irin na ALLAH na gode makan nan. Na yunƙura zan tashi ya maidani ya sake kwantarwa. “Barci” ya faɗa a cikin kunnena. “Idan nayi barci sukuma mi zamu basu suci?”. “Shiiii!!” ya faɗa batare da ya bani amsata ba. Shirun kuwa nayi ina masa kallon mamaki, yaja bargo ya lulluɓemu da shi tare da sakani a cikin jikinsa, a hankali ya furta, “Thanks you Miemaa”. Bansan dalilin godiyarba, dan haka na sake lafewa a jikinsa nace, “For What?”. “For Everything Zinaran” Ya bani amsa da wani irin salon da yasa tsigar jikina tashi. Sake lafe masa nai a jiki ina shaƙar mayataccen ƙamshin turarensa da akwanakin nan yakemin daɗi fiye da komai. barcin mukeji, dan haka kafin wani dogon lokaci yayi gaba da mu.
Barcin da su Umm-Anum suka gagara yinsa a daren jiya yau suna idar da salla suka nema yinsa, koda Jay da Anuwar suka shiga gaishesu sama-sama suka amsa musu, Jawaad da yasan za'a rina yaja hannun Anuwar suka fito. Dama yasan ai wannan barcin sai sunyisa dan shi ba'a cin bashinsa daman.
Kasancewar na kwanta da maganar abincin a raina sai barcina baiyi tsahoba na tashi, a hankali na zare jikina daga nasa na sauka a gadon, badan barcin ya isheniba na tashi, zuciyatace kawai bata aminta dana kwantaba bayan gida cike da baƙi. Ina fitowa babban falo naci karo da kulolin abinci, da mamaki na isa garesu na bubbuɗe, lafiyayyen breakfast ne a ciki wa
nda ya fito shar kamar ka zauna ka cinye kai ɗaya. Mamaki ya kamani na inda ake kawo wannan abincin? Sanin bani da mai bani amsa sai kawai na shiga kwashesu zuwa kitchen, na dawo nahau gyaran falon zuwa falonsa da nawa da duk inda dai bazan takurama masu barciba. Kafin su tashi na shirya abincin a falona na koma nayi wanka na na shirya tsaf cikin zani da riga na atanfa da sukaimin ƙyau.
Jinai kamar ana kallona, na juyo da sauri na kalli gadon batare dana ƙarasa ɗaurin ɗan kwalin ba. Boss dake kwance idanunsa a kaina ƙyam ya ɗan lumshesu ya sake buɗewa a kaina cike da salo. “Dama ka tashi?”. Kansa ya jinjinamin kaɗan batare da yace komaiba. Ɗan kwalinma sai naji na kasa cigaba da ɗaurasa saboda idanunsa duk sun takurani, haka dai na daure na ƙarasa na miƙe har lokacin idanunsa a kaina. Toilet naje na haɗa masa ruwa na fito, yanzu kam zaune na iskesa a bakin gado da waya a hannu. “Ga ruwan wanka can”. Kansa kawai ya girgiza min, batare da yace komaiba. “ba yanzu zakayi ba?”. ajiye wayar yay ya ɗago yana kallona, “Barshi idan naci abinci zanyi, bara na duba saƙon nan da Jabeer ya turo min” yay maganar yana miƙewa ya nufi Computer ɗin dake a ɗakin inda ya gyara a can gefe tamkar wani ɗan office. Da kallo kawai na iya binsa, danni mamaki yake bani yanda sam bai gajiya da aiki. Komai banceba na gyara gadon kawai na fice daga ɗakin.
A falo na iske Aunty Batool ta fito cikin shirin fita, na bita da kallon mamaki da alamar tambaya. Murmushi tamin kaɗan tana gyara mayafinta, “Zanje gida saboda abincin Alhaji babba, naga Ummah ganin ƴar uwarta yama mantar da ita”. Murmushi nayi, “Ah haba aunty Batool itama nasan ba mantawa tayi ba, kawai dai tana cikin yanayine mai wahalar fassara, to mizai hana ki ɗiba masa na nan? Idan kuma wani ya keso daban ai saina girka masa yanzun nan insha ALLAH”. “A haba, wahalan ai sai yayi yawa, bara kawai naje can ai zan dawo, koda yake nama san acan kuma yau za'a yini ma”. “A'a dan ALLAH, muje kiga na nan ɗin dai aunty Batool, shima idan yaji kin tafi can dan kawai dafa abincin baba ai bazaji daɗiba”. Nai maganar ina marairaice mata.
Da ƙyar na samu ta amince mukaje kitchen ɗin, duk abinda tasan zai iya ci shi ta ɗiba masa, ta zuba a kwando ta fice riƙe da key ɗin motar da sukazo a ciki.
Coffee na haɗa na koma kaima Boss, yanata aikinsa hankali kwance, na ajiye ɗan tray ɗin dana ɗora ƙaramar butar shayi da kofinta sai cokali a gabansa, tsiyayawa nai na miƙa masa, batare da ya kalleni ba ya amsa yana faɗin, “Waye ya fita da mota?”. “Aunty Batool ce” na bashi amsa a taƙaice. Baice komaiba yakai kofin bakinsa, ɗayan hannunsa kuma yana amfani da mouse.
★★★★★★
Zuwa goma da rabi duk mun hallara gaban abinci, bayan gaishe-gaishe da tambayar lafiyar juna mukai zaman karyawa, kowa nacin abinci cikin salama bandani da naketa tsakurarsa, badan rashin daɗiba kuma, haka kawai dai nakeji bana sonci kuma yunwa nakeji.
Jay ya lura bily batacin abincin sam, sai dai kunyar iyayensa ta hanashi cewa komai. Ummah babba ce ta lura da hakan, saita kira Bilkisu. Tashi nai na nufeta dan nazata wani abun zata sakani, sai dai ina zuwa ta jani ta zaunar kusa da ita, da kanta ta shiga ɗuramin abincin duk da nace mata na ƙoshine, ina kallon sanda boss ya sauke ajiyar zuciya. Daurewa kawai nake ina amsar abincin.
Boss ne ya fara miƙewa alamar ya ƙoshi, yaɗan kalli iyayen nasa yana faɗin, “Bara naje na watsa ruwa kafin time ya ƙure, jirgin su Abbu ƙarfe sha biyu zai sauka”. Cikin kulawa Ummah babba da ƙarama suka amsa masa.
Shigewarsa babu jimawa muma duk muka kammala, da taimakon su Anum na gyara wajen, gudun kar kwanikan su bushe sai mukai zaman wankesu, muna wanke-wanken ina tunanin abinda ya kamata na dafa mana da rana, dan koma daga ina ake kawo wannan abincin bana buƙatar a cigaba da kawosa, ya kamata nima in-lows ɗina suci girkina ai....
★★★
Jay na fitowa daga wanka ya samu wayarsa na haske kasancewar a silent take, matsawa yay gaban mirror ya shiga shafa mai batare da ya duba mai kiranba ma, bayan ya kammala yana gaban Wadrobe zai ɗauka kayan d
a zai saka ya kuma hangar wayar tana haske, guntun tsaki yaja, ya ɗauka kayan da yake bukata ya fara sakawa, sai da ya shirya tsaf sannan ya nufi wayar yana idasa saka maɓallan rigarsa. Gabansa ne ya ɗan faɗi ganin Batool ce ta jera masa har missed calls kusan talatin, sai kuma number sojan da sukanyi magana da baba ƙaura idan hakan ta taso. tabbas wannan kiran bana lafiya bane, dan kaf cikin ƴan uwansa babu wanda ya kai Batool iya zama da shi da halinsa, inhar tai masa kira ɗaya tai na biyu taga bai ɗaukaba bazata sake kiransaba sai idan shine ya kirata. Yana ƙoƙarin kiranta sai gashi ta sake kira, ɗagawa yay da sauri....
Daga can Batool ta sake fashewa da kuka jin an ɗaga, a cikin tsananin ruɗani tace, “Yayanmu akwai matsala, wasu mutane sunzo har gida sun tafi da Alhaji Babba da baƙon mutumin nan”.
Wani irin yankewa ƙirjin Jawaad yay ya faɗi, furicin Batool ya jisane cikin kunnensa tamkar saukar guduma, cikin rawar baki yace, “Su su.. Su wanene?”. “Ban sansuba Yayanmu, ina ɗakin Alhaji babba ina gyarawa suka shigo. fuskokinsu duk a rufe suke da facemask, nima nasan da sun ganni bazasu barniba, tun shigowarsu nake kiran wayarka amma baka ɗaukaba, ina tsoron na kira su Ummah su ruɗar da kansu shiyyasa ban kiraba.....” Bai bata amsaba ya katse kiran, ƙirjinsa na wani irin lugude tamkar ana gasar dakan fura a kansa. Da sauri ya fice daga ɗakin, harya nufi sashen Bilkisu sai kuma ya jiyo dariyarsu a kitchen ita dasu Nabeelah, can ya juya ya nufa......
Muna tsaka da yima Anum dariya boss ya faɗo kitchen ɗin, yanayinsa kawai ya sakani faɗuwar gaba, Anum da Nabeelah kam duk ɗauke numfashi sukai dan tsoro, baice komaiba yaja hannuna muka fice, har munje ƙofa ya juna yana watsama Nabeelah kallon gargaɗi, “Kucigaba da aikinku, idan kuma ƙafar wani ta fita a kitchen ɗin nan saina ɓallata”. Kai kawai suka jinjina masa, ya ja hannuna muka ƙarasa ficewa zuwa bedroom ɗinsa.
“Boss lafiya kuwa?”. “Babu lafiya Miemaa, yanzu Batool ta kirani........ Akwai matsala ace su Ummuna susan wannan maganar, musamman ma ita da nasan yanzu babu wanda ta ƙagu ta gani kamarsa, dan haka kiyi shiru da bakinki yanzu zan tafi can, kosun tambaya kice nafita amma zan dawo yanzun k.......”. Da sauri na katsesa da faɗin, “Boss tare zamu tafi, nima bazan zaunaba”. “Bazai yuwuba Miemaa, idan muka fita mu duka zasu iya tunanin wani abu”. “Dan ALLAH kayi haƙuri mutafi tare, koba komai nima zanyi wani amfanin ai, zamana anan zaisa na kasa jurewa na tona asirin komai”. “Miemaa!....” “Please boss”. Nai azamar katsesa. Bakinsa ya cika da isaka ya furzar da ƙarfi yana ɗaga wayarsa dake haske. Ban saurari amsarsa ba nashiga ƙoƙarin canja kayana.
Ta kitchen muka fita, bayan boss ya jama Nabeelah dogon gargaɗi akan ta kama bakinta wlhy, idan har sukace mun fita sai yay gutsi-gutsi da ƙasusuwanta yanda babu mai iya shaida itace harma Anum ɗin kanta. Daga haka muka fice, Sadiq baizoba, saboda weekend ce, dan haka boss da kansa zaiyi driving ɗin.
Mahaukacin gudu ya ke zubawa tamkar shi kaɗaine da titin, to dama yaya lafiyar giwa balle....., dama can shi ɗin ɗan babu sauƙine wajen gudu da mota, balle yanzu data zamto na ƙare numfashi. Ko gezau banyi da gudun nasaba yau, gani nakema tamkar baya gudun, sai faman kaɗa yatsun hannuna nake jikinna na wani irin tsuma. Yayinda boss kuma yana tuƙi yana waya da su Oga Hafiz.
Cikin mintuna ƙalilan muka iso gidan, mun iske tawagar su Jabeer a gidan harma da ƴan sandan zahiri, sai wasu daga cikin ƴan anguwa da abin ya faru akan idanunsu su Hafiz nata musu tambayoyi.
Aunty Batool ta iso garemu da gudu tana kuka, riƙo hannunta boss yayi idanunsa na sake kaɗawa suna sake komawa jajur fiye da yanda muka fito gida. Bayanin duk yanda yanda al'amarin ya faru ta shiga yimasa kamar yanda tayima su Sir Ahmad ma. Kasa cewa komai yay, sai jikinsa dake wani irin rawar bala'i, ƙwanjinsa da jijiyoyin kansa na sake buɗewa, yanda ƙirjinsa ke sama da ƙasa kawai zai tabbatar maka zuciyarsa na gudu maiban tsoro dake neman fin ƙarfin gangangar jikin nasa. ya saki hannunta ya nufi inda su oga A
liyu suke. Matsawa nai na rungumeta muna hawayen tare, sai dai ni saɓanin ita ina ƙarfafa zuciyata yau ina lallashinta, sai da naga ta tsagaita da kukan sannan na ɗagota na share mata hawayen. “Ki kwantar da hankalinki aunty Batool, insha ALLAHU zasu dawo, kosu wanene ALLAH bazai basu dama akan ƙudirinsu ba”. “ALLAH yasa haka mami” ta faɗa wasu hawayen na sake jiraro mata. kiran da oga Jabeer yaymin ne yasa na taimaka mata ta zauna a cikin motar.
Tun a yanda Jawaad ɗin ya taka birki sanda suka iso gidan su Sir Ahmad sukasan ransa a matuƙar ɓace yake fiyema da yanda sukai hasashen ganinsa. ganin Batool ta nufesa sai duk suka dakata daga yunƙurin zuwa inda yaken, bayan yabar wajen ya nufesu ne, Sir Ahmad yay saurin tararsa cikin zafin nama yana riƙe hannunsa “Jay! Ka kwantar da hankalinka, insha ALLAHU zamu gano inda suke, koma su wanene suka aikata hakan basuyi nisa damuba a halin yanzu tabbas, yanzu haka har su Jabeer sun fara ƙoƙarin gano inda suke. Ka nutsu banason ka fusata kanka da yawa, domin nutsuwarka ce abar buƙatarmu fiye da komai a yanzu. shin akwai wani da kake zargi ne?”.
Jawaad dake tsaye kawai yana kallon yanda su Aliyu da sauran ƴan sandan keta kai kawo akan al'amarin ya lumshe idanunsa yana busar da zazzafan numfashi, “Sir! Kowama zan iya zarga a halin yanzun, sai dai hakan bazai saka na kasa fidda ɗaya a cikin dubu ba”. “Nasani gwarzona”. Sir Ahmad ya faɗa yana ɗan bubbuga kafaɗar Jay ɗin cike dajin ƙarin alfahari da ƙwazon yaron.
Jabeer ne ya ƙaraso wajen riƙe da tab.. A hannu, yay salute ɗin Sir Ahmad sannan ya kalli Jay dake kallonsa shima. “Boss ƴan iskan mutanen nan basu bar wani alama ko kaɗan da za'a iya bibiyarsu ba, bayanan dake hannunmu ma a yanzu haka ko motar da sukazo a cikinta babu Number ma, abinda bayanan mutanen anguwa suke faɗa mana kawai motar baƙa ce, suma mutanen kuma baƙaƙen kayane a jikinsu, fuskokinsu a rufe”. Shiru yay yana kallon Jabeer cike da nazarin maganganunsa, kafin kuma ya kallesa yana ɗan cije lip ɗinsa na ƙasa, “Dama bana tunanin zasu bar wata alama ta zahiri, sai dai dolene za'a samu ta baɗini Jabeer. Zamanmu anan gidan baida wani amfani, inaga mu wuce office kawai”.
Jabeer yace, “Okay nima nayi wannan tunanin, dama isowarka muke jira muji ta bakinka, dan yanzu haka dai Number shi Alhaji Babba muketa ƙoƙarin bibiya saboda Batool tace tana zaton da ita ya tafi a jikinsa batare da suma maharan sun sani ba. a yanzu haka dai wayar na nuna tana titin gambari gab da babban titin ƴan robobi na gabashiya. Jami'anmu suma suna gab da isa wajen harda Aliyu”. Amsar Tab ɗin Jay yayi daga hannun Jabeer da sauri....
Hakan yay dai-dai da isowar Bilkisu da wani tunani yazo mata a zuciya inda suke. Sai da tai Salute ɗin Sir Ahmad itama sannan taɗan matsa kusa da Jay da hankalinsa kega Tab... ɗin da ya amsa a hannun Jabeer, amma yasan da zuwanta, dan ƙamshin turarenta ma ya ishesa shaidar tana wajen. “Sir anya kuwa wannan aiken ba daga gidancan bane?”. Da sauri Jay ya ɗago yana kallonta, “Wanne a ciki?” ya faɗa cike da ƙaguwa. “Inda na dawo daga farauta shekaran jiya”. Kafeta yay da ido dan maganarta na tafiya bisa ƙamshin gaskiya. Ta ƙara risinar da kanta cikin girmamawa a garesu, cigaba tai da faɗin, “Bazai yuwu ace dama ya barmu ba, dolene zai bibiyemu kodan maigadinsa, sai dai bamu da tabbas, hasashene kawai nayi Sir”. Jawaad yay wani ɗan murmushi yana maida duka hannayensa biyu ya goya a bayansa, taku ɗaya biyu yay sai kuma ya sake juyowa, hannunsa ɗaya ya sauke daga bayan ya tura cikin aljihu, ɗayan dake riƙe da tab... Kuma ya ɗagosa yana goga tab... Ɗin akan hancinsa. Daga Jabeer har Sir Ahmad da bilyn duk kallonsa sukeyi. Wani murmushin ya sakeyi da tsayawa cak, bily ya nuna da tab... ɗin hannunsa yana faɗin, “Maganarki akwai ƙamshin gaskiya, dolene a cikin biyu a samu ɗaya, idan kuma nai wani nazari zan iya ɗaurasu a mizani guda ya zama aikin haɗaka ne”. Ya ƙare maganar yana maida dubansa ga sir Ahmad da ke binsu da kallo kawai. Kafin yace wani abu Hafiz ma ya iso riƙe da waya alamar magana ya gamayi. “Mutanen nanfa inaga sun farga da
wayar jikin Alhaji babba, sam yanzu bama ganinsu alamar an kashe wayar”. Kallonsa duk sukayi, Sir Ahmad yace, “Dai-dai ina kuka daina samunsu?”. “Sir a Roundabout ɗin titin General hospital”. “General hospital?”. Jay ya faɗa cikin sigar tambaya. “Ƙwarai kuwa boss, ka duba ma zaka gani anan”. Tab... Ɗin Jay ya sake buɗewa, dai-dai inda Hafiz ya faɗa shima nan ya nuna masa, ya miƙama Jabeer tab... ɗin yana faɗin, “Yanzunan inason a bincikamin inda Alhaji Kokino yake, a kuma bincikamin inda Alhaji Ali da Qaseem suke, sai Mr Gebrail shima”. Yana maganarne yana daddana wayarsa daya ciro a aljihun wandonsa. Da mamaki na kallesa jin ya sako Dad da Yah Qaseem ciki, sai dai yanda yay kicin-kicin da fuska yasa na gaza cewa komai, sannan ma bani da wannan damar dan a fagen aiki muke matsayinsa na ogana ba miji ba. Da to muka amsa masa kawai, muna barin wajen.
Sir Ahmad dake kallon Jay yace, “Miyasa ka lissafo waɗanan mutanen? Kana zarginsu da aikata hakanne?”. “Sosaima kuwa Sir”. Jay ya faɗa yana ɗaura wayar a kunnensa jin an ɗaga. “Munkaila kana ina?”. Bansan amsar da aka bashiba daga can, ya gyara tsaiwarsa idonsa a sashen da su Bilkisu ke magana ita dasu Jabeer yace, “Ka ajiye wannan aikin, yanzun nan kaje gidan Alhaji Ali a ɗakkomin maigadin gidansa da kuku”. Kansa ya gyaɗa da sauke wayar.
“Jay ka sake sakani a duhu, wai ba kana magana bane akan Alhaji Ali dana sani baban Qaseem? Da shi Qassem ɗin kansa?”. Fuskar Jay cike da murmushin takaici ya jinjina ma Sir Ahmad kai, “Shi nake nufi Sir”. “To amma miya haɗashi da Alhaji kokino da har kake tunanin zasuyi aiki tare?”. “Hasashene kawai Sir”. Ya bama sir Ahmad ɗin amsa a taƙaice. Badan bai yarda da shi bane, yanason tabbatarwa kasafin ya buɗe aikin kowa ya sani........
__________________
BABA ƘAURA
______________
Tun a safiyar yau baba ƙaura ya sa ake nemar masa Number Jay sai dai ba'a samu ba, iya ƙoƙari sojan dake taimakama baba ƙaura idan zaiyi waya da Jay yayi amma wayoyin Jawaad ɗin duk sun ƙi shiga, sai kusan goma na safe da ƙyar ɗaya ta shiga, sai dai kuma anƙi ɗagawa kusan kira goma.
Ganin lokaci na sake ƙwacewa baba ƙaura yace sojan idan yasan inda gidan Jay yake ya kwatanta masa. Sojan shima bai saniba, dan haka yacema baba ƙaura bara yaje ya bincika ko za'a dace. Tunda sojan ya fita baba ƙaura ya kasa zaune ya kasa tsaye, ba komai ya kawo hakanba sai abinda ya jiyo a daren jiya, ga lokaci yanata sake tafiya kuma.
A jiya gaba ɗaya zaman ya gunduresa, jiyay yana sha'awar zagaya jeji, dan haka tun bayan sallar la'asar ya sulale yabar Barrack batare da sanin kowaba sai sojan nan da General ya ɗaura alhakin kula da shi akansa, yanda yaron ke masane ya sakashi ƙaunarsa harma yake masa wasu abubuwa na taimako, sannan baya ɓoye masa wasu abubuwan da suka shafesa, hakan yasa a fitarsa ta jiya ma ya sanar masa. Yayi ninƙaya cikin jejin sosai jiya bisa al'adarsa ta farauta da sanin sirrin jajejin da ALLAH ya bashi badan zaiyi farautar ba, dan ko karnuka babuma a tare da shi. Tun daga farkon dare har kusan ƙarshensa bai fitoba yana a dajin. sai da ya gama jin sirri mai girma daga shaiɗanun da suka maida wani yankin jejin nasu sannan ya fito, gab da asubahi ya shigo cikin gari, ana shiga salla masallaci yana isowa Barrack. A gaggauce yay alwala ya shiga masallacin shima. bayan an idar da salla ya saka sojan nan ya nemo masa Number Jawaad zaiyi magana da shi, sai dai sam an gaza samunsa, da aka samesan kuma ma sai bai ɗaukaba.....
Dawowar sojan tasakashi tsayawa cak daga kai kawon da yake faman yi da tunanin daren jiya, cikin ɗoki ya sanar masa an gano family house ɗin su Jawaad ɗin, kuma yana ƙyautata zaton a ciki jay yake zaune da iyalinsa. Baba ƙaura yayi murna, sojan nan yay masa rakkiya har bakin hanya ya sakashi a napep da faɗama mai napep ɗin inda zai kai baba ƙaura. Kasancewar gidan su Jay sanan nan gidane sai akaci sa'a mai napep ya sani.
Da ƙyar suka samu maigadin ya sauraresu, danshi tsoron baba ƙaura ne ya kamashi ganinsa sanye cikin fatun namin jeji, gashi babu hannu guda. Sai da baba ƙaura yayta m
asa magiya sannan ya sanar masa cewar Jawaad ba nan yake zauneba yanzu, yana gidansa da ke a A.Y street. Nanma sunsha daga kafin ya basu address ɗin, mai napep ɗin da yake yanada kirki shine ya sake ɗaukar baba ƙaura zuwa A.Y. sai dai suna shiga layin, motar Jay na fita. A gidan Jay ɗinma sunsha daga da maigadi kafin ya sanar musu Jawaad ɗin baya gida ya fita babu jimawa, suka roƙesa koya san inda ya nufa yace shi bai saniba. Sosai hankalin baba ƙaura ya sake tashi, burinsa kawai yaga Jawaad, harsun baro gidan ya roƙi mai napep ɗin suka sake komawa. Tambayar maigadi yayi ko ina drivern Jawaad ɗin?. Maigadi ya amsawa baba ƙaura a daƙile cewar yau Sadiq baizai zo aikiba yana gidansa. “Dan ALLAH ka faɗa mana inda gidan nashi yake zamuje mu samesa?”. baba ƙaura ya faɗa yana kallon mai gadin. A fusace mai gadi yace, “Kai malam kafa isheni, taya zan faɗa maka bayan bansan kaiɗin wanene ba? Nama sani ko cutar da waninsu zakayi, indai ma ogane yafi ƙarfinka dan shima wlhy aljanin kansane da kake ganinsa nan”. Murmushi baba ƙaura yayi, yace, “Yaro nafika sanin hakan ai, ka daure dai ka faɗa mana kokuma ka kira mana shi direban a waya idan ya gammu shi yasan manufarmu”. Kamar maigadi bazaiyi ba, sai kuma miya tuna oho masa ya ɗauka waya yay kiran Sadiq.
Babu jimawa saiga Sadiq mai napep shima ya kasowa, yana ganin baba ƙaura ya rikice, dan baiyi zaton shiɗin bane da gaske. Haƙuri yayta bashi akan abinda maigadi yay masa, baba ƙaura yace babu damuwa, so yake yanzunan ya kaisa inda Jawaad yake shidai. Maigadi dai jikinsa yayi sanyi ganin yanda Sadiq ya bama baba ƙaura muhimmanci, a take ya shiga bashi haƙuri. Baba ƙaura yay murmushi kawai yace karya damu........
___________________________
Anbar ƴan sanda zagaye da gidan Alhaji babba, su Jay kuma suka kwasa zuwa station dan aikin zaifi yuwuwa acan cikin sauri.
Bilkisu dai duk ta kasa sukuni akan sako Qaseem da Dad da Jay yayi a waɗanda yake zargi, zuwa yanzun kam tafara yarda da saƙe-saƙen zuciyaryarta, anya kuwa babu wani abu a rufe da bata saniba? Haka kawai mijinta da Dad bazasu ringa takun saƙa na kamar wasu maƙiya ba, a dafa surukinsa ne, sannan mijin yayar mahaifinsa ne. Ta tuna kallon kallo da suka dinga yima juna jiya duk da shi Dad yanata nuna babu komai.....
Da wannan tunanin a ranta suka isa station, babu mutane da yawa saboda weekend ne. Ni da su oga hafiz muka nufi office ɗin boss, shi kuma suka nufi na sir Ahmad..
Bamufi mintuna goma ba shima sai gashi ya shigo office ɗin ɗauke da takardu a hannu.
Kujerar zamansa ya nufa yana faɗin, “Miemaa taso kiyi wannan aikin”. Miƙewa nai daga inda nake zaune ni kaɗai na nufesa. Kujerar zamansa ya nunamin, babu musu na zauna shi kuma ya shiga ƙoƙarin dai-daita Computer ɗin.
Oga Jabeer da Hafiz dake can gaban Computers ɗin dake gefe guda biyu suka juyo suna kallonmu, Hafiz ne yace, “Boss babu watafa alamar waya data shiga tsakanin Alhaji kokino da Dadyn su Shahudah gaskiya, amma Dad yayi waya da Qaseem awa ɗaya da mintuna hamsin da uku da suka wuce. Barin inda nake yay ya nufesu, “Zamu iya samun maganar da sukayi?”. Jabeer da hankalinsa ke ga Computer gaba ɗaya yace, “Bazai yuwuba gaskiya, dan inhar mukai hakan zai gane, kasan wayar Qaseem tana da tsaro kamar yanda namu suke”. Jay yayi ɗan jimm na tunani. Numfashi ya furzar mai zafi yana dafe kansa dake sara masa, sai kuma ya zabura kamar wanda ya tuno wani abu. “Jabeer ina zuwa, bara na turo muku Numbers ɗin nan, dukansu inason mu tabbatar idan suna aiki a halin yanzun”. Yay maganar yana sake nufo inda nake, drawer ɗin jikin table ɗin ya jawo, flash ne da yawa a ciki, ya shiga ɗakkosu ɗaya bayan ɗaya yana duba rubutun da yay a jiki, cikin sa'a ya samo wanda yake nema, miƙamin yay yana faɗin, “Saka shi”. Yanda yake min magana babu wasa tattare da shi yasaka jikina har tsuma yake, sai da na gama dai-daita komai abubuwan dake cikin flash ɗin suka bayyana sannan ya ranƙwafo kaina, hannunsa ya ɗora bisa nawa dake a dafe da mouse muka ringa control ɗin Computer tare.
A haka Sir Ahmad da wasu jami'a
nmu manya biyu suka shigo suka samemu. Nan take aikin ya sake ɗaukar zafi, ni dai ta ɓangarena da taimakon boss nakeyi. Kusan minti goma sha biyar mun duƙufa, hankalin kowa nakan abinda ke gabansa akai knocking ƙofar office ɗin, batare da jiran izini ba oga Aliyu ya shigo da sallama. Inda muke ya nufo bayan yayi salute ɗin su Sir Ahmad. Bansan miya gwargwaɗa ma Boss a kunne ba, na gadai shima boss ɗin ya miƙe ya nufi Sir Ahmad cikin zafin nama. Sai kuma suka fice shi da Sir Ahmad ɗin daga office ɗin.........
_________________
BABA ƘAURA
_______________
Cikin mintuna ƙalilan suka iso station ɗin bisa taimakon Sadiq, sai dai kuma securitys sun hanasu shigowa musamman ganin yanayin baba ƙauran, sun musu roƙon duniya amma sun hanasu, Sadiq ya kira wayar Jay amma bai ɗagaba, hakan yasa suka koma gefe cike da damuwa, musamman ma baba ƙaura dake matuƙar matse da son ganin Jay.
Suna a wajen tsaye su biyu Sadiq na cigaba da kiran Number Jay sai ga motar su Aliyu, harma an buɗe musu gate zasu shige Aliyun ya hango baba ƙaura ta mirror. Sauke gilashin motar yay ya saka ɗaya daga cikin securitys ɗin yay masa magana da baba ƙaura. Ganin shi ɗinne dai kamar yanda yay hasashe sai ya bada umarnin barinsu su shigo. Bayan ya shige da motar ya samu waje yay fakin ya fito shi da waɗanda sukabi masu ƙwamushe Alhaji babba, gaisuwa kawai yay da baba ƙauran ya shiga ya sanarma Jay.
Duk da Aliyu ya sanar masa baba ƙaura ne hakan nbai hanashi yin mamakin ganinsa har station ɗinsu ba, ya ƙarasa fuskarsa babu walwala, dan duk yanda yaso aro fara'a ya azama fuskar tasa kamar yanda ya saba idan yaje wajen baba ƙaura hakan ya gagara. Cike da girmamawa suka gaishesa har Sir Ahmad.
Kallonsu baba ƙaura yay ya ɗauke kansa yana faɗin, “Kagani har a wajen aikinka ko?”.
Ɗan murmushi Jay yayi da cewa, “Babu komai baba, ai nasan zuwan naka mai muhimmanci ne”. “Hakane” baban ya faɗa yana sake maido hankalinsa garesu sosai. Yace, “Tun da safe na saka a nemomin kai amma hakan ya gagara, ba'a samunka da farko, daga baya kuma ta shiga ba'a ɗagawa”. Kai Jawaad ya dafe, “Dan ALLAH kayi haƙuri baba, wlhy na tsinci kainane a yanayin da komaima bazan iyaba”. “Gudun faruwar hakanne ya sakani yimaka neman gaggawa ai daman, tun bayan wucewarka na tafi jeji ne, acan ma na kwana, dan sai gabannin asubahi na shigo gari, sanda na iso nan har an shiga salla. Na saka a nema min kaine domin isar maka da saƙon abinda idona ya ganomin jiya a cikin jajin nan. Muhammad Jawaad lallai akwai matsala babba dake tunkaroku, da idona na gani, na kumaji da kunnena, gashi rashin samunka akan lokaci ya nunamin alamomin fara faruwar matsalar dana guda ma a yanzun”.
Hankalin Jawaad a tashe yace, “Baba hasashenka duk haka yake, yanzu haka zancen da nake maka anje har gida an ɗauke kakana, akan binciken inda zamu samesa muke”.
“Wannan shine shirinsu na farko dama. Na zauna nayi ƙyaƙyƙyawan nazari mutanen nan ba haka nan suke bibiyarka ba, akwai wani abu aƙasa wanda akwai jininka a ciki, ina nufin cikin zuri'arku akwai wanda ke tare da mutanen nan.....” cike da mamaki Sir Ahmad da Jay suke kallon baba ƙaura. Ya jinjina kansa yana cigaba da faɗin, “Kar kuyi mamaki, neman duniya babu wanda baya ɓatarwa, lallai kamar yanda na faɗa akwai wani abu a ƙasa, dan babu rami miya kawo rami? Bayan abubuwan dana sani ke a hannunku akwai wani abu da kuka ɗakko a wani gida ne?”. Sir Ahmad ya kalli Jay, shima ya kalleshi, sai kuma ya maida dubansa ga baban yana jinjina masa kai. “Akwai wani tukunya baba, wanda.........” ya labartama baba ƙaura da Sir Ahmad komai.
Baba ƙaura da keta faman jinjina kai cike da nazarin maganganun Jawaad ya sauke nannauyan numfashi. “UBANGIJI ya baku kariya sosai to akan wannan aikin, dan suna cikin ruɗani mai girma akan son gano wanda ya ɗauki tukunyarnan, amma sun gaza gano komai, inuwar wadda ta ɗauka ɗin kawai suke iya gani, sannan har yanzu tsafin nasu kuma bai iya nuna musu mahaifiyarka ta shigo ƙasarnan ba. Wannan hikima ce da rahama daga UBANGIJI, inaga iyakar suce tazo shiyyasa komai
ya keta ƙwace musu. A taron da sukai daren jiya sun tattauna abubuwa da dama wanda zarge-zarge da yawa sun sami rinjaye a kai kanka, sai dai a yanda na fahimta na yau sai sun fisu muhimmanci. Dan haka nakeso ku kasance a wajen kai da matarka idan zai yuwu, sannan lallai matsayinku na jami'an tsaro wannan shaiɗancin ya kamata ma ace ku kawo iyakarsa ma baki ɗaya. Dan tabbas kakanka yana tare da su, acanne kawai zaku iya samosa a halin yanzun dama wasu mutanen da aka kai a wajen bisa zalunci da son zuciya”.
Boss ya cika bakinsa da iska ya furzar yana taunar lip ɗinsa na ƙasa da ƙarfi. Kallon Sir Ahmad dake fahimtar dukan maganganun nasu a baibai yayi. sai kuma ya maida ga baba ƙaura yana faɗin “Babu damuwa baba, amma kana ganin ita zuwa da ita bazai zama haɗari ba?”. Ƴar dariya baba ƙaura yay yana kallon Bilkisu data fito da waya a hannu ta doso su, “Babu wani haɗari insha ALLAHU, matar nan taka akwai sirrika tattare da ita waɗanda ALLAH kaɗai yasan tushensu, amma haka kawai nakeji a raina kamar sunada nasaba da taka ƙaddarar. Amma ita ɗin ba jami'ar tsaro bace?”. “Eh jami'ar tsaroce, irin aikinsu ɗaya”. Sir Ahmad ya bama Baba ƙaura amsarsa. Baba ƙaura ya sake faɗaɗa murmushinsa “Ka barta itama ta nuna bajintarta a aikinta da ƙwazon da ALLAH ya bata, ALLAH yana tare daku a dukkan al'amuranku insha ALLAHU. kudai kuci gaba da gayama ALLAH”. A tare suka jinjina masa kawunansu da faɗin insha ALLAHU baba. “Karkuji komai, wannan tafiyar tafi ta farko sauƙi insha ALLAHU, ta wani ɓangaren kuma tafi waccan haɗari, dan haka runduna zaku haɗa mata da tafi ta farko indai aikin zakuyi da gaske” ya ƙare maganar dai-dai da isowar Bilkisu wajen.
Rissinawa nai na gaida baba ƙaura da banyi tunanin ganiba anan, ya amsamin cike da fara'a da kulawa. Cikin girmamawa na miƙama Sir Ahmad takardar hannuna da aka aikoni na kawo masa. Amsa yay yana dubawa, ni kuma na maida dubana ga boss da yanayinsa ya bani tsoro. Da ido nai masa alamar ‘Lafiya?’. Kansa yaɗan girgizamin kaɗan yana lumshe idanunsa dake jajur.......
Sir Ahmad ne ya katse mu da faɗin, “Jay inaga yanzu haɗa rundunar da zamu tunkaru jejin ne ya dace, bara na nema mana jirage masu saukar angulu yanzun nan, sai ku haɗa kayan operation ko”. “Okay Sir” Jay ya faɗa cike da karsashi na jami'i mai cikakkiyar lafiya da zafin nama..
Tare muka koma da baba ƙaura office ɗinsa inda su Jabeer keta aiki cike da zafin nama da ƙwarewa. Boss ya ɗan bigi tebir da zafi-zafi yana faɗin, “Ayi shirin fita operation mun gano inda suke insha ALLAHU”. Duk juyowa sukai suna kallonsa da mamaki, harni kaina kallon nasa nake, amma sai ya ɗauke kai yana nufar telephone ɗin dake saman table ɗinsa yana jero sunayen waɗanda za'a kira yanzun nan”.
Cike da bin umarni Aliyu ya fice zuwa office ɗinsa domin aiwatar da komai, shima bayan yayi waya da wani da bansan ko wanene ba ya ajiye yana kallona da nufar ƙofa yace na biyosa ni da Dawood da suka dawo da Oga Aliyu yanzun.
Store ɗin station ɗin muka nufa, inda acan muka iske Sir Ahmad da wani ogan mu shima suna haɗa bindugu. Muma aikin haɗa wasu makaman aka sakamuyi. Mamaki ya kuma cika zuciyata, duk yanda nake hasashen al'amarin da alama ya wuce nan, nasan Boss mutum ne mai muhimmanci a hukumarnan tamu, ya cancanci a nuna masa kowanne irin halacci akan taɓa ahalinsa, amma yanda ake shirin fita operation ɗin sai nakeji a raina kamar ya zarce na maido kakansa kawai. Cikin mintunan da bazasu gaza talatin ba duk wani shiri an kammalashi, duk jami'in da aka buƙaci gani ya amsa kira, a mamakina harda su Ummie su dukansu, Rose harma dasu Ada, sai sauran jami'ai na departments ɗin da ba namuba ma. Dukanmu mun kasance cikin Uniform ɗin aiki, dan boss ma da yake sanye da kayan gida a da sai gashi ya fito cikin Uniform harsu oga Jabeer da Sir Ahmad ɗin kansa. An bamu bullet proof jacket duk mun sassaka, kafin oga Hafiz ya rarraba mana bindugu harda kibiya ga waɗanda suka samu horo na musamman a kanta, wasu kuma wuƙaƙe naga an basu manyan takubba, sosai mamaki abin yayta bamu mu baƙin shigowa hukumar, dan zan iya cewa wannan shine operation na
farko gagarumi da za'a fita damu..............✍
Da ace zan iya sai nabi wasunku da bulala goma-goma a ɗuwawu aradu🙄, wlhy nafiku son naga na kammala buk ɗin nan🤦🏻. Uzirin daya riskeni ya wuce dukan tunanin mai hasashe, yanzunma dauriyace kawai dason ganin na faranta muku, saɓanin wasunku da bakunansu ke furta abinda bai daceba a gareni😢🚶🏻.
ALLAH ka gafartama iyayenmu🙏🏻😭
Post a Comment for "KWAI CIKIN KAYA BOOK TWO PAGE 57"